Chapter 27
Chapter 27
mana zuwa yanayi na ban mamaki da tsoro, abin ya faro ne saboda ganin da ummulkhair tayi Abbuna ya dauki dukkan kulawarshi ya bamu ni da kanina *ATEEK* kiyayya iri iri babu wacce Ummul bata nuna ma Ateek, kiyayyarta a garemu batayi karfi sosai ba har saida ta haihu, a lokacin ne ta nuna wa Ateek karara ba ita ta haifeshi ba, in na tafi makaranta na barshi kafin in dawo gida ya jigata da yunwa, gaba daya Ummul ta shafe idonta ta manta da zumunci saboda kasa ta rufe idon ummuna wacce ta zamto yar uwarta ta jini, burinta a kullum Abbuna ya kula da ita da yaranta guda uku " Haidar, Affan, da Farouk," saboda rashin zaman Abbunmu shiyasa bai taba sanin halin da muke ciki ba, bai kuma kula ya duba ba, saboda a ganin shi kamar da ummunmu muke tare, bai taba kawo ummul zata taba koda yi mana kallon banza ba, bare har ta kai ga cuzguna mana, Kakarmu ita kadai ce gatanmu, gurinta hankalinmu ke kwanciya, wannan zuwan da mukayi ma ta'aziyar rasuwarta muka zo, daga can muka taho nan mambila inda kanwar kakanmu (wanda ya haifi ummunmu) take domin gaisheta.. gidan sam baya min dadi saboda duk yan uwa basa kulawa da lamarin mu saboda rashin idon uwa, kuma suna ganin Ummul ce mai rike damu sannan ga kudi tana musu facaka dashi shiyasa duk suka dauke idonsu akan mu, rashin jin dadin zaman gidan yasa da na ga Habeeb ya fito zai taho siyan madara na biyoshi dan in zaga inga gari hankalina ya kwanta, ashe kaddararmu ce anan ni da shi, tunanina daya *Ateek* da na tafi na barshi yana bacci, yaya rayuwarshi zata kasance in har babu wanda ya biyo sahun duba ni, yaya rayuwar Ateek zata kasance, ta karashe cikin kuka mai ratsa zuciya,,,,, Share hawayen tausayi Hardejo yayi yace "zasu zo su sameki, nasan zasu zo dan na tura a nemo inda iyayen yaron suke, ko basu zo ba ni zan je har mambilan in kaiki gobe, cikin kuka tace jirgin su a daren yau zai tashi ya koma cairo, kuma kasani ba'a samun jirgi akai akai, Kwantar mata da hankali Hardejo yayi yace "Gobe tun da asuba zan tafi in kaiki, ki kwantar da hankalinki, " "Abin da Hardejo bai sani ba shine labarin mutuwar Habeeb ya karade ko ina a tsaunin mambila, kuma an hade harda ita Atikar ance an kasheta, saboda firgicin labarin kuma ance musu limamin garin yasa an dauke gawar an suturce yasa gaba daya yan uwanta suka shirya komawa Cameroon a daren, harda ita kanwar kakar tasu wacce dama Habeeb din ne karfinta a garin.... Suna idar da sallar asuba sukayi janaizar gawar Habeebu, bayan an binneshi kamar yadda Hardejo ya karanta sukayi mishi adduoi sosai sannan kowa ya wuce gidanshi, ko abincin safe bai ci ba ya shirya ya tarar da Atika tana shan fura, tana gamawa ta mike suka dauki hanyar tafiya tun kafin garin ya gama yin haske, sai da sukayi tafiyar awa daya sannan suka samu motar awaki ta karasa dasu, A garkame suka samu gidan da ya kasance daki biyu tall, cike da tashin hankali malam Hardejo yabi makotan gurin yana tambayarsu, sukace ai kuwa tun daren jiya suka tafi saboda firgicin mutuwar su Habeebu, zamani na babu waya bare ace za'ayi kiransu su dawo, Takalmin Ateek ta gani a kofar gidan kafa daya, dauko takalmin tayi ta zauna dabas taci kuka ma ishi hade da rungumar takalmin tana sumbata, "Allah yasa ina da rabon sake ganinka Ateek, ya Allah ya hadamu da kai da alkhairi,, Hardejo saboda tausayi baiyi yunkurin hanata ba, saida tayi kukanta sosai sannan ta tashi suka koma can kauyen su Hardejo,, kauyen da rayuwa tayi dadi hade da wuya ga Atika, kauyen da ya maida yar gata baiwa, kauyen da Atika tayi rayuwa mai cike da ban tausayi.... Ya Allah kai ka zama gatan mara gata, Allah ka sanyani na zama uba kuma gatan Atika dan alfarmar annabi da hasken alkurani... addu'ar da Hardejo yayi tayi kenan har suka isa gida...... Mrs Tijjani shattima.... [01/03 12:08 AM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU*•• 2⃣4⃣ By *Aysha Ya'u Kurah* Satin Atika hudu ta fara sakin jiki da yaran gidan duk da bata gane yarensu, karatun qurani da littattafai take yawan koyar da yan matan da yan yaran gidan, sai addu'oi na azkar wadanda ta koya daga gurin mahaifinta... Shaho kuwa tunda ya fahimci tana gidan Malam Hardejo hankalinshi ya tashi, duk iskancin shaho yana tsoron Malamin saboda kwarjinin da yawaitar ambaton Allah ya haifar masa, kullum in yayi niyyar zuwa gidan sai yaga gidan ya zame mishi bakikkirin,, gashi kullum bashi da nutsuwa saboda yawan mafarkin Habeeb da yakeyi, bacci sam ya daina daukarshi dan daga ya rufe ido zaiga fatalwar Habeeb.. kwance yake yayi firgai firgai zuciyarshi cike da kunci da radadi wanda baisan daga inda suke ba, hatta da abinci ya daina samun lokacin ci saboda yanayin rayuwar da ya tsinci kanshi,, rashin ilimin addini ya sa ya kasa gane jinin mu'muni da kuma adduar malami irin na zamanin da wanda baya iya yin komai na sabon Allah ne ke dawainiya dashi ba, iyayenshi sun kasance masu kudin kauyen sosai, shiyasa yake yin abin da yaga dama, ganin halin da ya shiga ba karamin daga hankalin mahaifiyarshi yayi ba, duk irin sangartar da yakeyi ita sam bata ganin laifinshi, ko da aka kawo mata labarin abinda yayi murna tayi tace "sai ku jerasu cikin sauran mutanen da ya kashe, ai ba yau ya fara ba, ita a kullum alfahari takeyi da halayyarshi saboda jahilci.... Halin da taga danta a ciki ne ya sanya ta dangata halin da son bakuwar gidan Hardejo, alkawari ta mishi na a cikin satin nan zata aura mishi ita koda kuwa duk abin da take dashi zasu kare..... ******-------******** Jin inuwar mutum a kansu ne ya sanya su dagowa daga duba littafin dake hannunsu, Maryam yar Hardejo ta mike tsaye jiki na rawa tace "ina yini, bata amsata ba tace "kira min Mai babban suna, da sauri ta shiga daki ta kira mahaifiyarta, kafin su fito maman shaho ta karewa Atika kallo sosai, a zuciyarta taji dadi da danta zai samu wannan zukekiyar yarinyar a matsayin mata.., "Gambo kece tafe, Aisha ta fadi tana shimfida tabarmar kara, ba zama nazo yi ba mai babban suna, nazo ne in fada miki Shaho yana son bakuwar gidanku, in Hardejo ya dawo kice mishi yazo ya sami Barde (mahaifin shaho) sai su shirya ayi musu aure yadda addinin Hardejo ya tsara, "galala Aisha tayi a zuciyarta tace "yau isar har ta kawo kansu, kafin tayi magana Baffa ya shigo gidan tare da ma'u, duk abin da ta fadi akan kunnensu, "ko bakiji abin da nace bane mai babban suna? Gambo ta tambaya tana huro hanci, karap Ma'u tayi tace "yo ko taji amsar me zata baki, yanzu ke d'anki har wani d'a ne da zakizo kina hurawa mutane hanci kina nuna iko akan yar mutane, to walle duk wani iskancinku yazo kurewa, dan ko sama da kasa zasu hade yarinyar nan bazata auri azzalumi irin shaho ba, ba Aisha da matan gidan dake tsaye a tsorace ba, har Baffa da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156