Chapter 40
Chapter 40
dauki Badariyya ta hada da Husna ta shayar dasu cike da kulawa... Tun a karancin shekarun 'yayan suwaiba suka fahimci zumuncin zuri'arsu sai in kana da kumbar susa, marasa wulakantasu aciki kadan ne.... Rayuwa Badariyya tun tana karama ta tashi a sangarce, bata ganin mutunci ko jin kunyar kowa, Hilal shine wanda tun fil'azal basa shiri, a gurinshi tasan ba mummy bace ta haifeta, ranar yaci dukan tsiya a gurin mummy, Tana gama dukanshi ya fita dan ko a jikinshi dama so yakeyi ya nuna mata ita fa ba yar gidansu bace ta daina kusu fi'ili...... Da wannan labarin zumunci ya faro, sila itace mace, uwa, wacce take da daraja, wacce Allah swt ya bata ragamar tafiyar da zuri'a, lallai Macce ta gari itace ginshikin alumma, domin gyara rayuwae ya mace kamar gyara alumma ne, mu dage tun yanzu gurin yi ma 'yayanmu maza adduar mace ta gari domin wayau ko dabara bazai basu ba, sukuma yayanmu matan ka sanya su zamto Mar'atus saliha ga mazansu..... Mrs Tijjani Shattimah.... [08/03 12:28 AM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣1⃣ By *Aysha Ya'u kurah* _HAKKI, HAKKI BABBAN ABU NE YAN UWA, KOMIN KANKANTARSHI MU GUJI DAUKARSHI DAN KANANAN ZUNUBBAI SUNFI MANYA ILLAH, DAN ALLAH MU KIYAYE HAKKIN JUNA_ *Cigaban Labari* Jiki a sanyaye ta dauko sarkar dake cikin akushin tayita juya ta a hannunta, tasan Baffa ya dade da mantawa da zaman sarkar shiyasa tayi mata muguwar ajiya, ko da wasa bata taba yunkurin sata ba, tun da taje ta tambayi kudin sarkar taji kudi ne masu tarin yawa ya sanyata kara yi mata kyakykyawan ajiye, ajiye sarkar tayi hade da tagumi. ya zame mata dole ta nuna musu gaskiyarta, shiyasa ta fito da sarkar dan bawa su Nadeeyah gadonsu, tasan wannan ita ce kadai mafita a gareta da diyarta, tasan in tayi hakan Muntari bazai yi mata zargin muguwar uwa ba, zaiyi mata kallon mai amanar da ta iya rike abu mai daraja saboda soyayyar uwarsu, wannan hanyar ita kadai ce abin da zai samar mata mafita... Rufe akushin tayi bayan ta dauko wasu magunguna a ciki, inda ta daukoshi nan ta maidashi ta fito parlor ta dauko leda mai kyau ta zuba sarkar a ciki, sannan ta shiga yin amfanin da magungunan domin rufewa su Daddy da sauran baki.... *1:51pm* Motaci uku ne suka shigo cikin harabar gidan Baffa, Motar Anty Reemah ce ta fara shigowa, sannan sauran kannenta suka rufa mata baya, Raliya ce zaune a gaban motar Anty Reemah, sai Zainab (kanwar Nadeeyah) da Hinad, a motar Radiya aka tara taron marasa mutunci, Raudha da Badar, Cikin kunci Badar take saboda Nadeeyah da Husnah sun shiga motar Hilal, duk yadda taso taja Husna suzo a mota daya taki saboda farin cikin tayin da Hilal yayi mata na shiga motarshi, ko kallon motarsu batayi ba ta wuce cikin gidan tana huci, a zaune ta samu Goggo hannu rike da carbi tana ja, Allah kadai yasan abin da take furtawa domin janshi kawai takeyi, babban tashin hankalinta bai wuce kar Baffa ya fada musu komai na labarin Atika ba, burinta su sameta ita kadai ta hada musu kirkirarren labari ta fada musu saboda tseratar da auren yarta, jikin ta Badar ta fada ta fara zuba mata shagwaba, gyaran murya Goggo tayi ta mata nuni da carbi alamar ja takeyi, sauka tayi ta daura kanta a kan cinyarta, damuwar da Goggo take ciki ta hana ta fahimtar damuwar dake kan fuskar yar lelenta... Sallamar su Anty Reema ne ya sanya Goggo sakin Murmushi hade da tattara hannu guri daya tana musu gaisuwa dan su gane carbin take ja bata son a katseta, neman guri sukayi suka zauna suka bude flow din hirarsu ta kasuwanci, shigowar su Nadeeya ne ya katse musu hirar saboda yadda Goggo ta yafito su da hannu ita da Zainab, a darare Nadeeyah ta sauke zainab suka matsa kusa da ita suka durkusa zasu gaisar da ita tayi saurin durowa daga kan kujerar ta hadesu ta rungumesu hade da kuka mai karfi, "Allah sarki Suwaiba, ganin jininki ya tuno min ke, inama ni mutuwa ta dauke ta barki cikin 'yayanki, inama zan juyo da hannun agogo baya da na nuna miki irin muhimmacin da kike dashi a cikin rayuwata, cike da mamaki daukacin mutanen parlon ke kallon Goggo, Ciki kuwa harda Baffa da ya sanyo kanshi cikin parlon ya tarar da abun da idanuwanshi basu taba tozali dashi ba, yaran da ko cikin parlon basa samun albarkacin shiga bare har su samu darajar runguma, wani dadi ne ya ziyarci zuciyarshi yayi tunanin mutuwar Suwaibar ce ta kadata haka, da sallama ya katse shurun mamakin yace "yau gidan nawa cike yake da matana kenan, sai wacce na zaba, Murmushi dukkansu sukayi suka gaida shi hade da cewa ai dukkan mu zaka hada, Badariyya ya kalla da ta rike kanta saboda bugeta da Goggo tayi gurin sakkowa daga kujera, "a'a Amaryata me akayi miki naga kin rike kai? sakin kan tayi ta turo baki tace "ba Goggo bace ta bigeni, kallonta Goggo tayi tace "yi hakuri Badariyya ban kula bane, hankalina nakan marayun Allah, babu uwa babu uba, kai wannan rayuwa abar tsoro ce, Anty Reemah da abun ya bar bata mamaki tace "dama haka ne Goggo, Allah baya barin wani dan wani yaji dadi, ta yiwu mutuwar ita kadai Allah ya ga zata zamto hutu a garesu, shiyasa yayi gaggawar daukesu, Allah sarki Mama Suwaiba,, wani kukan Goggo ta kuma kecewa dashi tana dada kankame zainab, kallon tsoro zainab din take mata shiyasa ta saki kuka ta fisge kanta ta koma jikin Nadeeya, share ma juna hawaye sukeyi gunin tausayi, shigowar su Mummy dakin ne yasa duk suka mike domin bawa Daddy gurin zama, bayan yan gaishe gaishe Baffa yace " yau gida yayi albarka, dariya Daddy yayi ya tsuguna ya gaishesu, bayan yan hirarraki Daddy ya gabatarwa da Baffa dalilin zuwansu, ya kuma kara da cewa "kayi hakuri Baffa nayi maka shishigi a cikin alamarin gidanka, inason sanin dalilin kiyayyar ne saboda yana neman zama min matsala a cikin Zuri'ata... Kuka Goggo ta saki tace "Babu kiyayya cikin zuri'ata da na gina ta shekara da shekaru, kasan zumunci yanzu ya zama na yan zamani, amma ni a gurina kowa daya yake, bana banbanta su,, gyara zama Daddy yayi yace "nasan bakya banbanta su, domin dukkansu 'yayanki ne babu bare a ciki, amma ya kamata ku tsawatar akan yadda akayi ma zumunci rikon sakainar kashi, bana san yadda abubuwa suka kasance a nan gidan su kasance a cikin 'ya'yana, bazan dauka ba, inason 'yayana su fahimci muhimmancin mai shi da marar shi, banason dattin duniya ya zamana sillar yankewar zumuncin 'ya'yana, shiyasa nazo a warware min komai kuma ayi ma tufkar hanci, Gyaran Murya Baffa yayi zai fara Magana Anty Reemah tayi saurin cewa "yi hakuri Baffa zan katseka, dan Allah so nakeyi ka fada mana wacece *ATIKA* a duburce Goggo ta waigo ta harareta ba tare da sun hada ido ba, a zuciyarta tace "kaji shegiyar yarinya, ana neman kai magana karshe ba tare da an bullo da maganar Atika ba ta sako zancen ciki, kara gyara zaman carbinta tayi tana kallon Baffa dake shirin basu labarin Atika.... Kuka sosai Nadeeyah da Hafeez sukayi najin ba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156