Skip to content

Chapter 35

Chapter 35

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

gida, addua takeyi a zuciyarta na Allah yasa yayarta na gidan, ita kadaice zata iya taimkonta daga ukubar da zasu mata, kamar daga sama ta jiyo sallamarshi, kallonshi tayi ta kauda kai tace "Ameen wa alaikum salam, ina yini, wani sanyi ne yaji ya ratsashi na jin daddadar muryarta, Amsawa yayi yace "lafiya kalau malama Suwaiba, dago kai tayi cike da mamaki tace "laaa sunana, a ina ka san sunana?, daga kanshi sama yayi yace "wahayi akayi min da sunan, kuma aka ce inzo nan in sameki, rike baki tayi ta daga kai sama tace "a can sararin samaniya? Gyada kai yayi yana murmushi yace "kwarai kuwa, ko kina tantama ne, cike da nutsuwa tace "kwarai ba tantama nakeyi ba, yarda ce banyi ba saboda na karanta a littafi, manzanni kadai ake wa wahayi, kuma nasan a cikin duniyar nan da azzalumai sukayi yawa babu tabbacin samun wani annabi, kuma ai annabin Allah shine karshen annabawa, dan Allah in ma gatse kakeyi to ka daina domin ina tsoron wani ya samu zunubi ko yayi shirka domin ni, "Ya ilahi ya fadi a zuciyarshi ya kalli Abokinshi dake cikin mota yace "kaji Kalamai daga bakin fasihiyya ko Abbakar, kallon motar tayi tace "laa uncle Abu ina wuni, fitowa yayi a motar yana dariya yace "lafiya kalau Suwaiba, anyi hutu ana jin dadi za'a koma gida ko, murmushi kawai tayi a zuciyarta tace wani hutu, ita da za'a barta ta kare rayuwarta a makaranta ai da taji dadi, katse mata tunani Abbakar yayi yace "wannan abokina ne, sunanshi *MUKHTAR KYARI* ganin irin masifar da yar uwarki take miki ne yasa shi tsayawa ya baki shawarar ki dage ki dinga ramawa, kyawawan mata da tsiwa aka sansu, ke kuma hakurin naki yayi yawa, kallonshi Mukhtar yayi yace "to sannu koma mota, nagode da ka tayani fada, dariya sosai Abbakar yayi ya wuce cikin mota yana fadin 5mins na baka, kasan we have alot to dzoo, a gaugauce ya tambayeta ko zai iya sauke su a gida daga nan sai yaga gidan nasu, kallon Leemah tayi da ta waigo tana hararar su tace "bari in tambayi yar uwata, ajiye akwatin tayi a kasa yayi saurin daukarsu ya zuba a boot, ya shiga motar yace "abokina kai zaka musu magana su shiga dan dakyar waccan masifaffiyar ta yarda su bimu, magana daya Uncle Abu yayi musu suka shiga motar, a kofar gidansu yayi parking, da sauri Leemah ta bude motar ta shige gida gudu, jiki na rawa Suwaiba ta bude motar tace "ina akwatinan mu? Bude boot din yayi ya fito da akwatinan yace "muje in rakaki, nauyinsu yayi yawa, a'a tayi saurin cewa, hade da mika hannu, Dan Allah ka rufa min asiri, fada za'a min a gida, "let her go kyari, bakasan condition din da take ciki ba, sakin akwatinan yayi tayi saurin dauka ta ruga cikin gidan da gudu, bin ta yayi da ido har ta kure cikin gidan sannan ya shiga motar ya tada suka wuce.... Mrs Tijjani Shattima..... [04/03 12:44 PM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 2⃣8⃣ By *Aysha Ya'u Kurah* Tun daga zauren gidan take jiyo masifar Ma'u hade da kukan Leemah, sharri kala kala tayi mata sannan tace "ta hadu da saurayi tanata shige mishi har ta rokeshi ya kawo su gida, innalillahi wa inna ilaihir rajiun kawai suwaiba ke furtawa a cikin ranta, da sallama ta shigo gidan ta ajiye akwatinnan ta tsuguna har kasa ta gaida Ma'u, matsowa kusa da ita tayi ta daga hannu ta kwada mata mari, Halima sa'arki ce da zaku hadu da kawayenki kuyi ta cin mutuncinta, ke dan uwarki ke kika bawa kanki kokarin, au dan na yarda kun shiga makaranta daya, shine zaki nuna zakewa ki nuna kinfi ta iya komai, bulala Leemah ta miko ma Goggo tace "ga yaren da tafi ganewa nan Goggo, karbar bulalar tayi ta fara zuba mata tana cewa uban waye ya saukeku a kofar gida, yanzu dan rashin kunya kina ganin yayunki basuyi aure ba ke har kina da tsaurin idon tsayawa da saurayi, to wallhi in na kara ji da ganin kin tsaya da saurayi tun yanzu sai na miki illah, banason rashin ido a gurin y'a mace wallahi, bulalar da zata kai mata na karshe ne ya sauka a jikin yaya zainab (Bingel) da ta shigo gidan a lokacin, dago suwaiba tayi tana share mata hawaye itama hawayen take tace "haba Goggo, kowa ba rabonshi yake samu ba, yanzu wannan abun da kikeyi shine Allah zaisa mu samu miji ko me, ki duba kiga yadda na girma na rika a gida babu mashinshini, haka Halima babu wanda ya taba furta mata kalmar so duk ko da irin kyan da muke dashi, a cikin mu Allah ya sanya suwaiba nada farin jinin da duk ta fita sai ta samu mai cewa yana sonta, ai sai mu godewa Allah, wani kukan ne ya kufce mata na tuno saurayin da tayi arangama dashi a bikin Nafisa jiya mai cike da barkwanci da halin kirki, a zuciyarta tana takaicin yadda yayi mata nisa ta ko wani irin bangare saboda matsayin shi, daki taja suwaiba suka shige ta bar Goggo nata banbamin bala'inta, itama tana takaicin bakin jinin da yaranta suke dashi, babu irin maganin da batayi musu ba dan su samu mashin shini amma a banza, to ita kuwa ta yaya zata yarda ta bar suwaiba ta kula samari alhali yaranta duk ba mashin shini, masifar ta cigaba dayi kamar zautacciya zuciyarta na mata zafin balbalin wuta..... Albishirinki Ma'u!!! Kai yau cikin farin ciki nake wallahi, Goro ta fadi tana zuba mishi ruwa a kofi, baibi takan ruwan ba ya kwala kiran suwaiba, da sauri ta fito yace "akwai bako a waje kira Yayarki kuje ta rakaki, kuma kar ku dade, cike da faduwar gaba Ma'u tace "baka ce min komai ba kuma kace yara su fita, yanzu sai aga yara sun fita zance kai ba abin kunyar ka bane, "shiyasa nace Zainabu ta raka ta ai, saboda idon mutane, zuciyar ma'u kamar zata fito tace "to meye albishir din, gyara zama yayi yace "kinajin labarin Alhaji Garba Kyari mai fata ko?, gyada kai Ma'u tayi kirjinta na tsananta bugawa, yace "to danshi ne yaga suwaiba yake so, kuma da aure, nace yaje ya turo magabatanshi mu tsayar da maganar aure, wallahi Ma'u bakiji dadin da nakeji ba, ko ba komai zan fara aurar wa, mutanen unguwa zasu bar zundena, yake ma'u ta shiga yi tana fadin madallah Allah ya sanya alheri, Ameen.. Baffa yace ya mike ya wuce daki zuciyarshi wasai bai ko lura da yanayin ma'u ba, shidai a yadda yakeji a ranshi, yasan suwaiba ta gama samun gatan duniya saidai kuma ta roki lahira.... Tun da suka fito Bingel tayi tozali da Mukhtar cikin kayanshi riga da wando fela, gashin nan Afro ya tajeshi ya mike sosai, hankalinta yayi kololuwar tashi, shine, shine wanda ta ganshi a gidan Nafisa, karasowa yayi gurin kafin su iso yace "barka da fitowa sahibar ruhina, ya ilahi, suwaiba kamar zata nutse ta damki hannun yayarta hade da rufe fuskarta cikin hijab, no, no, no, wannan kunyar cutar dani zatayi, kiyi hakuri ki dago kanki ki kalleni, sakin hannun Bingel tayi ta ruga cikin gida da

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156