Skip to content

Chapter 80

Chapter 80

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

zata iya yi mata aikin tashin asuba, "Nadeeyah, dan Allah da asuba ki tashi Musaddiq, ki hada mishi break fast dan jirgin 6 zai bi zuwa abuja, Yaye bargo Badariyyah tayi da sauri tace "zan tasheshi Mummy, "a'a Badar kar kisa ya makara, 9 ake son ganinsu, "Allah Mummy zan sa alarm ta fadi tana hararar Nadeeyah, to shikenan Allah ya kaimu, dan Allah kar ki bari ya makara, "karki damu Mummy ta fadi hade da dauko wayarta ta sanya alarm karfe biyar da rabi dan tsabar kwancewar noti, yaushe har ya tashi yayi wanka ya ci abinci, al'amuran Musaddiq lokaci suke bukata, mutumin da sai afi awa ana tashinshi a bacci, Badar kuwa cike da murnar zata kasance da abin kaunarta ta ja bargo ta rufe kanta.... Karfe hudu saura Nadeeyah ta tashi, kallon yadda Badariyya ke bacci ba tare da motsi ba tayi, a zuciyarta tana tsoron tashinta kar ta jama kanta zagi, "dakyar ta fara tashinta tana fada mata lokaci yayi, inaaaa Badar bacci yaci karfinta ta juya ta cigaba da baccinta, Hudu da yan mintuna Nadeeyah ta fita dan tasan in dai aka biyewa Badar tofa babu abin da zai hana Musaddiq kaiwa tara a gidannan, Murda kofar dakinshi tayi taji karar alarm a gefenshi amma ko gezau baiyi ba, karasawa tayi tana murmushi ta dauki wayar ta kara mishi karan a kunne, "ummmmmm kawai ya fàdi hade da toshe kunnenshi da pillow, ajiye wayar tayi a kan gadon ta yaye bargon jikinshi ta fara zare pillon, kara kankame pillon yayi yana sambatun dadin bacci, dan a wannan lokacin wani irin rarrashi shaidan yakeyi ma mutum mai sanya bacci dadi, babu lokacin da yakai karshen dare dadin bacci, dakyar ta iya fisge pillon wanda hakan yayi sanadiyar fadawanta jikinshi da karfi, cikin bacci ya kankameta ba tare da yasan yayi ba, kici kicin kwace kanta ta shiga yi wanda hakan yaki yuwuwa saboda girma da tsawon Musaddiq, gaba daya jinta tayi kamar wata babyn roba a jikinshi saboda tsabar kankantar da ta mishi, ganin ta kasa kwatar kanta ya sata sanya hannu a hancinshi ta toshe, tasan dole ya bude ido saboda babu hanyar numfashi, wani irin numfashi ya saki ta baki hade da bude idonshi ya sanya su cikin nata, kara runtsesu yayi dan ya dauka duk cikin mafarkin da yakeyi ne, yana kara rufesu ta kara rufe hancin, bude idon yayi gaba daya kamar zaiyi kuka yace "menene? dariya tayi maganarshi ta mantar da ita a inda take tace "ka tashi karfe shida har da rabi, ga Daddy can ya je dauko bulala, *Haka Mummy ke ce mishi in yaki tashi ya tafi makaranta*, Husnah ta bata labarin jiya kafin su kwanta, "uhmmm ni zan kara minti biyar ya fadi yana sake runtse idonshi, "Hello Daddy yaki tashi wai bazai je inter----- da sauri ya mike har yana bige mata hannu, dariya ta saki tace " kayi sauri kayi wanka, lokaci ya kusa, bari inyi saurin hada maka break fast, bayi ya fada yana lumshe ido kamar zaiyi kuka, daurewa yayi ya shiga shower ya wanke jikinshi tass, A bayin ya shafa mai bayan yayi alwala, saida ya idar da Sallah ya shirya cikin kananan kaya masu kyau cool colour, dakin ta kawo mishi kayan kari lokacin biyar da minti goma, "Bana karyawa da wuri, dan Allah ki maida, in naje can zanci abinci, "noo gara kaci tun yanzu in kaje can babu time, hada mishi tea tayi ta bashi bread guda biyu ta mika mishi plate din kwai, ka canza wadannan kayan, kai da zaka shiga cikin manyan mutane sai a ganka kamar area boy, "dauko min wasu kawai ya fadi yana mai jin kuncin tashi daga daddadan baccin da yakeyi, Drawershi ta bude tana dariya ta fito da golden brown shadda mai kyau da yauki, yana gama karyawa ta fita tabarshi, kayan jikinshi ya canza hade da feshe su da turare, milk takalmi yasaka sannan ya ratayo jakar takardunshi da laptop dinshi ya fito parlon, "ina hular fa? ta tambaya tana karasowa inda yake da leda a hannunta, shi yama manta da wata hula yace "ta dauko mishi, "gefen jakar hannunshi ta bude ta saka ledar hannunta, taba gurin yayi yace "meye wannan? "zaka gode min in kaje can, karka bude, zama yayi akan kujera yana jiran ta kawo mishi hular, Hular data dace da kayan ta dauko ta mika mishi, kanshi ya miko mata a cewarshi bashi da karfin daga hannu, gyara karin hular tayi ta sanya mishi ita akai, yayi kyau matuka kamar wani babban mutum mai cike da haiba da kwarjini, sakkowa Daddy yayi yana dariya yace "Saaaadiq ne yau da tashin asuba, baki ya turo gaba yace bakai kasa ta dameni ba, dariya Nadeeyah tayi ta tsuguna tace "ina kwana Daddy, "lafiya kalau yar albarka, kin samu ladan yayanki, Allah ya biyaki, murmushi tayi taja da baya ta barsu suna zantawa, kudi masu yawa Daddy ya bashi sannan yayi mishi fatan alkhairi, "har bakin mota Nadeeyah ta rakashi da addu'a sannan ta fada mishi in zai shiga ya karanta suratun Nasr kafa uku, Har Malam Ali ya tada motar tayi saurin cewa ka kira Mummy da Daddy lokacin da zaka shiga gurin, adduarsu mai karfi ce a gareka, gyada kai yayi yana murmushi ya daga mata hannu, itama hannun ta daga mishi tana fadin Allah ya bada sa'a, saida motar ta fita a gate din sannan ta koma ciki ta gyaro mishi dakinshi da kyau, lokacin biyar harda minti arbain, Dakinsu ta shiga ta ji karar alarm din Badar, tana hangenta tayi tsaki ta kashe wayar gaba daya, samm baccin asara yasata ta mance abin da kudiri niyyar yi, " bayi Nadeeyah ta shiga tayi wanka ta canza pad saboda tana hutun sallah, komawa tayi ta kwanta tana sauraron karatun qu'rani har bacci yayi gaba da ita, Badar bata tashi ba sai karfe tara da minti ashirin, da sauri ta duro a gado tana fadin "na shiga uku, kallon agogo tayi taga lokaci, jiki na rawa ta fito parlor taga ba kowa, dakin Musaddiq ta fada ta ganshi a gyare kamshi mai dadi hade da sanyi na tashi a ciki, tsaki taja mai nuni da tsanar irin lalurar baccin dake dawainiya da ita....... Karfe takwas na safiyar ranar Papy da iyalanshi sukayi shirin komawa Gombe, gidan Baffa suka wuce dan suyi Sallama dashi, A kofar gida suka tadda shi yana gaisawa da makota, fara'arshi ce ta karu da ya hangosu, Suna karasowa ya gabatar musu da danshi, jikokinshi, da amaryarshi, Gaisawa sukayi da su, Alh Jogana ya kalli Hafeez yace "wannan ba sai an fada min ba, dan marigayi Adamu buzu ne, kamanin sun nuna kansu, dariya Baffa yayi yace "kwarai kuwa babban danshi ne, Allah sarki... Alh Jogana ya fadi cike da tausayi, har yanzu dai ba'a samu labarin danginsa ba, mutumin kirki, ko yaushe na tambayeshi sai yace min daga Agadez yake, amma sunan garin da yake a agadez ya bace mishi, ba mamaki maraya ne, Allah yayi musu rahama, Ameen... dukka mutanen gurin suka ce sannan Baffa ya sallamesu ya shige gida, Wata sabuwar gaisuwa suka sake yi Baffa yace "Har kun shirya tafiya, "eh Papy yace hade da fito makudan kudi a aljihunshi ya

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156