Skip to content

Chapter 119

Chapter 119

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,197 words 0 views Progress saved
Download Book

a cikinsu ya tanka ta dan anyi mata mai kankat.... Dakinta ta shiga ta tattare kayanta da gwalagwalanta ta fice ta bar mishi gidanshi.... ********* Saida Musaddiq ya kwana uku a asibiti, lokacin ya farfaďo yana gane duk wanda ke kanshi, babu abinda yakeyi daga kallon su Daddy sai bacci in allurai sun ratsashi, tunda ya farfaďo kamar an tafi da hawayen da yakeyi, magana ba ya yinta ko kadan sai dai in sunyi ya bisu da ido, Da support yake zuwa yayi alwala da wanka saboda jikinshi samm babu kwari, a wannan lokacin ne aka yarda kowa yazo ya ganshi dan jikinshi yayi kyau matuka, abinci da ya zamo aminin Musaddiq yanzu ya maidashi babban makiyinshi domin sai anyi bacin rai kafin ya yarda yayi cokali daya, kowa burinshi ya farantawa Musaddiq dan dai kawai su samu ya saki jikinshi ya cigaba da Mu'amala kamar yadda ya saba, Zainab da Ruwaida ne samm ba'a yarda suje inda yake ba saboda har yanzu bakinsu bai bar tambayar inda Nadeeyah take ba... A cikin kwanan shi na bakwai aka sallameshi, har wannan lokacin babu wanda yayi mishi maganar inda Nadeeyah take, shidai yafi bada an binneta shiyasa ma baiyi yunkurin tambaya ba, dan kar ya sake tayar wa da hankalin su Daddy, Suma kuma har lokacin basu bar neman Nadeeyah ba, dan har police station suka kai, tunda Allah baiyi sunga gawarta ba sunsan tabbas tana raye, in da rai wata rana dole su haďu in shaa Allah.... **** "Karka damu Daddy, i will take care of myself, Kallon Zubair Daddy yayi yace "Dan Allah ka kula dashi, karka barshi ya dinga tunani, ka---- "Nace i will take care of myself, i'm nt a kid, yadda yayi maganar da tsawa ya sanya Anty Reemah matsowa kusa dashi, Dafa kafaďunshi tayi tace "Laifi ne dan ance a kula dakai, tafiyar nan ance ka hakura da yinta, baka da lafiya, ka dage sai kayi ta, dole a nemi mai kula da kai.. Hannunta ya cire a kafadunshi ya dauki brief case haďe da kallon Daddy yace "kayi min addu'a in shaa Allah babu abinda zai sameni, tunani shi ke yin kanshi, with ur Du'a komai zai daidaita, Murmushi Daddy yayi yace "In shaa Allah son, Allah ya tsare ku ya bada sa'ar abinda aka je nema... Gurin da Hilal ya ke tsaye Musaddiq ya kalla, suna haďa ido ya karaso inda yake ya rungumeshi, rashin walwalar Musaddiq na matukar damunshi, babu abinda yake sanya shi farin ciki, dariya kanta ya manta yadda akeyinta, domin wani sashi na yin dariyarshi ya mutu a ranar da ya rasa Nadeeyah, "Take care kaji, in na gama project zanzo Singapore inyi keeping dinka company, gyaďa kai kawai Musaddiq yayi suka fita, dukkansu yan parlon kowa na mishi fatan alkhairi haďe da adduar Allah ya kara sanya farin ciki a cikin zuciyarshi...... Mutum kamar Musaddiq wanda baisan menene bacin rai ko fushi ba a ganshi a haka dole hankalin makusantanshi ya tashi dan sun san ba karamin abu bane yake sanya Musaddiq fushi, Daddy yaso yayi quiting aikin da yakeyi amma Musaddiq sam yaki, saboda shi kadai ne yake ganin zai dabe mishi kewa, badan Daddy yaso ba haka nan ya yarda dan yaso ya zauna tare dashi har ya samu sassauci a zuciyarshi... Duk wani shiri na barin gidan su Badariyya sunyi domin abun kawai da ya rage musu shine su tarwatsa kuttun tsafin Bokan gaba daya, layar dake bakinsu suka matsa dan bacewa suka ji su har lokacin a gurin, cike da tashin hankali suka kalli juna haďe da sake latsata, hankalinsu bai kara tashi ba sai da sukaji damka a bayansu, waigowa sukayi dan ganin mai ganinsu a wannan lokacin da suka san sunyi komai dan bacewa ganin mutanen gidan, Yareemah Suhail suka gani gefenshi kuma duk wasu kulli da sukayi ne wanda ya warwaresu ya sanya musu wuta, Dariya sosai yayi yace "kun taba jin labarin wanda ya shigo gidannan ya fita shi kadai, shafa kanshi yayi ya cigaba da cewa "Badariyya nasan da hatsabibancinki kika zo, sai kuma kika kara da na Marakisiyya, da nice ke zanyi biyayya domin cikin biyayyar wata rana in da rabo ina iya kaiki gida ki ga yan uwanki har kiyi musu sati in kinaso, amma tunda kin biyewa wannan hatsabibiyar sai kuyi ta zama da taurin kanku, duk ranar da kuka ga kun amince da zaman gidan nan sai kuyi biyayya, in kuna da rabo sai kuga na kaiku gida dan ziyara, yana kaiwa nan yayi wurgi dasu cikin wani dakin da basu san da zamanshi a gidan ba.. Kukan jini ne kadai Badariyya batayi ba dan ta ga koshi ya rikide ya zame mata kwanan yunwa, tayi shirin komawa ta shiga Musaddiq sosai har ta kai ga aurenshi hankali kwance ba tare da kowa ya zargeta ba... Taci kuka sosai har saida faďa mai karfi ya kacame musu ita da Marakisiyya, faďan da ya sanya zubewar hakoran Badariyya na gaba, dan Sosai Marakisiyya tafi karfinta..... *6months later...* ******* Radiya.. bani dubu biyu zan baki gobe in Reemah ta turo min, Buďe baki Radiya tayi tace "ina na gansu Mummy, nawa nake binki? kusan 30k fa, ina zanga dubu biyu yanzu, Raudha dake kwance akan kujera tace "Ki bata mana, jiya fa kika siyar da zobenki, meye a ciki dan kin bata, kika san abunda zatayi dashi... To munafuka, da na siyar da zoben baki faďa mata abun da nayi dashi ba, saida zoben kaďai kika iya faďa mata, ni fa na gaji da wannan rayuwar, duk wani abu nawa ya kare, kullum ni kenan cikin bada kudi sai kace wata banki, na gaji wallahi ta mike fuuuu tayi cikin daki.... Share zufa Mummy tayi haďe ficewa daga dakin tana mamakin hali irin na Radiya, kwallar da ta fito a idanunta ta share haďe da yin tagumi tana tunanin a wani hali Musaddiq yake yanzu, rabon ta da ta sashi a ido tun daren da suka fita nemo Nadeeyah, ko sau ďaya bai taba tunanin nemanta ba, ta sani ta bata mishi matuka, a yanzu dana sani takeyi sosai na biye wa san zuciyarta da tayi, kawayenta da a da suke like mata kaff dinsu sun guje ta saboda halin da take ciki, Nairah dari yanzu mugun sha'awa take bata, ga Baffa ya dauke Anni ya maida ita gidan da Papy ya siya saboda ya dinga sauka in yazo, ko ganinshi basa yi a gidan saboda a cewarshi basa girmama matarshi, Daddy kuwa ko ta kirashi bata samu dan ya sanyata a black list, samm bata samunshi, koda text tayi mishi saidai ya dawo mata dan ko kusa baya isa gurinshi... Shigowar Rilwanu da kayan abinci shi ya katse mata tunanin da takeyi, da murnarta ta mike tace "Wadannan kayan daga ina? "Alhj karami ne ya zo shi ya sauke su, yana waje nasan yanzu zai shigo, Hijab ta dauko da sauri jiki na rawa ta fita tarbo Papy... Kuka wiwi ta dinga mishi tana neman gafararshi, rike mata hannu yayi yace "Haba, wallahi ban taba rike ki ba, we are all humans, we make mistakes, ni waye da bazan yafe miki ba, komai ya wuce wallahi, ina Goggo? Hmmm ta tafi kauye tun shekaran jiya, "Nace

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156