Skip to content

Chapter 142

Chapter 142

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

basu sake ganinta ba... Da matsanancin kuka ta farka amma ta gaza furta komai dan daga ta buďe idonta zata maida ta rufe, hawaye ne kaďai bai yanke mata, ga azabar ciwo da take ji a hakarkarinta da hannunta, babu irin tambayar da Kamal baiyi mata ba taki kulashi sai ma kallo kawai da take binshi dashi, Dr Marliyya ce ta hanashi matsa mata domin gudun kar wani abu ya sameta, badan yaso ba ya kyaleta har suka fara shirin tafiya airport a motar asibitin..... **** Satin Taheer ďaya ya warke sosai kamar bai taba ciwo ba, saidai ita Nadeeyah kamar lokacin ciwon ya sameta domin ta jikkata sosai a jikinta, Sau huďu Kamal na zuwa gidan Alh Mukhtar sai ya samu a rufe, karshe karya yayi ma Taheer yace mishi sun bar kasar kwata kwata, sannan Number Raliya sam basa samu, haka gidanta sau uku mai gadin gidansu na zuwa bai samunta.. Da haka Taheer ya hakura ya maida hankalinshi kan nemawa Nadeeyah lafiya, duk wadannan abubuwan da yakeyi yana yinsu ne kawai dan Allah da kuma wani abu da yake ji a cikin jininshi game da Nadeeyah, amma bawai dan ta dawo mishi ba, tunda yaji labarin tana da ciki yasan lallai Nadeeyah tayi mishi nisan da bazai taba kamo ta ba, yasan duk inda mijinta yake yana nan yana nemanta, ya dauki alwashin sai ta warke sarai sannan zai maida ta gidan mijinta domin shine silar ciwonta... Watanta uku ta fara tafiya kaďan kaďan da taimakon su Amal da Aman domin Taheer ko rabar kusa da ita bayayi, shidai burinshi ta warke sosai, a kullum in ya tambayeta number wanda zata kira sai dai ta fashe mishi da kuka, samm bata da number Hafeez da shi zata bayar domin tasan yana can cikin tashin hankali, number Hilal ma in tayi yunkurin kawota kanta sai ta manta domin gargadin da su Raudha sukayi mata na su ba danginta bane.. wahalar da take sha kashi biyu ce, ga ta rabuwa da Musaddiq wacce tayi mata kiki kaka a cikin zuciya, ga kuma ta azabar ciwo wanda take tunanin babu ranar warkewa.... Cikinta na wata takwas da kwanaki ta warke sarai har tana iya hawa da sauka, babu wanda baiyi farin ciki ba a cikinsu, Anty Saude kula sosai take bata domin bata san wacece ita ba a lokacin, duk tunaninta wata ce daban wacce danta ya bige da mota yake taimaka mata... *Nadeeyah....* Ajiye ice cream din da take sha tayi tace "Na'am uncle, kujerar da ke fuskantar gadon da take ita ya zauna yace "Ina son yau mu kai karshen komai, kinga lafiya ta gama samuwa a gareki, ki faďa min inda yan uwanki da mijinki suke dan in maida ki, nasan yanzu hankalinsu na nan a tashe, a yanzu na daukeki tamkar kanwata ta jini, babu zancen soyayya a tsakaninmu.. bazan so inga wani naki ya cutu saboda ni ba, Dan Allah ki faďa min inda suke domin mu samu mu maida ke hankalinsu ya kwanta muma namu ya kwanta... Tunda ya fara maganar take kuka, "Kuka bazaiyi mana magani ba, ki faďamin matsalarki, in zan iya inyi miki maganinta, nasan bani da hurumin sanin damuwarki, dan Allah ki faďa min ko zan samu sukuni.... "Ya sakeni, Mijina ya sakeni, sun ce kar in sake zuwa inda suke, sunce bani da asali uncle.. bani da number wayar yayana, yana zaune a gombe, nasan shi kaďai ne yake cikin damuwa, sai Papy, sai kanwata Zainab.... Rashin asali na bazai barni in zauna cikin masu asali ba, nasan mahaifina mutumin kirki ne, ba barawo bane kamar yadda su---ka fadaaa.... runtse idonta tayi saboda yadda taji wani irin ciwo a bayanta... Share hawaye Taheer yayi bayan ya dawo daga shock din labarin sakin da ta bashi.. Mikewa yayi saboda yadda yaga tana cije baki, Subhanallah, lafy? Ya faďi da karfi bayan ya isa gurinta, mararta ta rike tana kokarin mikewa ta kasa, "Momm---- gani nan Tee, gani nan, ina jinku, duk abinda kuke faďi inaji, ashe dama itace Nadeeyar da ta yaudareka? "Momma plss help her, in muka dawo gida zamuyi maganar nan, kinsan sunce kar mu bari tayi labour, c.s zasuyi mata, hararashi tayi ta kamo Nadeeyah domin tasan ciwon nakuda bazata taba barinta cikinshi ba, amma tabbas lokacin barinta gidanta yayi..... Suna isa asibitin babu bata lokaci suka karbeta sukayi aune aunensu, bayan sun gama suka yankata suka ciro santalellen yaro wanda ya shiga cikin zuciyar Anty saude a ganin farko, farin ciki a gurin Taheer da Amal ba'a cewa komai, tun daga nan yaro ya fara ganin gata ta musamman domin yini yakeyi a hannu... Ranar Suna yaro yaci suna Mukhtar.. Hilal, shima dakyar Nadeeyah ta faďi dan da cewa tayi su sa da kansu, duk yadda Anty Saude taso ta nuna ma Nadeeyah bata kaunarta Taheer ya hana domin ya nusar da ita cewar ba laifinta bane... Akwai wani dare da tace mishi "Kar dai so kakeyi ka koma gurin bazawarar yarinyar nan, to wallahy Taheer in har tunaninka kenan gara ka janye dan bazan taba yarda su kashe min kai ba, karka yarda kace zaka dawo da ita cikin rayuwarka in ba haka ba sai nayi mugun saba maka, Shidai kwantar mata da hankali yayi bai bata amsa ba.... Watanta biyu da haihuwa Taheer ya fara lallabata su tafi gida, cikin kankanin lokaci ta yarda cike farin cikin sake ganin Musaddiq, tasan in yaga gudan jininshi zai dawo da ita su cigaba da rayuwarsu cikin kaunar juna, Saboda tsabar sonshi da takeyi ta manta da irin wulakancin da yayi mata shi da su Anty Raudha, tayi musu uzuri na ajizancin dan adam... Ganin yadda take farin ciki ya sanya Taheer soma shirin tafiyarta, ranar da suka tafi tare dasu Amal saida Anty saude tayi kewa, tayi matukar sabawa da Junior, komai ita ke mishi, tsanar da tayi wa Nadeeyah sam bata shafi danta ba, domin sau daya takk a rayuwarta ta taba samun opportunity din raino, sai gashi Allah ya kawo mata wani wanda kaddarashi tazo da ta tsani mahaifiyarshi, Soyayyar Taheer ce kadai tasa ta yarda Nadeeyah ta zauna har wadannan kwanaki, sai kuma soyayyar dan mala'ikan Allah..... Lagos Nigeria.. Da murnarta ta sauko a cikin motar haďe da lumshe idonta, memories din baya ya shiga yi mata yawo, kofar gate din ta kama ta tura, Mummunan gamon da tayi shi ya sanyata sakin kofar Garammmmmm.... ta koma motar su Taheer da sauri tana sheshshekar kuka... "Lafiya Nadeeyah? Menene, "Muje kawai uncle, zanyi maka bayani, tada motar yayi yajata ya fita daga layin ya wuce hotel din da ya sauka kwanakin baya, daki biyu ya kama da parlor, saida suka gama kimtsawa sannan ne ya tambayi Nadeeyah da har lokacin bata bar kuka ba... "Babu amfanin komawa garesu Uncle, sun manta dani, Musaddiq ya riga yayi aure, ya auri Faida wacce tayi sanadiyyar rabuwarmu, Dan Allah uncle karka matsamin in koma gurinsu, domin rayuwata bazata taba inganta ba, bazasu taba barina na zama independent ba, kowa a cikinsu ya manta dani, bani da sauran gatan da ya wuce in nemi ilimi, ku tafi kawai, zan shiga duniya neman ilimi har Allah yasa in dace da tsayuwa da kafafuwata... Tissue ya mika mata yace ta

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156