Chapter 16
Chapter 16
ya mutu to fa bazai dawo ba, kuma taga yadda akayi wa babanta haka akama mamanta, domin kafin a fitar da gawarshi saida aka kaita kanshi, wani irin kuka ta saki hade dayin wurgi da sweets din da Hafeez ya sai mata bata sha su a makaranta ba, Mamma ki tashi, dan Allah ki tashi, wallahi bazamu sake barinki kiyi kuka ba, ga yaya Hafeez ma zance kar ya sake tafiya ya barmu, dan Allah ki tashi, hannun wacce tayi mata wanka ta kamo tace "dan Allah ki tasheta, kice tayi hakuri karta tafi yanda Baba ya tafi, wallahi muna santa ni da Anty Nadeeyah, kowa baya santa, tasani mu kadai ne muke santa, rungumeta Husnah tayi hawaye na bin idanuwanta, ta dauketa ta fitar da ita a dakin dakyar,, babu wanda bai zubda hawaye a gidan ba.. Bayan an gama shiryata kowa yayi mata addu'ar samun dacewa da rahama.. Baffa na zaune a kofar gida, idon nan nashi kamar gauta, jikinshi babu inda baya rawa, dakyar aka dagashi ya shiga dan yiwa diyarshi addu'a, ki yafe min suwaiba, ki yafe min, ubangiji Allah yayi ma abin da kika bari albarka, na cutar dake matuka, tun kuruciyarki har kawo yau, kuka sosai yakeyi kamar karamin yaro, tabbas mutuwa tayi mishi gaggawa, ina hankalinshi yake lokacin da yake azabtar da marainiyar Allah, babu abin da yasani nata tun tasowarta, bashi da masaniyar damuwarta, duk rashi irin nata bata taba gajiyawa gurin kyautata musu shi da matarshi ba, wani irin kunci yakeji a cikin ranshi da ya tuno bai taba barinta ta samu abinda take so ba, kallon gefenshi yayi ya hango Daddy tsaye shima hawayen ne ke zubar mishi babu kakkautawa, dukkansu biyun abubuwa masu zafi suke tunowa da faruwarsu shekaru da dama da suka shude, share hawaye Daddy yayi ya fita daga dakin zuciyarshi a karye... ************ ****Kalli sararin samaniya ki fada min abun da kika gani, sauke idonta tayi bayan ta kalla, tace "Naga abubuwa da yawa, wasu taurari masu kayatar da duhun daren samaniya, saidai Mamma, ga wani tauraro can, yafi kowanne haske, ga kuma wasu masu haskawa biyu a kewaye dashi, sannan ga wasu can sun disashe su biyu ba'a ko iya hangosu, murmushi Mamma tayi ta dafa Nadeeyah tace "Tauraron da yafi ko wanne haske 'Kece Nadeeyah', sannan biyun dake kewaye dake bani da masaniyarsu, amma tabbas alkhairai ne masu karfi da yalwa a kewaye dake, sannan sai biyun da suka disashe----- sai tayi shuru tana kara kallon sama, tace "bar batun biyun nan Nadeeyah Allah kadai ya barwa kanshi sani, saidai a gefen tauraronki baki hangen wani wanda yake turo kai karfi da yaji yana san doke hasken naki, da sauri Nadeeyah ta kalli sama, a firgice ta maida kanta kasa tace "waiii Mamma wannan hasken mai cutarwa ne, bazan iya jurar kallanshi ba.. Jajircewa zakiyi Nadeeyah, daurewa zakiyi ki fuskance shi domin bashi kadai bane, hango wani yana fasowa a dayan gefen, duk sun kewaye taurarin dake kewaye dake da haskensu, waigawa tayi cike da zumudi da murnar jin maganar mahaifinta, Baba dama baka mutu ba? kaga yadda kayi kyau kuwa, hannuwanta ya kama yace "Tafiya ce ta kamani ta gaggawa, kinga mahaifiyarki bata iya jure zaman, ta biyoni, saidai dawowar mu ba mai yiwuwa bace, domin tafiyar ta din din ce, lokacin da zakiyi wannan tafiyar baiyi ba, yanzu lokaci ne na hakuri da jajircewa, in kina son nasara sai kin jure, in kina san zuciyarki tayi haske sai kinyi hakuri, "Amma fa ba hakurin da zai cutar dake ba, cewar mamma tana murmushi tana shigewa jikin mijinta, akwai hakuri me cutarwa ne Suwaiba, murmushi tayi tace "akwai mana, hakurin da kana ji kana gani a taka ka a wuce, wannan hakurin ka iya fasa zuciya, manzon Allah s.a.w yace "in bazaka iya hakurin abun da akayi maka ba ka rama daidai yadda akayi maka,, "kwarai haka yake, Baba ya fadi sannan ya cigaba cewa "ke din me nasara ce, zaki daukaka fiye da tunanin mai tunani, saidai kinsan dukkan ma'abocin daukaka yana tare da kalubale, amma ki sani kuma kisa a ranki, a ko yaushe Allah swt yana tare dake, karki yada Addu'a domin ita din garkuwa ce ga mu'imini... lokacin tafiyarmu yayi, ki kula da dukkan rayuwarki da ta yar uwarki, sannan kiyi hakuri da dan uwanki, domin shi din mai rauni ne, Nadeeyah tayi saurin cewa "zan biku Mamma, murmushi mai sanyin kyau sukayi mata, suka hade baki cikin murya me kamar amsa kuwwa, sukace "wannan tafiyar ta musamman ce, lokacin yinta a gareki baiyi ba Nadeeyah, Tafiya suka fara yi Nadeeyah na binsu tana kuka tana fadin karku tafi ku barni, tun tana hangensu har haske ya kara kewaye gurin, tsayawa tayi hade da runtse ido tana kiran sunayensu hade da shashshekar kuka... Hannun da taji kan kuncinta mai sanyin kamshi ne ya soma farkar da ita, a hankali ta bude idonta ta saukesu kan Hinad da itama kukan takeyi.. "Sorry Nadeeyah, kiyita karanta innalillahi wa inna ilaihir rajiun, i know it hurts but bamu da yadda zamuyi, addu'a itace tafi dacewa dasu a wannan lokacin, Allahn da ya halicce su ya fimu sansu.. kawar da kai Nadeeyah tayi tana tunano hirarsu ta cikin mafarkinta, "kunyi tafiya mai nisa Mamma, tafiya mai dadi a gareku in shaa Allah, sannan mai radadi a garemu, hawayen idonta bai bar ambaliya ba ta cigaba da maganar zucin da takeyi, yanzu yaya rayuwarmu zata kasance, shikenan bamu da wani sauran gata... "Gatan kowa Allah ne Kanwata, babu wani gata mai daraja, dadi, da dadadawa irin na ubangiji, in Allah ya baiwa bawa gata, to babu wanda ya isa ya tauye ko ya kwace mishi, mika lamarinki gurin ubangiji, kuma kiyi tawakkali kisan shi ne kadai maiyi... saida ya kai aya Nadeeyah ta dago ta kalli gefen da yake, tabbas zancen da takeyi a zuci ne ya fito har ya iske kunnuwanshi, shi din ma tsaye yake idon nan nashi yayi jawur kamar gauta, wani hawayen ya share sannan ya karaso jikin gadon da take, zama yayi gefenta yace "ya jikin naki, runtse ido tayi ta amsa da sauki, Allah ya baki lafiya da hakuri hade da juriya, "Ameen yaya Musaddiq, Hinad fadi tana share mata sauran hawayen dake gefen kunnenta.. Ina Zainab take yaya Musaddiq? Kafin Musaddiq yayi magana sukaji an murda kofar, Hafeezu ne ya fara shigowa sai su Anty Reemah, Hilal ne karshen shigowa shi da zainab, hannunta rike da ledojin kayan kwalama, fuskar nan tata tayi jawur, tana ganin Nadeeyah ta saki ledar ta karasa ta fada jikinta tana kuka, mikewa Nadeeyah tayi a hankali sannan ta janye daga kusa da musaddiq, ta dago kan zainab tace "menene, me aka miki? Anti Nadeeyah mamma ma ta mutu, ta tafi gurin baba, sun dauketa sun fita da ita, shikenan bazamu sake ganinta ba, dariya Nadeeyah tayi tace "inji wa yace miki, mamma bata mutu ba, kinsan tace miki zata je Agadaz rannan ko? Eh zainab tace tana me kallon Nadeeyah, to can ta tafi, kina gani sun shiryata ta hau jirgi tana jin dadinta ke kuma kina nan kina kuka, oya share hawayenki ki ji abin da mamma tace in fada miki dazu kafin ta tafi, da sauri ta share hawayenta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156