Skip to content

Chapter 152

Chapter 152

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

zuciya wata nurse tayi taja zani ta rufeta ta kalli Mummy tace "Saidai hakuri, ta mutu!! Bazan mutu ba Goggo ta faďi a wahalce haďe da yayewa ta damki hannun nurse din, irin jinin da ya zuba a jikin Goggo ya isa dukkan karfinta ya kare, A tsorace Nurse din ta fincike hannunta taja da baya da sauri, dan minti ďaya baya tabbas taga mutuwa a tare da Goggo.. Sunan Mummy ta fara kira a hankali saboda duhu ya fara ziyartar ganinta, daga nesa Mummy ta amsa dan tsabar tsoron irin rayuwar da Goggo ta ďibo, gaba ďaya yanayinta ya canza daga farar bafulatana wacce tsufa ya tattare fatanta zuwa wani irin yanayi na ban tsoro, jinin dake zuba a jikinta gaba ďaya ya kafe dan babu ragowarshi a jikinta, karfaffiyar zuciyarta wacce rashin imani ya kesashar ita kadai ke aiki a jikinta... Babu wanda a dakin bai bata mutuwa ba saboda irin ukubar da tasha kuma take kan sha, a lokacin nan mutane da dama sun sake tsorata da Allah domin shine ke da ikon yin wannan abun al'ajabi,, Sake kiran sunan Mummy Goggo tayi a karo na uku, a ďarare ta matso kusa da ita tace "Gani, "Yanzu duk wannan azabar da nake ciki bazaki iya zuwa ki kiramin wani bokan ya fidda ni ba, duk abubuwan da nayi a baya saboda ku nayi shi, amma ni yanzu abu ďaya da zaki min in fita daga wannan azabar bazaki iya ba.... babu wanda ya fahimci abinda Goggon ke faďa sai Mummy domin ita kadai ce a gefenta, Cike da damuwa Mummy tace "Shin har yanzu baki saduda kin san Allah daya bane? Har yanzu kina tunanin akwai wanda ya isa ya hanaka yin aure bare ya hanaka mutuwa, lallai kuwa in dai wannan azabar da kika sha ta tsayin watanni bata nunar miki hanyar Allah ba babu wata azaba da zata maidaki daidai, Mutuwarki itace alheri ga dukkan yan uwa musulmi, domin ke ďin anno----- wata damka Goggo ta kai mata wacce idonta bai nunar mata gefen da ta kaita ba saboda duhun da ya fara rufesu, a hanzarce Mummy ta mike haďe da fincikewa wanda hakan yayi sanadiyyar kai Goggo kasa, zafin faďuwar ya sanyata sakin ihun karshe wanda daga shi bata sake cewa komai ba sai fisga da jikinta yakeyi yana dukan gadon.. A wannan lokacin mai daukar rai ya ziyarci tsohuwa Goggo wacce tayi kisan ban mamaki kuma take tsoron mutuwar kanta, a lokacin Goggo ta dandanin azabar da matattun da suka mutu a sanadinta suka dandana, babu rayuwar da bata tunano ba kafin ganinta ya dauke baki ďaya.... *(Kullu nafsin za'ikatul maut,, Duk mai rai sai ya dandani mutuwa)*... *Anzo a banza an koma a wofi...* Furucin wata tsohuwa ne doki kunnen Mummy dake zaune tana kuka tana jiran azo daukar gawar Goggo, Wani sabon kukan ne yazo mata tanata adduar nemawa mahaifiyarta sassaucin ubangiji, *(Allah ghafuru raheem*).... Mutuwar Goggo ta taba makusantanta, domin ko babu komai rai daraja gareshi duk ko irin bakin halin wannan ran.. A ranar da akayi sadakar uku Baffa yasa aka kwashe kayan Goggo aka kaiwa tsofaffin mabaratan bakin titi, kayan kudinta ne kadai ya bawa Goggo domin itace magajiyarta shi kuwa a bangarenshi yace baya bukatar komai nata domin ta fita a sahun matarshi kafin rai yayi halinsa... *********** Har gurin mota Daddy ya raka su Anty Saude domin hirar da ta jashi da shi ba wacce zasu katseta bace, Cike da damuwa ita ta katse hirar bayan ta ajiye jakarta a bayan mota, "Ya jikin Musaddiq? Hope da sauki, Hafeez ke faďa mana jiya ashe bai ji dadi ba kwana biyu, Cike da basarwa Daddy yace "Alhamdulillah, jiki kam da sauki sosai, dan har ya fita ma yau.. "To mashaa Allah Anty Saude tace cike da farin ciki, jikanka dai yana neman haddasa min fitina, daga yaga zamu fita zai fara kuka saidai a barshi a gida, yanzu dai na barsu da Taheer zasu zo zuwa anjima suyi muku gaisuwa sai yayi dabara ya barshi can gurin Nadeeyah, "Murmushin dattaku Daddy yayi wanda ya tuno mata da samartakarshi yace "Babu komai, nasan rashin sabo ne, wata rana ba zaiso ya bar gidana ba, "In shaa Allah Anty Saude ta faďi tana dariya, motar ta shiga tana faďin "Kyan alkawari dai Kyari, ina nan ina jiranka,, Baki da matsala, in shaa Allahu gobe zanzo ai ni na faďa.. ya faďi cike da jaddadawa... "To saika zo bari mu wuce Allah ya kara hakuri, Ameen Daddy ya faďi haďe da rufe kofar motar... A tare motar su shigo cikin katafaren gidan, sai da kowacce tayi parking a mazauninta sannan suka fito rike da kaya niki niki.. Cike da ladabi Kamal ya gaisheta bayan ta sakko daga cikin motar, Amsawa tayi hannunta nakan kayan tace "Har kun dawo? Allah yasa dai bakuyi shirme a list dinnan ba, Girgiza kai Taheer yayi cike da gajiya yace "komai muyi momma, muje ciki ki gani, My dear kawo ledar nan ya karashe yana duban Junior dake rike da leda yana ja, "Noo Daddy, muje kaima naka akwai nauyi, daya daga cikin mai musu aiki ne ya karaso ya karbi dukkan kayan harda na hannun junior, sai a lokacin suka saki ajiyar zuciya suka wuce ciki ko wanne na dauke da gajiyar kasuwa data zaban kaya.. Buďe kayayyakin Shareefah takeyi tana duban Anty Saude dake cire warwarayen hannunta tana kallon kanta a mudubi, "Kaya Machaa Allah Saude, yanzu abu kadan ya rage a gama, sai kuma su *plaķiù'oòl..* Nasa Raahilar masu gari ta siyo ta taho dasu, naso ayi bikin nan a can Agadez saboda a nuna su ga dangi kuma ayi biki kashi biyu, na Yareemah mai jiran gado da kuma daurin auren tunda abun duk phàmèè ne, to Taheer ya hana yace dole ayi shi anan, amma ki faďa mishi daga an daura zamu wuce can sai ayi biki domin bazai yiwu bikin yazo min a yar karo ba alhali dukkansu nawa ne, dole a buga tambura agadez ta dauki bikin jinina, shakikai na wadanda zan bugi kirji ince su din nawa ne... Warwaron karshe Anty Saude ta zare ta dawo kusa da Shareefah, "Karki damu yar uwa, yin bikin a nan ya zama dole, bayan an daura sai kiyi yadda kike so babu wanda zai hana, kwana nawa ya rage, kedai kisa a fara shirye shirye a can kafin isowarmu.. Wannan ba matsala bane, biki kam za'ayi shi wanda ba'a taba yin irinshi ba a tarihi.. Shareefah ta faďi zuciyarta cike fal da murna... ********** Tsakurar indomien dake gabanta takeyi a hankali tana kaita baki, tunanin abubuwa da dama sun cika zuciyarta, ga tausayin halin da Musaddiq yake ciki ga kuma tausayin Taheer wanda ya sallamar da dukkan hope dinshi a kanta, tsaki tayi a hankali ta ture indomien gefe dan dama cinta takeyi badan daďi ba sai dan yunwar dake neman yi mata illah... "Nadeeyah in kin gama Daddy yace kizo.. kafin ta juyo ta ba Husnah amsa har ta bacewa ganinta, ruwa kaďan ta kurba ta gyara gyalen dake daure a kanta ta nufi parlon kamar wacce kwai ya fashewa a ciki... Cikin dariyar karfin hali Daddy yace "Amarya taho nan ki zauna mana, Cike da karyewar zuciya ta

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156