Chapter 20
Chapter 20
gurin ke yi.......! Mrs Tijjani Shattima...... [07/03 6:31 AM] fareedah: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 2⃣2⃣ By *Aysha Ya'u Kurah* Share zufa Goggo tayi cike da tashin hankali tace "To Allah ya kaimu, sai kunzo, Ajiyar zuciya Mummy tayi tace "to Goggo, amma bakya ganin fadin sirrin zai iya kawo karshen zama na da Muntari, "Ko kusa, Goggo ta fadi cike da dakiya tace "in ya rabu dake ina zai kai yaran da kika haifa mishi, ai zancen rabuwa babu shi, domin kuwa yanzu girma ya kamaku, ki kwantar da hankalinki ni nasan abun da zanyi..... Ajiye wayar Goggo tayi ta shiga safa da marwa a cikin dakinta, Gumin dake tsatstsafowa a fuskarta bai tsaya ba duk ko da irin sanyin fankar dake kad'awa a dakin, jiki na rawa ta haye can saman gadonta mai rumfa dakyar tana numfarfashi, ta mika hannu tayi ta dauko wani akushi, bude cikin shi tayi ta zuraa mishi idonuwanta duk jikinta a sanyaye kamar wacce aka tsinkewa lakka, nan take tunaninta ya tafi can shekaru da dama da suka wuce... Shekarun da Allah subhanahu wa ta'ala ya arawa Goggo su, Shekaru masu cike da abubuwan al'ajabi wadanda aka shafe tunaninsu a doron kasa... "sau tari Allah na arawa mutane lokaci ko zasu samu su gyara abubuwan da sukeyi marasa kyau, amma ita Goggo a gareta gani takeyi cancantarta ne yasa har yanzu Allah bai mata komai ba, saboda yasan irin gwagwarmayar da tasha .... *********TARABA 1969********* Kauyen *GEMBU* dake Karkashin karamar hukumar *SARDAUNA* a cikin jahar TARABA, Babban kauye ne wanda yake cike da fulani arna da kuma tsirarun musulmai, Irin arnan da babu abinda sukeyi a rayuwarsu sai kiwo da noma, mazan su da matansu, Hatta abin da zasu ci ma su suke noma shi da kansu, Kauye ne inda babu wanda ya damu da addini bare har sukai ga assasa shi, "walau Addinin kirista ko na musulunci" kowa harkar gabanshi yakeyi, da yawansu saboda rashin addini basu dauki kowacce irin mugunta a bakin komai ba, komai suke aikatawa a garin su a ganinsu dai dai ne...... Ihun shanaye ne kawai ke fitowa daga cikin wagegen bukkar gidan JAURO, Samarin dake zaune a kofar gidan kowa ya fara gyara zaman jarkarshi dan sun san yanzu za'a fara kiran layi.. Cike da gadara ya ajiye jarkarshi a gaban ta kowa, ya koma jikin gidan yana sakuce hakorinshi.. Shuru sauran mutanen sukayi saboda tsoronshi da sukeji, Cike da damuwa saurayin da ke zaune tun safe a gaba ya daga jarkarshi a kasa, ya kuma ga in yayi shuru to fa za'a cuce shi, Mikewa yayi cikin sanyi ya fara magana da gurbatacciyar hausarshi ta kabilun fulani "Tun asuba nake nan, kayi hakuri can tsauni zan kai madara kaga da nisa banasan dare yayi mana, bude idoo saurayin yayi cike da gatsali yace "amma kai bako ne anan ko? gyada kai saurayin yayi yace "eh a can tsaunin Mambila nake, nazo siyan madara ne akwai bakin da suka zo daga Cameroon zasu tafi anjima da maraice kuma suna son madara irin ta gidan jauro, shine nazo siya, kayi hakuri a bamu, tare muke da yar su gata can a zaune duk ta gaji, Dago kai saurayin me suna SHAHO yayi ya kalli gurin bishiyar da saurayin ya nuna mishi, kyakyawar budurwa ya hango zaune a gefen bishiyar fuskarta da alamun gajiya, da ganinta kasan ba yar nigeria bace, jikinta rufe yake ruff da bakar riga har kanta, sandar dake hannunshi ya ajiye yace "a zuba maka in ma jarkar da ka kawo sun kai goma, kanshi ya fara kakkabewa ya fara nufar inda budurwar take, Da sauri saurayin ya taro shi yace "ina zaka je? Yarinyar nan bata jin hausa haka fulatanci, larabci kadai take ji, kayi hakuri muyi abinda ya kawo mu, mu tafi mu bar muku garinku, wani irin kallo Shaho yayi mishi, baice dashi kala ba ya bi ta gefenshi ya karasa kusa da yarinyar, gyara rigarshi yayi zai zauna saurayin ya tureshi ya tare gurin zaman, "Na fada maka, yarinyar nan bakuwa ce, alama yayi mata da hannu yace ",ga motar da muka zo can je ki shiga ki jirani, gurin kwarababbiyar motar shanun ta nufa ta haye tana ta kalle kalle jikinta duk a mace, wani irin ihu Shaho yayi har saida matan dake gefen bukkar suka tsaya da tatsar madara saboda firgici, saurayin dai bai girgiza ba sai ma kara komawa jikin motar da yayi ya tsaya, sauran mutanen gurin suna kallonshi cike da mamaki suna tsoron irin hukuncin da Shaho zaima saurayin, tunkarar motar shaho yayi gadan gadan, cikin harshen larabci saurayin yayi wa budurwar magana, a firgice tabi umarnin shi ta kwanta kan kujerar hade da runtse idonta, yana isowa gurin ya dunkule hannu ya kai wa saurayin naushi, gocewa yayi ya daki karfen motar har saida ta girgiza, kafin ya kai mishi wani naushin saurayin ya kai mishi a baya, nan fa suka fara kokawa sosai, ganin da shaho yayi saurayin yafi karfinshi yasa shi zaro wata sharbebiyar wuka ya zabtari naman gefen kanshi, Nan fa jini yayi tsalle ya fallatsa har fuskar budurwar, wani irin ihu ta saki tana fadin "Ya subhanallah, Ya Hayyu ya kayyum bhi rahmatika astagithu" cikin zafin nama saurayin ya sake yin kan shaho, kafin ya karaso kusa dashi ya sake luma mishi wukar a ciki, ihu mutanen gurin suka shiga yi, wasu na tausayin saurayin wasu na kuranta shaho, kaca kaca shaho yayi wa saurayin da wuka sannan yayi wani ihun murnar ganin ya samu galaba akan saurayin, bakin motar yayi yana maida numfashi, "wayam" ya gani babu kowa a ciki, dube dube ya fara yi yana fadin ina ta shiga, ina yarinyar nan ta shiga, babu wanda ya lura da sanda yarinyar ta bacewa gurin, nan Shaho ya hargitsa gurin da nemanta... Da sassarfa ya isa gida ya turo kofar gidan gam harda kara sanya wani karfe, "Ma'u, Ma'u am, da sauri ta fito daga sakarkari hannunta rike da yar jinjira, lafiya dai irin wannan kiran me muka samu ne, sauke budurwar yayi a bayanshi ya kwantar da ita akan wata tabarma, ajiye jinjirar ma'u tayi cikin daki kusa da wata yar yarinya da bata wuce shekara 8 ba, da sauri ta fito tana mai zumudin sanin inda mijinta ya samo yar MAKKA, dan su duk wani balarabe a gurinsu dan Makka ne, " kawo di yam ma'u, ya fadi yana mata firfita hade da share jinin fuskarta, ruwa ta debo cike da koko ta mika mishi ta zauna a kusa dashi, a hankali ya fara shafa mata ruwan a fuskarta da hannunta, Ajiyar zuciya tayi mai karfi hade da fashewa da kuka tana kiran sunan "HABEEB" toshe mata baki yayi da sauri saboda jiyo ihun su shaho a bayan gidanshi, cikin harshen filatanci yacewa ma'u tayi saurin shigewa daki da ita, kama hannunta tayi suka shige can kuryar daki ta turata cikin wani yayi ta daura mata kaya a kanta, kafin su kai ga taba kofar bukkar mai gidan ya fito daga gidan yana mika, tsayawa su shaho sukayi yace "Kai Baffan Bingel da Boddo kaga wata yarinya Makka da bakin kaya, hamma ya kakaro yace a ina zan ganta ni da na tashi daga bacci yanzu, wucewa sukayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156