Chapter 14
Chapter 14
mishi da addua dan dama zuwanka bazai maido shi ba, yaja tsaki ya kashe wayar cike da takaicin halin son kai irin na Hafeez, (Dama Halin mutum na Kwarai ko kirki baya bayyana Sai yayi arziki).... Jiki na rawa Hafeez ya Mike, Ya dauki riga Ya sawa jikinshi, ko jiran farkarshi baiyi ba yayi waje yana jiyo muryarta tana kwala ihun kiranshi, inaaa bai ko waigo ba bare yayi tunanin komawa dakin Ya sallameta, Motarshi Henesy ya shiga ya tayar Ya fara gudun fitar hankali, hanyar Kaduna Ya dauka yana tafe yana kukan dana sani.... Takwas da rabi ya iso gidan lokacin ana kici kicin daukar gawar Malam Adamu, kuka ya fashe dashi da ya hada ido da mamma, Kure shi tayi da ido cike da mamaki da takaici, durkushewa yayi a gabanta yana kuka Mai Sosa zuciya, ganin da yayi za'a fitar da gawar ne Ya sanya shi mikewa da sauri ya nufi gawar, ya sa hannu zai karbi makarar a hannun Musaddiq yaji wata gigitacciyar tsawa a bayanshi, " IDAN KA KUSKURA TA TABA MAKARAR NAN BAZAN TABA YAFE MAKA BA,, Chakkk ya tsaida hannunshi ya waigo ya Kalli cikin idonta, kau da kanshi yayi da sauri saboda abun da ya gani a kwayar idon, soyayya mai dishi dishin kiyayyar bacin rai ya gani, "Kiyi Hakuri Suwaiba, mahaifinshi ne Ya zame mishi dole yayi rakiyar gawarshi, Sailuba matar malam Sada ta fadi tana share hawaye, "Ban hanashi rakiya ba, amma kar kazamin hannunshi ya kuskura ya taba min gawar miji, ta karashe hade da mai da kanta jikin bango tana gunshekar kuka, fitar da gawar akayi nan gidan ya sake gawraye da kukan mutane musamman makusantan gawar..... Mrs Tijjani Shattima [04/12 09:49] Meela Adeel: ZUMUNCINMU A YAU By Aysha Ya'u Kurah 1β£5β£ Ranar murna, mun cinye gasar BBC, proudly fikriansππ»ππ»ππ» Safiyya ciyaledi i β€ u bebi..... FIKRAH WRITERS Bamu fi kowa ba, Amma da wuya ka samu irinmu, komai namu daban yake... Yin na Allah ne ba namu ba ALHAMDILILLAH..... "Ita Rayuwar nan da kake ganin ta Hafeezu kamar gari ne kaje wanda ba naka ba, kaga komai daren dadewa, komin dadin zaman garin nan dole ka barshi, saboda ba garin ka bane, bakunta ne ya kaika... TALAUCI jarrabawa ce babba wacce cinyeta yana da matukar wahala, duk karfin imaninka dole wata rana zuciyarka ta raurawa saboda zafin wannan jarabawar, Haka shima *ARZIKI* Jarabawa ce mai wuya kuma mai sauki ga wanda ya fi karfin zuciyarshi, ina mai baka shawara da kayi yaki da zuciyarka, ka tafiyar da arzikin da ya fara ziyartar hannunka ta hanyar da ya dace, domin akwai ranar da zakayi bayanin hanyar da ka kashe su, nayi maka farin ciki matuka na samun abin yi Allah ya sanya wannan arzikin ya zama sanadiyyar shigarka aljanna, Allah ya baka ikon sauke hakkinmu kafin mu bar duniyar nan domin Allah shi kadai yasan gawar fari.......... **** Durkushewa Hafeez yayi idonshi na hango murmushin fuskar mahaifinshi yayin da yake mishi wannan Nasihar, Wayyo Allah na, wayyo Baba, kaico na, kaicon rayuwata, ya Allah ka dauki raina nima in huta da wannan bakin cikin, wayyyyo baba..., dakyar mazan gurin suka iya dagashi saboda yadda ya cije yana buga kanshi a kasa, ku sakeni Dan Allah rayuwata bata da sauran amfani, dan Allah ku barni in mutu, Tsawa mai karfi Daddy ya daka mishi hade da ma mutanen alamu da su sake shi, hannu yasa a bakinshi yace "wallahi zan bata maka rai idan kayi yunkurin sake koda nishi kwakwkwara a gurin nan, in har so kakeyi ka nuna mana ka fita a musulunci to kaje daga wajen makabartar nan akwai rijiya ka fada, domin wannan duk haukan banza kakeyi, Nutsuwar da daddy yaga ta bayyana jikin Hafeez ne yasa shi ya sakko ya dafa shi yace "zai fi kyautuwa ka tsuguna kayi mishi addu'a domin a wannan gabar ita kadai yafi bukata a gurinka ba kuka ba, Hannun Daddy Hafeez ya kama yana kuka sosai, yace "in na rokeshi gafara zai ji ni ya yafe min, idon Daddy ya ciko da kwallar tausayi domin yana auno shine mahaifinshi ya mutu yana fushi dashi, rungumeshi yayi yace "nasan ya yafe maka Hafeez kai dai ka dage mishi da addu'a da sadaka su kadai zasu nuna zallar soyayyarka a gareshi.... limamin da ya jagoranci sallar gawar ne yayi addu'oi hade da nasihohi, sannan duk suka juya suka bar makabartar suna masu yi ma mamacin fatan dacewa...... CYPRUS Tsaye yake jikin wagegen bud'ad'd'en windon dakinshi, iska na kada labulen windon yana taba gefen fuskarshi, hannunshi rike da daya daga cikin zanen, ya kura mishi jajayen idanuwanshi, zuciyarshi a karye take a wannan lokacin, wayarshi ya dauko ya sake kiran Musaddiq, wannan karan ma bai daga ba, wurgi yayi da wayar hade da dafe kanshi yana mai jin radadi a cikin zuciyarshi, komawa gado yayi ya kwanta ruf da ciki, shi kanshi a yawancin lokuta yana mamakin yadda Nadeeyah ke makale a cikin dukkan kewayen zuciyarshi, tun baisan kalmar So ba yake jinta a ranshi, tun ganin da yayi mata lokacin da ita kanta bata san kanta ba, yana mamakin da a kullum bashi da zanen da ya wuce nata, kullum kara auno fuskarta yake da yanayin girmanta, gyara kwanciya yayi yanata juye juye, a kunnenshi akayi kiran sallar asuba, mikewa yayi jiki ba kwari yayi alwala ya fito dan zuwa masallaci, Anty Reemah da Papa ya hango zaune a parlon kasa sunyi jugum jugum cike da damuwa, da sauri ya sakko daga sama har yana bige kafarshi a matakalar karshe, baibi takai ba ya karasa gurinsu, Mum, Papa, "meya faru na ganku haka? Ya tambaya yana mai tsugunawa kusa da mahaifiyarshi, uhhmm Anty Reemah tace, sannan ta cigaba da cewa, "mijin Mama Suwaiba ne ya rasu cikin dare, yanzu Raliya ta kirani ta fadamin, "innalillahi wa inna ilaihir rajiun, kalmar da Hilal keta maimatawa kenan a cikin zuciyarshi, tunanin shi ya tafi gun sanin halin da Nadeeyah take ciki, zungurinshi Anty Reemah tayi tace "bakaji an tada Sallah bane, mikewa yayi a firgice ya bi bayan Papa da yake kokarin fita daga kofar palon..... Kuka sosai Badar takeyi hannunta rike da kanta tana shashsheka, saboda tsabar kuncin da take ciki bata san gari har ya waye ba, rana ce ta kyallaro ta jikin dan tsagin labulen ta kashe mata ido, a daidai lokacin ta mike da niyyar wucewa daki tayi tozali da madubin parlon, wani irin kamanni ta gani a tattare da ita mai wuyar fassaruwa, fuskar nan tayi jawur hancin yayi suntum saboda kukan da tasha, wani kukan ta sake fashewa dashi hade da rugawa cikin daki, cikin kunan rai ta fada bayi ta kunna pampo tana watsa ruwa a fuskarta tana magana cikin kuka, "Nadeeyah bazan taba kyaleki ba, kamar yadda kikayi min ruining wannan ranar sai nayi ruining life dinki gaba dayanta, bazan taba iya tuna rabon da na zubda hawaye ba, amma yau na zubar sanadiyar ki, na tsaneki, na tsaneki Nadeeyah!! ta karashe hade da kifa kanta jikin bangon bayin........ Mrs tijjani shattima..... [04/12 09:49] Meela Adeel: ZUMUNCINMU A YAU By Aysha Ya'u Kurah 1β£6β£ A yau ne malam Adamu ya cika kwana bakwai da mutuwa, in kaga Nadeeyah da mamanta a wannan lokacin sai ka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156