Skip to content

Chapter 104

Chapter 104

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

jin da Marakisiyya tayi ba wata muryar dake sake fitowa daga bayanta ya sanya ta karasawa kusa da Badar hade da toshe mata baki, ihu marar fita Badariyya takeyi tana mutsu mutsun neman kwatar kanta, "shhhhh, taimakonki zanyi, zauna ki kuma yi shuru, ni mutum ce yar uwarki, kamar yadda aka kawoki nan, nima haka aka kawo ni, shekarata ta biyu kenan a gidan nan, haihuwata ďaya talll, sunana Marakisiyya, a garin katsina nake, zanso jin labarinki sannan mu haďu mu nema wa kanmu mafita, gobe da safe kizo bayan Bukkar yara zanyi zaman jiranki.. tana kaiwa nan ta saki bakin Badar ta mike ta fita da sauri, tayi mamakin da taji muryarshi kuma bata ga bayyanarshi ba, har ta karasa bukkarta tana addu'ar Allah yasa bai jita ba.. Gimbiya Sailuba.. ita ta dauke hankalinshi daga isa gurin su Marakisiyya, yadai san dalilin zuwanta bai wuce dan neman mafita ba, wata dariya yayi haďe da maida kanshi jikin Sailuba, "yaro bai san wuta ba sai ya taka.... Badar kuwa tun zuwanta gidan bata taba jin abin da ya faranta ranta kamar maganar Marakisiyya ba, juyawa tayi ta tsinci kanta da murmushin jin dadin ta kusa barin gidan ta koma ta samu Masoyinta, abin kaunarta Musaddiq, tunanowa da tayi Nadeeyah na cikin rayuwarshi ya sanya zuciyarta tafasa haďe da sake saken muggan abubuwan da zatayi mata bayan ta kubuta a gurin..... (wasa farin girki) Jakar kayanta ta janyo ta sauko parlon haďe da sake kiran Raudha karo na uku, daukar wayar Raudha tayi haďe da latsa hon, "Gani a gate, kashe wayar Radiya tayi ta mike ta nufi kofar fita daga parlon, Da sauri Raudha ta kashe motarta ta fito ta nufi inda Radiya ke tsaye, "Anty dan Allah mu koma, wallahi bazaki tafi yau ba, sai kinyi wannan sati biyun da muka ce, wallahi sai mun cika burin mu, in kika tafi ma ai dadi zata ji ta samu damar juyashi san ranta, nayi waya da Mummy tun asuba na shirya mata maganganu, tace zata turo Faida gobe ko jibi, sannan tace zata nemi Badariyya tasa ta dawo daga makaranta, gara duk mu hadu mu kauda wadannan dangin tsiyan cikin zuri'armu, Ita kuma Husna mu zuba mata ido, tunda ita taji ta gani babu wanda zai tursasa ta, in taji wuya ta nemawa kanta mafita, bata bar Radiya tayi magana ba ta dauki jakarta ta bude kofar ta jata suka koma ciki, kafaďunta Radiya ta dafa tace "Raudha, bakiji abinda naji bane, wallahi yanzu haka kunyar ganin Little nake, nidai bazan iya ba, in zauna gidan yaro kullum yana zuba rawar kafa akan yarinya karama, ni kuma su barni da saurare, kuyi keda su Badariyyan kawai, ni kam na girma da wannan,,, "Ohhhh Anty, kunya ai shi zai jita, ke kam zama zakiyi a cikin gidan dan ki dinga lura da movements dinsu, ni kuma zanyi duk wasu kullin da suka dace, sannan Faida da Badariyyah sune zasuyi completing aikin in shaa Allah, zaunar da ita tayi ta gama tsarata tayi convincing dinta har ta yarda zata kara sati ďaya a gidan, cike da farin ciki Raudha tace "ko kefa, ai mu ya kamata mu maidashi hanya, in muka barshi ya cigaba da haukar kuruciyya ai sai ya bata rayuwarshi kan wannan yarinyar marar asali, cire hijab dinta tayi ta nufi sama tace "ina zuwa Anty, ita dai Radiya bata ce komai ba sai gyaďa kai kawai da tayi.... Bugu da Murda kofar da Raudha tayi yayi daidai da fitowar su daga bayi, sake gyara towel din da ya naďota yayi ya sake rungumeta cikin kirjinshi haďe da cewa "ina kwana Anty, plss come nd help me sai kuka takeyi, yadda yayi maganar shima kamar zaiyi kukan ya sanya Raudha yi mishi wani irin mugun kallo, "Me na faďa maka jiya? yanzu dan rashin kunya little bazaka iya jiran Anty ta bar gidan nan ba, bansan ranar da ka lalace har haka ba wallahi, kai da kayi barnar sai ka gyara da kanka, sakarai kawai... tana kaiwa nan ta fita daga dakin haďe da buga kofar da karfin gaske, kwantar da ita yayi yana share mata hawayen da yayi kaca kaca a fuskarta, "sorry plss, bari insa miki kaya muje asibiti, hannunshi ta kama haďe da girgiza kanta tace "ka barshi, ba sai naje asibiti ba zan sami sauki, rike hannunta yayi sosai yace "Noo ki bari muje, banasan wannan kukan da kikeyi plss, kanta ta juyar gefe tace "um um, ka bari kawai, ďago kan yayi ya zauna haďe maidota jikinshi yace "dan Allah ki tashi mu tafi, kinga jikinki yayi zafi, "Ni bazani ba, in naje kace musu meke damuna? hawayen da ya gangaro bayan ta gama maganar ya share mata ya rasa yadda zaiyi, murya a raunane shima kukan yake shirin farawa yace "To me kike so inyi miki ki daina kuka, "ka kyaleni, zan taimaki kaina, wayarshi ya mika hannu ya dauko ya latsa number Anty Reemah, "Little ango, an tashi lafiya?, "lafiya kalau Anty, yadda taji muryarshi yasata mikama Zainab plate din arish tace "maza kije ki karya kafin su Adeel su fito.. "Lafiya Diku? ya naji muryarka haka? Cikin Muryar shagwaba yayi mata bayanin komai, dariya tayi tace "To ni me zanyi, kai kayi barnarka ni kuma sai in maka magani, "Ni dan Allah Anty ki faďa min, bata tsaida dariyarta ba tace "bani Nadeeyah, da sauri ya kara mata a kunne yana cewa "kiyi magana, Anty Reemah ce, A kunyace ta gaisheta, cike da zolaya Anty Reemah tace "Allah yasa na samu ďa, kuma jika, rufe ido Nadeeyah tayi kamar tana gabanta, "ki kama jikinki Nadeeyah, ki sa ruwan zafi da gishiri ki zauna a ciki, sannan kisha tea mai zafi ki hada da paracetamol, kina yin hakan zakiji sauki, Allah ya kara lafiya, karki raga mishi ki bashi wahala kamar yadda ya baki kinji ko, Murmushin karfin hali Nadeeyah tayi tace "nagode Anty, ki gaida min su Hinad, "zasuji my sister, ki kula sosai da mijinki da kanki, yanzu ku biyun nan kune sirrin juna, ku kare ma kanku mutunci, in abu ya dameki ki sameshi ki fada mishi, ku tattala rayuwarku ke da shi, Allah ya baku zaman lafiya, "Ameen Anty nagode sosai, "bakomai dear, a tashi a kama jiki, sai na jiki, bata jira amsarta ba ta kashe wayar, ta cigaba da ayyukan gida.... Taimaka mata yayi ta koma bayin sannan ya fito ya sanya jallabiya ya fita da sauri dan nemo magunguna da abun karyawa, ko kallon inda su Raudha suke baiyi ba, hakan ba karamin dugunzumasu yayi ba suka mike suka nufi dakin da Nadeeyar take.. Jin karan ruwa ya sa su bude bayin a isgilance, yadda ruwan ke shiganta yasata lumshe ido tana jin wani dadi na ratsata, jin muryar Raudha da tayi babu zato shi ya sanyata bude kumburarrun idanuwanta, kallon da suke mata ne ya sa cikinta kartawa ta fara rawar baki tana fadin "ina kwananku, "Lafiya kalau karuwar karshen zamani, yadda maganar ta fito babu control ya sanya Nadeeyah jin wani irin bakin cikin da bata taba ji a kalamansu ba, sunsha zaginta da kalamai marasa daďi amma wannan shine zagi mafi muni da taba cin karo dashi daga garesu, maida kwallar idonta tayi

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156