Chapter 90
Chapter 90
kar in yanke, "in ka yanke zaka hakura ai ta fadi itama tana dariyar, "har so kikeyi in yanke ko? "Kai ka fada nidai bance ba! "Kin ce mana, ya fadi a shagwabe kamar karamin yaro, dariya tayi hade da tattara dankalin ta juya mishi baya ta cigaba da aikinta, "An fada miki sakona?? Wani irin faduwar Gaba taji da ya jefo mata tambayar, bata samu bakin amsashi ba ta cigaba da aikinta hannunta na rawa, Gabanta ya dawo yasa hannu ya dago fuskarta, da sauri ta runtse idonta tace "wani sako? In abinci ne kasan yanzu zan gama, "uhm ga acici ko? To wannan sakon yafi cikina muhimmaci, Hilal bai fada miki komai ba? Ya karashe tambayar cike da kasalar da soyayyarta ta sakar mishi, turo baki tayi hade da ture hannunshi tace "ni bai fada min komai ba, hannu yasa a aljihu ya dauko waya ya fara latsata, da sauri ta daura hannunta kan wayar tace "Dan Allah yaya Musaddiq ka bar wannan maganar, yin soyayya ni da kai ba abu bane mai yiwuwa, "dalili?? Ya tambaya fuskarshi ta nuna alamun damuwa, rasa abun ce mishi tayi kawai tace "saboda inada wanda nake so, zoben dake makale a hannunta ta nuna mishi tace wannan zoben alkawari ne, kuma kasan babu kyau karya alkawari, Hannunta ya rike a hankali yana shafa zoben zuciyarshi kamar zata soye saboda azabar radadin da take yi, iya karfinshi yasa ya fincike zoben a hannunta, tana kallonshi ya sa hakori ya karyashi yayi wurgi dashi ta window, kallonta yayi da wani irin yanayin da bata taba gani a tare dashi ba yace "koma waye saidai yayi hakuri dan ba samunki zaiyi ba, ke tawa ce ni kadai, kin gane ko? Kasa tayi da kanta hawaye ya fara zubo mata tace "kayi hakuri, ina sonshi sos---- *Nadeeeyah....* ya fadi da karfi rai a bace kamar namijin gaske, sautin kukanta da yaji ne ya sa jikinshi mutuwa, hannu na rawa ya dago fuskarta ya fara share mata hawayen, "kiyi hakuri ki daina kuka, bazan iya jin bakinki ya furta san wani bayan ni ba, bazan jure ba, rage murya yayi yace "dan Allah ki soni ni kadai, kamar dada ingizo kukanta yayi saboda bata son ya matsa su shiga cikin matsala tare, ganin yayi mata tsawo sosai ya sanyashi rage tsawonshi daidai fuskarta, "Nadeeyah---- "dan Allah kayi hakuri ta katseshi cikin kuka, "wai dame zan hakura ne? ya za'ayi in hakura da abun da nake so, kin san bazai yiwuwu ba, ya karashe yana daura hannunshi a saman idonta, "ki daina min kuka, bana so, in ba so kikeyi inyi ba nima, kiyi hakuri kinji? ki manta dashi ga dan uwanki, kinsan nafi sonki, kuma kema kina sona, zaki fi kula dani, abinci na, komai na, "Ni bana sanka ta fadi tana goge fuska da hannunta, saboda shaukin so dake dibarshi baisan sanda ya hada jikinshi da nata ba ya kankameta hade cewa "zaki soni sosai, Fiye ma da kanki Ma... Fiye da komai a duniya... lumshe idanuwanshi yayi ya cigaba da fadin *I love yhu Nadeeyah, more than life it self......* Innalillahi wa inna ilaihir rajiun..... maimata Kalmar Mummy tayi sau uku tana tafa hannun cike da mamaki da takaici....... Mrs Tijjani Shattimah...... [05/04 10:42 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 5⃣4⃣ By *Aysha Ya'u kurah* Na shiga uku ni Zainab! yau me zan gani a cikin gidana, Da sauri Musaddiq ya mike har takalminshi daya na fita a kafarshi yace "me kika gani Mummy? "Ubanka na gani ta fadi a harzuke, abin da kukeyi kenan Musaddiq? yau ni na shiga uku na lalace, Oooh wato shiyasa kullum kike hanyar dakinshi da nufin tashinshi a bacci, ashe zuwa kikeyi ki koya mishi yadda mace da namiji suke jiyewa kansu dadi, yanzu Nadeeyah har kinyi girman da zaki koyawa namiji yadda zai dinga yi miki kiji dadi, *DANKARI!* lallai wannan abun babba ne, "Wai Mummy me ya faru ne? babu abin da mukayi fa, kawai ina taya---- zan ci maka mutunci in ka sake yi min magana, wallahi kana cewa takk zan kwada maka mari, sakarai wanda bai san inda yake mishi ciwo ba, maza ka biyoni.... kallon Nadeeyah dake tsaye tana share hawaye tayi tace "To munafuka maza ki wuce daki ki jirayi hukuncin da zan miki, yar iska mara mutunci, Rai a bace Musaddiq yace "ki daina zaginta Mummy, me tayi miki da zafi har haka kike kiranta da munanan kalamai, haba.... "Bance karka sake samin baki ba, zo ka fita ka wuce sama gani nan zuwa, Saida ya bari Nadeeyah ta fita sannan shima ya fita ya haye sama yana kunkuni dan shi samm baiga abin da sukayi ba..... "Ashe yarannan Iskancinsu sukeyi, wallahi da wani ne yazo ya bani labarin cewa yaga Musaddiq da mace a yadda na gansu wallahi bazan yarda ba, dan rashin kunya a cikin gida, ita kuma dan ta gama zama yar iska harda kankame wuyanshi.... *Zainab....* Daddy ya daka mata tsawa da karfi dan yaga tana neman wuce gona da iri, shuru tayi tana hucin bacin ran kalaman da ta jiyo danta da ta gama shirin kece raini dashi yana fadawa Nadeeyah, Nadeeyar Adamu mai gadi! da sauri ta runtse idonta dan wallahi tuno abun ma mugun taba zuciyarta yakeyi, kallon Musaddiq Daddy yayi fuska babu alamun wasa yace "ka fada min gaskiya, menene tsakaninka da Nadeeyah? Nasan ko kai zaka iya rungumar mace Nadeeyah bazata taba kusantar namiji ba saboda i have full faith in Suwaiba's upbringing, Shin me mahaifiyarka ta gani wanda ya sanyata yin wannan tunanin, kamar jira yakeyi mahaifinshi ya kai aya yace "Daddy dan Allah ka aura min Nadeeyah, wallahi ina santa sosai, "Bakin cikin kiran Sunan Suwaiba da Daddy yayi da kuma na kalaman Musaddiq su suka hadu suka dugunzuma zuciyar Mummy ta sakar mishi wata irin kazamtaciyar ashariya, kallo daya Daddy yayi mata tayi saurin dauke kai idanuwanta sunyi jaa saboda bacin rai, Maida hankalinshi gurin danshi yayi Zuciyarshi fess saboda dama abin da yake ma danshi addu'a kenan, "ka nemi soyayyarta? Daddy ya tambayeshi cikin sakin fuska, "Eh Daddy, ita ma tana sona, "Karya kakeyi wallahi, inaji tana cewa bata sanka, Yadda Mummy tayi maganar ya sanya Daddy dauke kai dan dariya ta kusa kufce mishi, jiya bata barshi ya runtsa ba saboda labarin Faida yar gidan *Hon Danjuma Diriss*, ta matukar cin burin bikin, shi kuwa a gurinshi sam bayasan danshi yayi auren *MATAUL HAYAT*, irin su Nadeeya ya dade yana fata, sai gashi Allah ya kawo mishi cikin sauki, waya ya daga ya kira number Husnah yace suzo tare da Nadeeyah, Mummy najin haka ta dauko wayarta ta tura text din gargadi zuwa ga Nadeeyah, A lokacin da ta tura text din a lokacin Nadeeyah da Husnah sun kusa taka step din karshe..... Cikin hikima Daddy yayi musu Nasiha ya nuna musu muhimmancin aure at early age, sannan ya kalli Nadeeyah yace "Nadeeyah kina da wanda kike so? Aure zan muku ke da Husnah... A kunyace taja hijab dinta ta kasa hada ido dashi, ya za'ayi ta iya furta bata san danshi na cikinshi, Daddy, Hilal, Anty Reemah, Musaddiq, Anty Raly, uwa uba Husnah da bata banbanta kanta da ita, duk a cikin zuriar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156