Skip to content

Chapter 154

Chapter 154

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

bata san shakuwar da sukayi da Abubakar tun suna makaranta ita ce ta sanya ďaya baya barin daya ba, a ranar da ta yanke shawarar faďa mishi abinda ke ranta a ranar taji mummunan labari daga gareshi na haďuwa da wata yar makaranta wacce ya kwallafawa ran aurenta, cikin sanyin jiki ta tattara takardunta tace ma Uncle Abu bata da lafiya, bata tsaya duba kulawar da Kyari ke kokarin nunawa a gareta ba ta wuce cikin gida idanuwanta na zubar da hawaye, tasan tabbas kyari ya faďa cikin tarkon so domin a yadda ta kula baya son kula mata gashi da yawan kushesu tasan wannan din da ya gani ta dabance, a daren ranar taci kuka har ta gode Allah sannan ta roki Allah da ya kawo mata wanda zai aureta cikin gaggawa ko ta samu ta mance *Mukhtar Garba Kyari*..._ Washe gari da safe da taje gaida Mahaifinta Alhaji Halliru Ďan Magarya, bayan sun gaisa yake tambayarta yaushe zasu fara jarabawa, cike da damuwa ta amsa mishi da cewa "Jibi in shaa Allah, "Mashaa Allah Mamana, Allah yasa ku rubuta alkhairi, yasa ku fito da sakamako mai kyau, tunda an kusa zana jarabawar karshe sai maganar aure, shin kina da wanda kike so? nasan dai bazaki rasa ba kar inyi miki katsalandan, Kauda kanta gefe tayi dan bata so sam mahaifinta ya gane halin da take ciki tace "A'a Pappa, duk wanda ka zabar min ina maraba dashi, Cike da murna yace "Mashaa Allah, shiyasa nake daďa sonki a cikin raina, sai yanzu na fahimci dalilin da yasa Allah ya mallaka min ke kadai, saboda yasan ke ďin daya ce tamkar da dubu, Allah yayi miki albarka, ki shirya gobe, Haroun Yallo dan wazirin Agadez zaizo neman aurenki, satin da ya wuce da naje Agadez na bawa mahaifinshi ke, shi mazaunin nan ne, a nan yake kasuwancinshi, Allah ya sanyawa haďin albarka, Amsa mishi tayi da Ameen sannan ta tashi ta wuce ďaki tana kuka ririss.... Bayan tayi candy da sati biyu aka daura aurenta da Haroun, da fari ta dan samu matsalar zama dashi saboda tunanin kyari da takewa son da bai san tanayi ba, sai daga baya kyautatawar Haroun ta kashe boyayyar soyayyar cikin zuciyarta... Ashe dai soyayyar ba mutuwa tayi ba, ashe doguwar suma tayi, wanda a yanzu ruwan soyayyar Daddy ya farfaďo da ita... Ajiyar Zuciya tayi tace "Wannan karan bazan rasaka ba Kyari, koda zuciyarka bata sona zan koyar da ita yadda zatayi shi, a yanzu na haďu da kai bayan na cire rai da sake yin wata soyayya bare har inyi aure, haduwarmu dakai ta nuna min tabbas kai ďin nawa ne koda kuwa ba nawa bane ni kadai, rabuwa a tsakanin mu babu ita saidai mutuwa ka raba, tana kaiwa nan ta tashi ta nufi daki dan sakeyin wani wankan.... Da ido Shareefah ta bita tana mata adduar samun abinda take so, domin Allah ma yasan tayi hakurin rashin miji a gefenta, yadda ta damu da maganar Kyari ta tabbatar tana matukar sonshi, zata tayata da addu'a in alkhairi ne Allah ya tabbatar..... Bayan isha'i Daddy yazo gidan, tarba mai kyau ya samu daga dukkansu harda Taheer wanda a yanzu yake matukar jin kunyar haďa ido dashi, kimarshi ta karu sosai a idonshi.. Bayan sun gama gaisawa Anty Saude ta cika gabanshi da abinci da sha, zama tayi a gefenshi tana mishi hira yana cin abinci suna tuntsira dariyar tuna baya, sosai sukayi hirarsu har Daddy yakai karfe goma bai san ya kai ba, yayi matukar jin daďin hira da ita, zuciyarshi da tayi mishi nauyi ta rage saboda ta tuno mishi da memories ďin baya, lokacin yana kan ganiyarshi, bashi da wani bacin rai sai tarin farin ciki musamman lokacin haďuwarshi da Suwaiba.... Rike murfin motar tayi bayan ta gama jin tambayarshi na "Bayan biki zaki koma can canada ne? Kallonshi takeyi cikin ido dan jinta takeyi kamar yar budurwar da ta fara tsayawa da saurayi tace "In ka shirya komawa can me zai hana! Dariya Daddy yayi yace "Wato dai kin maidani joker, karfin ramawa ne bani dashi da kema kinsan bazaki sha ba, dare na daďa yi bari in wuce, Ina miki fatan alkhairi haďe da murnar samun suruka irin Nadeeyah, Allah ya basu zaman lafiya... "Ameen Anty Saude tace haďe da rufe mishi kofar cike da tausayawa halin da ďanshi yake ciki, ya zatayi ta iya yin wannan taimakon? Ya zatayi da zuciyar tata ďan in ya rasa Nadeeyah, Addu'a ita kadai ce mafita a garesu domin Allah shine kadai mai sassautawa.... Bayan tafiyarshi da awa ďaya ta tura mishi text din godiya da ban gajiya sannan tace "Akwai muhimmin abun da zan faďa maka, in shaa Allahu bayan biki komai zai ziyarci ji da ganinka, have a nice dream *Joker* ... Dariyar rashin shiri Daddy yayi ya kashe wutar dakin da Musaddiq yake ya fita daga dakin, saida yayi shirin kwanciya sannan ya tura mata cewa... *Same Sauden Himma, Amaryar gandiroba...* Dariya sosai tayi na tuno sunan Himma,, gandiroban da ya like mata lokacin yarintarta, ashe bai manta ba ta furta a hankali cike da nishaďi, *Soyayya ruwan zuma, ita soyayya babu ruwanta da tsufan mutum, in ta kama ka dole ta zautaka*..... Good morning bride, Maleekah ta faďi tana haďawa Little Nadeeyah tea, Rau Rau Nadeeyah tayi da idonta haďe da kwabe baki zatayi kuka, "Hey, ba ruwana fa, kiyi saving kukan nan zuwa anjima ki sakarwa Abbu shi, kinsan yau zasu zo bikin unknown jika... ta karashe cike da zolaya, kafaďunta Nadeeyah ta daka haďe da haďiye da kukan dake shirin zubo mata, Dariya Maleekah tayi tace "Let it flow beb, kinsan in daďi yayi maka yawa hawaye kansu dadin fita sukeji, My Inlaw da ciwo ke da kuka, nd for once baki taba tunanin zuwa dubashi ba, haba Nadeeyah, if nt for him sai kiyi for his child, kinsan duk inda kikaje that child will always connect u saboda ya riga ya haďaku... Share hawaye Nadeeyah tayi ta juya ma Maleekah baya, zancen zuci takeyi wasu hawayen na sake bulbulowa, rabon da tasa shi a idonta tun ranar mutuwar Goggo da ta shiga ďakin dan duba jikinshi lokacin yana bacci, bata san abun da zai sake sawa ya ganta domin bata san yi mishi fami akan abun da take da yakinin yana yunkurin mantawa dashi, kwana uku ya rage ta zama mallakin wani, runtse idonta tayi saboda hangota cikin wata sabuwar rayuwa, rayuwa ba tare da Mussadiq ba, wanda ya fara koyar da ita soyayya, wanda ya shayar da ita gubar soyayyar da ya illata ruhinta... "Go nd see him for the last tym Nadeeyah, atleast zai samu sukunin cewa kin damu dashi, kaddara ce zata rabaku, plsss Nadeeyah.. ta karashe haďe da hada hannayenta guri ďaya tana rokonta... duk wadannan maganganun cikin harcen turanci take yinsu... Share hawaye Nadeeyah tayi da Hijab dinta ta fara tafiya dan bin umarnin yar uwarta, tana zuwa kofar dakin taji kafarta ta fara rawa, dakyar ta iya murďa kofar tana addu'ar Allah yasa yana bacci, Ajiyar zuciya tayi bayan ta gansu kwance suna bacci shi da junior da fushi ya hanashi kwana a gurinta, shagala tayi cikin kallonsu tanajin wata irin nutsuwa na saukar mata a curarrar

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156