Skip to content

Chapter 148

Chapter 148

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

duk idonsu ya ciko da hawayen tausayi, Raudha da Radiya ma cike da Kuka suka tsuguna a gabansu suka shiga ba Nadeeyah hakuri... Hamdala Raliya tayi a cikin ranta sannan ta sake godewa Allah da yasa dukka yan uwanta da mahaifiyarta suka gane kuskurensu... To kukan ya isa a miko min jikana in bashi abinci, dariya Mummy tayi ta Saki Junior da yake a matse dama, da sauri ya koma gurin Anty Saude ya ďane jikinta haďe da kwanciya ya runtse idonshi.... Sai a hankali zai saba, kunsan yanzu ne ganinku dashi na farko, sai kunyi hakuri da koma meye... yadda Anty Saude ke maganar cikin fitar da tsammanin zamanta tare dashi ya sanya Nadeeyah barin kitchen din da sauri, ta riga ta gama yanke hukuncin zama da Taheer, babu wani dalili na tausayi ko wani abu da zai canza mata ra'ayinta, Halaccin da zatayi wa bayin Allahn nan kenan, ta kare rayuwarta tare dasu..... Gyaran murya Sarki Tidjani yayi yace "Hukumullahu laa Ajabun, hukuncin Allah ba'a mamaki akanshi, abin da ya kawo mu daban sai gashi Allah cikin ikonsa mun haďu da abinda muka shekara da shekaru muna nema..... Kamar dai yadda na faďa maka Alh Mukhtar, Taheer ďana ne, kanina ne ya haifeshi, mahaifinshi Allah yayi masa rasuwa shekarun baya da suka wuce, to yana zaune tare da mahaifiyarshi acan Canada, wannan zuwan da mukayi, alkhairi ne ya kawo mu, a yanzu da na fahimci wacece Nadeeyah sai nakejin kamar yau dinnan a kaddamar da komai a hutar da kowa, domin ita din 'ya ce ga kowanne a cikin mu, duk da na fi kowa karfi akanta a al'adarmu da kuma musuluncinmu, yanzu a gurina nine mutum marar karfi akanta dukkanku nan kun fini karfi, ku kuka san komai nata tun tasowarta, Saboda haka Alhaji Mukhtar nazo gareka ina nemawa ďana *Taheer auren ďiyarka Nadeeyah.... * yana disa aya fadawa suka yi mishi kirari haďe da miko mishi ruwa yasha domin yin magana mai tsayi... Ya ilahi... haskowa masu karatu halin da daukacin yan uwa da masoyan Musaddiq halin da suke ciki.. A kiďime Musaddiq ya mike da zaman da Papy ya tursasa masa yinsa, domin yaso bin bayan su Anty Saude da kuma Nadeeyar da ya tabbatar tana kitchen din... Cikin kaurarrar murya yace "whatt a jo---- da sauri Hilal ya toshe mishi baki haďe da kokarin maidashi ya zauna, iya karfinshi yasa ya hankaďa Hilal ya tafi tagaga zai faďi.. Daddy da a ganinshi yafi Musaddiq din shiga tashin hankali yayi saurin mikewa ya rike Musaddiq dake shirin sake magana, "Da aka fara magana kaji an kira sunanka? Ko irin tarbiyyar da ka samu kenan?, a gaban bakin mu wanda yake kamar Mahaifi ga Nadeeyah kake kokarin nuna musu irin rashin mutuncin da ka koya cikin kankanin lokaci ko?, to bismillah, in ka gama dasu sai ka dawo kaina..... 'Dago idonshi da ya zama kamar gauta yayi ya kalli gefen da Taheer yake, da sauri ya kauda kanshi haďe da fara takawa baya a hankali, cikin rashin sani yayi muguwar buguwa da bangon bayanshi.. Da gudu Hilal ya doso inda yake, kafin Hilal ya karaso ya juya ya haye sama da gudun da taku uku kaďai yayi ya isa ďakin da yake... Dafe kai Papy yayi cike da tausayi ya kalli Daddy da ya koma ya zauna yana magana cikin karfin hali.. "Mashaa Allah ranka ya daďe, na baku Nadeeyah, Allah ya sanya albarka a cikin auren, karku damu da sakarcin Musaddiq, yarinta ke damunshi.. Cike da jindadi Sarki yace "To madallah, sai a yanke mana sadaki domin muna da nisa, munfi son ayi komai cikin lokaci... Wannan karan duk wani kuzari na Daddy ya kare da kyar ya iya cewa "Da kai da kaya duk mallakan wuya ne, ranka ya daďe duk hukuncin da ka zartar daidai ne... Kuka sosai Anty Raliya ta fashe dashi na tausayin dan uwanta da kuma halin da taga mahaifinta, daki ta wuce da gudu Husna ta rufa mata baya itama kukan takeyi... Innalillahi wa inna ilaihir rajiun... shi kaďai take maimaitawa tana faďin duk laifi na ne, a tunanina in Nadeeyah ta dawo zata komawa Little, ashe wata kaddarar Allah ya shirya mana daban, Cikin kuka take bawa Husnah labarin komai da tayi wanda yake neman jefa dan uwanta cikin barazanar rayuwa.... Wani irin wawan mari Anty Reemah da ta biyo bayansu taji komai ta wanka mata.. cikin masifa ta fara zaginta tana kiranta da marar imani, tasan inda Nadeeyah take tabar kowa cikin zullumi musamman Mahaifiyarta dake fuskantar rayuwar ukuba saboda hakan, ta inda take shiga bata nan take fita ba.. Durkusawa Anty Raliya tayi cikin kuka ta bata hakuri da kuma amsar laifinta, ita tayi shi ne in a good faith dan Nadeeyah ta samu ingantacciyar rayuwa, ashee inganta rayuwarta zaiyi sanadiyyar shigar rayuwar Musaddiq cikin wani rudanin..... ta karashe cikin matsanancin kuka..... Zama sukayi su ukun suna cikin jimami suna zubarwa da dan uwansu hawaye... Minti goma kaďai su Sarki suka kara sukayi shirin tafiya, Kallon Hafeez Shareefah tayi tace anjima suzo shi da iyalanshi su sameta.. cikin ladabi ya amsa mata da "To, Adress ta karba gurin Taheer ta bashi cike da farin ciki..... Katse wayar dake shigowa cikin wayar Baffa yayi karo na biyar ya tashi ya tafi yin rakiyar su Sarki shima jikinshi ba kwari, kawai dai basu da bakin bijire musu ne dan suna da dukkan iko akan Nadeeyah, ga kuma taimaka mata da sukayi, ya zama dole suma su rama musu halaccin da sukayi mata... Kallonshi tayi cike da tausayi bayan ya gama nacin Junior yazo gurinshi yaki, A hankali tace "Bari mu tafi *KYARI* in shaa Allah gobe da safe zan kawo maka shi, baka bani phn numbernka ba, kai dai har yanzu kana nan da miskilancinka akan mace, to ni na tambaya a bani, Dariya yayi wacce da gani yake ce, ya fara faďa mata number, Shafa kan junior yayi yace "Takwarana sai gobe ko, ka zo da kaya da yawa dan rikeka zanyi.... Saida suka ga fitar motocin sannan suka koma ciki dukkansu babu mai karfin yiwa dan uwanshi magana... *DADDY* sunan da ya bayyana a jikin wayar haďe da special ringing tone, Dauka Husnah tayi ta nufi kitchen da wayar, can baya ta hangota zaune tana wasa da yatsun kafarta, dafata tayi haďe da zama a gefenta, Idonta da sukayi luhu luhu ta dago ta kalli Husnah haďe da kakaro dariya, zatayi magana kenan wayar ta sake kara, Ajiye mata wayar Husnah tayi akan cinyarta ta kauda kanta can gefe, ganin sunan ya tabbatar mata da junior ne da aikin nan dan tare suka siyo sim din Nigeria dashi,, Saida ta kusa katsewa ta dauka,, "Mamma.. ya faďi kamar karamin yaro.. "Uhmmm Uncle,, tafiya babu sallama ko? Kwantar da kanshi yayi a jikin kujerar yace "Na daga miki kafa ne, nasan yau baki da lokacin mu ni da junior, kinga yan uwa bayan dogon lokaci, just call to tell yhu "I love yhu alot.. Runtse idonta tayi tace "Uhum, "Uhummm, say it plss, ya faďi cikin kaguwa, "Same to yhu.. Dariya yayi yace "Muna nan zuwa anjima bayan isha'i, take care plss... "Ohk uncle, in shaa Allah bye.. tana kaiwa nan ta katse wayar... "Husnah kun dawo

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156