Chapter 68
Chapter 68
kallo sosai, saida tayi mishi guga na musamman sannan ta ajiye, tana gama gyaran office din ta sake daukar hoton tana kallo, Hakanan taji mutumin cikin hoton ya shiga ranta, Sanye yake cikin babbar riga da hula, yayi kyau sosai, Tana kokarin ajiye hoton taji yace "my late Father " *Alhaji Haroun Yallo*, Ajiye hoton tayi da sauri tace sorry Sir, na gama yanzu zan wuce class, Bashi da niyyar matsa mata a makaranta sam, dan a yadda ya tsara a makaranta nuna mata rashin sani zaiyi kururu. amma ya zaiyi, soyayyarta ta hanashi katabus, Takowa yayi ya karaso inda take tsaye ya dauko hoton, "Wannan shine Mahaifina, rayuwar da mukayi dashi ba mai goguwa bace, kullum in ban tunashi a duk numfashin da nakeyi ba to tabbas zan tunashi a duk takun da zanyi a rayuwata, He is my best friend, Mutuwarshi ita ta kashe wasu sassa na farin cikin dake cikin zuciyata, mutuwa ce wacce yayi ta ba zato babu tsammani, Ajiye hoton yayi yace "Mutuwa wata abace wacce zafinta yafi dukkan zafin wutar dake cikin duniyar nan, zafin wuta na warkewa ya barka da tabo, amma mikin rashin makusanci kullum sabo yake zama, Mahaifina ya nuna min kauna har ranar da zaiyi tafiyar din din din, "A ranar da zai mutu ranar na dawo daga Canada, saboda kar ya daga hankalinmu shiyasa ya boye mana ciwonshi, ya dinga biye ma duk wata rigima tawa, Tare muka je aski, cikin rashin sanin yana ciwo nasa akayi mishi askin dukka kanshi dan ya zame min abin tsokana, haka nan badan yana so ba ya yarda akayi mishi, Daga gurin askim muka wuce yawo muna ta zaga gari muna ziyarar gidajen Abokanshi, Masallacin cikin gidan mu nan ne guri na karshe da muka tsaya, A daddafe ya idar da sallar magriba, jin irin numfashin da yake fitarwa ya sani tambayarshi ko baida lafiya ne, dariya ya kakaro hade da naushin cikina kamar yadda muka saba yace "in yana da ni ta ina ciwo zai samu muhalli a jikinshi, Nan take Muryar Taheer ta raunana, hawayen da suka cika idanuwanshi suka dinga tsere a tsakaninsu, ya cigaba da cewa "A sujjar karshe ta sallar isha'i karfin Abbana ya soma karewa, Gaba daya masallacin yayi shuru saboda jam'i da ake bi, numfarfashin Abbana kadai ake ji a ciki da wajen masallacin, gaggauta yin sallama liman yayi, kowa yayi kanshi saboda ganin har lokacin bai dago daga sujudi ba, kuma bai bar fitar da numfarfashi ba, Ko da aka dago shi ya gama fita cikin hayyacinshi, A lokacin wanda ya taba dandanar mutuwa zai fahimci inda Abbana ya dosa, Dagoshi nayi da karfi ina fadin ya tashi muje asibiti, Girgiza kai ya shiga yi yana fadamin "ka barni anan Taheer, ka barni anan, asibiti, ko gida, a yau basu da amfani a gareni, Murmushi yakeyi mai dauke da kuka yana fadin Taheer kayi hakuri, kayi hakuri abokina, na boye maka ciwo na saboda nasan ba na tashi bane, Naso sai ka koma makaranta zanyi tafiyar nan amma inaa lokacina yayi, ban isa kara kwana daya ba koda kuwa ina son kara shi, "Kukan da Taheer yakeyi a lokacin mai sautine dan bai taba fitar da wannan labarin da yayi mishi karan tsaye cikin rayuwarsa ba sai yau da a karo na biyu yake shirin rasa wacce yake tunanin dawowar farin ciki cikin rayuwarshi, Ita din ma Nadeeyah kukan takeyi na tausaya mishi da tausayawa kanta, domin ita ma tayi rashin dukka iyayenta, "Ban taba kawo mishi mutuwa ba saboda ban yarda zai tafi ya barni a wannan lokacin ba, kin saurararshi nayi muka daukeshi dan kaishi asibiti, ina tuno sanda ya shafa fuskata muna gab da fita daga masallacin yace "Taheer kaki yarda ko? Dole ka yard---a d------a wann---- nan ya fara kakari har yafi karfin wadanda suka rikeshi, ka-- kula da--- kanka da-- da-- mahaifiyarka, damke hannuna yayi har lokacin idonshi bai gama rufewa yana tayi min murmushin da ya saba, "A wannan ranar ne na ga abun da ake kira damuwa karara, a wannan bakar ranar naga kaddarar rabuwa da abin da kakeso, a wannan daren mahaifina ya mutu tare da duk wani kuzari nawa.. Tun daga ranar na manta farin ciki da yadda akeyinshi, babu abin da ke burgeni a duniyar nan bare har yasani farin ciki, Rabuwa da Abbana.... ya ilahi!! nan da nan Nadeeyah ta rikice saboda yadda yake kuka kamar ana zare ranshi, kuka sosai yakeyi wanda bai samu damar yinshi ba ranar da ya rasa mahaifinshi, Abubuwan da suka cunkushe mishi ya fitar yau yake kokawa a kansu, shakuwar da yayi da mahaifinshi ta wuce ta ďa da uba, ta zamo shakuwar jini da hanta, a ko da yaushe ya rufe idonshi murmushinshi kadai yake gani, bai taba karo da bacin ranshi ba sai dai farin cikin shi, Gabanshi ta tsuguna itama kukan yaci karfinta tace "Uncle kayi hakuri, sau tari abubuwan da muke so basu cika kasancewa tare damu ba, jarabawar mu kenan, gara kai kana da wacce in ka juya zakaji dadi, ni fa babu uwa babu uba, babu yan uwan uba da zan kirasu nawa saidai na uwa, ka godewa Allah domin not all are fortunate, Duk abinda kaga Allah ya dauke maka to yana da dalilin yin hakan, ta yiwu in ya bar mana su wata rana saboda azabar ciwo mu gwammaci tafiyarsu akan tsayuwarsu cikin ciwon da mu kanmu bamu isa mu magance musu ba, nasan yadda kakeji domin nima ina jinshi ko ma ince fiye da naka, Dan Allah a duk lokacin da ka tunashi ka dinga fadin *innalillahi wa inna ilaihir rajiun* sannan kayi mishi addu'a domin yafi bukatarta a yanzu.... Wata irin nutsuwa ce ta saukar mishi wanda tun kafin rasuwar Abbanshi rabon da ya shiga irin ta, share hawayen idonshi yayi ya dago ya kalleta, Sai a lokacin yake tambayar kanshi dalilin dayasa har ya fada mata damuwar da ya dade yana dakonta, Tabbas zuciyarshi ta gamsu ita ce wacce zai samu nutsuwa da ita, kalamanta sunyi matukar sanyaya mishi zuciya, jin zuciyarshi yake wasai kamar an sauke mishi duk wani nauyin da zuciyarshi ke dauke da shi, Tsugunawa yayi kamar yadda tayi yace "is ok, kukan ya isa haka, ni nasa ki kuka, ni kuma na daina ke kin ki dainawa, sorry kinji, tashi ki zauna... Mikewa tayi tace "zan tafi class ne, kujera ya ja mata yace "kice wa ya saki kuka? Ajiyar zuciya tayi mai karfi sannan ta zauna, Ji yakeyi kamar ya rungumeta ya hanata wannan kukan da yasan irin ciwonshi, "nace ya isa ko nima so kikeyi in cigaba, kinsan in na fara nawa biyu zan hada, da na rashin mahaifi da kuma rashin farin cikin rayuwata, ya karashe fadi a raunane cikin damuwa, Share hawayenta tayi kamar me shagwaba tace "na daina, "Kina sona Umm Nadeeyah? Yadda ya jefo mata tambayar ta sanyata saurin dauke kanta daga kallonshi, "ummm bani amsa plss, nd "who is Musaddiq? Ya karashe yana janyo kujera... "Yaya Musaddiq? Ta fadi tana kallonshi, gyada kai yayi yace "yes waye shi, meye alakarku? "Babu komai, he is my cousin, "nd husband to be, Taheer ya karashe yana kallon cikin idonta, A razane tace "whatt, ba gaskiya bane, kaga
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156