Skip to content

Chapter 95

Chapter 95

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

Shattimah........ [11/04 12:07 AM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 5⃣6⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Mikewa Mummy tayi zuciyarta ta fara sanyi na yadda taga Badar ta harzuko, tasan tabbas Badar bazata taba bari auren nan ya tabbata ba koda kuwa zai zama ajalin Nadeeyah... Hannunta ta kamo tace "Musaddiq dinki Badar, mun gama magana da wani malamina akan halascin aurenku, da murnata nazo na fadawa Daddy, shine yake cemin wai ai Papy Saif yazo mishi da maganar yanason hadin auren Nadeeyah da Musaddiq, shi kuma nan take ya amsa mishi saboda kinsan yadda Daddynku yake da s-any-in haaa--li, ni yanzu bansan yadda zanyi da raina ba, ta karashe da kuka sosai wanda yake nuni da tabbas tana bukatar taimakon Badar... Furzar da huci Badar tayi murya a kausashe tace "Wallahi bazai yiwu ba, na dauki alwashin saidai Musaddiq ya zauna babu aure in har ban halasta a gareshi ba a baya lokacin da kika ce ba aure a tsakanin mu,, bare kuma yanzu da na tabbatar na halasta a gareshi zan yarda ya auri wata, watar ma Nadeeyah, wallahi Mummy saidai ayi auren nan babu raina, bazan ma mutu ba, sai dai ita ta mutu, hannu ta daura kan kafadun Mummy tace "ki kwantar da hankalinki, kima daina kuka, kisa ma ranki salama yau zuwa gobe zakiji sabon labari, zaunar da ita Mummy tayi cikin tsorota da yanayin kalamanta tace "Badai kauce hanya zakiyi ba? Dariya Badar tayi tace "karki damu nace, badai kin yarda da batun aurena da Yaya Musaddiq ba? Gyada kai Mummy tayi tace "eh, a zuciyarta kuwa tana jin tsoron karyar da tayi ma Badariyya, tasan sarai in auren nan ya lalace wata rigimar ce zata sake bullowa, kauda zancen tayi a zuciyarta, dan tasan yadda zata tafiyar da Badar bayan maganar auren Nadeeyah ta lalace...... *KUNGAMAR GARZAR* Washhhhh...., na taka qaya, duba min kigani Lawisa Lawal, hannunta Lawisa ta kama tace "sauri fa zamuyi Badar, kina ganin har la'asar tayi bamu karasa ba, dajin nan is very dangerous, nima Anty Laurah ta taba kawo ni, ban taba tunanin ma zan gane ba, dan Allah ki dago kafa, "dingisawa Badar tayi ta sake yin ihu hade da tsugunawa ta cizge kayar, bata damu da jinin da ke bin kafarta ba tabi Lawisa suka dinga sauri cikin dajin, minti talatin suka kara suka isa gaban wata katuwar bukkar fulani, almajirai ne kewaye da ita suna kara kaini da alluna, sai gungun kyawawan yaran fulani daga can nesa suna wasan kasa, matan na yar gala gala... Suna shiga gidan suka bangaji wata yar budurwa da ta arto a guje tana ihun kuka, wata katuwar farar mace fuska duk kalangu na biye da ita da bulala a hannu tana zaginta da fulatanci, ramawa budurwar takeyi tana fadin "Allah ya isa muguwa, azzaluma, bazan yi wanke wanken ba, in kinga dama ki kashe ni, ganin su Badar ya sanya matar yar da bulala tana fadin "marabanku, ku shigo daga ciki, a darare Badar ta kalli matar sannan ta kalli Lawisa dake kokarin janta zuwa ciki, zatayi magana kenan Lawisa tayi mata alama da tayi shuru su shiga daga ciki, a tsorace ta fara bin Lawisa da matar har suka isa wata lafiyayyar bukka dake kawace da adon fulawoyi, "babu abin da ke fitowa a bukkar sai hayaki mai karfin kamshi wanda ka iya buga kan mutum in ya shakeshi na tsawon minti goma, da sauri Badar taja gyalenta ta rufe hancinta gabanta na tsananta faduwa, a zuciyarta tana dana sanin biyo Lawisa gurin nan da tayi.. " *Lawisa ta dade tana bata shawara akan tazo suje inda zata karkato da hankalin Musaddiq da Mummy su yarda da aurensu koda kuwa bai halasta ba Badar taki, saboda a ganinta zata iya shawo kan komai saboda irin soyayyar da Mummy ke mata, jin batun auren Nadeeyah da Musaddiq shi ya harzukota ta nemi Lawisa suka taho ba bata lokaci, bata san azal ke kiranta ba* katse mata tunani Lawisa tayi tace "ance mu shiga Badar, firgigit Badar tayi ta cire takalmanta suka fada cikin bukkar, Suna suka saka kafarsu a ciki hankalinsu ya gushe suka manta inda suke, sai ganin kansu sukayi a cikin wani kayataccen parlon da duk iya maitar mutum bazai san ta inda yabi ya shigeshi ba, jiki na rawa Badar ta damki hannun Lawisa suka zauna a gaban wanda Badar tafi zaton shine bokan, gefenshi kuma saurayi ne dan shekarun da basu fi talatin da biyar ba yana zaune shima da kayan tsubbun a gabanshi, dago kai saurayin yayi ya kallesu yace "Badariyya da Lawisa barkanku da zuwa, nan cikin Badar ya duri ruwa saboda tsabar tsoron da taji, a ina yasan sunan su? Tambayar da ta dinga yi ma kanta kenan, "Nasanki tun ranar da kika duro duniya Badariyya, babu motsinki da ban sani ba, har wannan zuwan da kikayi na sani, dan ni na shiryashi, gefen da Lawisa take ta kalla nan da nan ta saki hannunta saboda wata iriyar dariyar da takeyi mata mai cike da ban tsoro, mikewa lawisa tayi tana dariyar da ta ke amsawa a cikin dakin, sannan ta Kalli Badar tace "ke matar dan sarkin mu ce, wannan shine *Sarkin bokaye Shahalu* sai danshi *Yareemah Suhailu* karki damu Badariyya, ni kawarki ce kamar yadda kika dauka, amma ki sani na zo gareki ne saboda wannan ranar da zan cikawa Sarkin mu burinshi, "ni ba mutum bace, amma sarki da yareemah mutane ne kamar ke, kyakykyawar mu'amalar dake tsakaninmu dasu ita ta janyo har na taimakeshi, ki kwantar da hankalinki yau kinzo inda kaddararki take, zaki ji dadin zama dashi da yan uwanshi, bissalam kawata Badariyya.... ta karashe tana daga mata hannu tana dariya har ta bacewa ganinta, wani irin ihuu Badar ta saki tana bin gurin da lawisa tabi, "wayyo Allah Mummy ki taimakeni, wayyo Allah Daddy, na shiga uku na lalace, wayyyyyo Allah na, keeeeeeee!!! Wata irin tsawa taji daga bayanta wacce ta sanyata dunkulewa guri daya, murya a kausashe Sarkin bokaye yace "Karki sake yi min ihu anan, kin san Allah dama? In kika sake kiramin sunan Allah anan zan cire idon ganinki, na rantse da abun bautarmu *GARGAZ*, Kee... *Kande* ya kwala kiran katuwar matar da ta shigo dasu, Da sauri ta karaso ta tsuguna a gabanshi tace "Ranka ya dade gani, "Maza ki dauketa ki kaita cikin gida dakin da *Halyo* ya gyara jiya, an sa gado da katifa dama, jiran zuwanta kawai akeyi, sannan ki jawa *Gimbiya Sailuba* kunne, babu ruwanta da kishi da ita, domin wannan itace matar Suhailu ta farko, tun kafin tazo duniya Mahaifiyarta ta bashi, sai yau *Garzar* ya bamu ikon dawo da ita gurin mijinta, cike da girmamawa Kande tace "to ranka ya dade, an gama, nan ta damki hannun Badariyya tana janta a hankali Badar na turjewa tana ihun neman dauki a inda babu mai jinta sai Sarkin sarakunan da biyayyarshi bata dameta ba, sarkin da a sati baifi ta gaisheshi sau daya ba, sarkin da ya hore mata lafiya da kuma abun da lafiyar zata ji dadi... *ALLAH AZZA WA JALLAH* shi kadai zai fidda Badar daga kangin da take ciki...... *SHIN INA BADAR TA FADO* _(fadan da yafi karfin ka ya kai dan uwa, bar

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156