Skip to content

Chapter 39

Chapter 39

Zumuncinmu A Yau Book One Complete Hausa Novels 1 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

ta ke dashi ya disashe, rayuwar dai yinta kawai takeyi saboda Allah a hakan yaso ya ganta, kullum saidai tayita yi mishi Godiya da bai daura mata ciwo ba.... Leemah kuwa ta zama yar gayu sosai, university take zuwa Abu zaria, babu abinda zatace tana dauka a makaranta, ita dai kawai ta shiga gayu, yau ta tsaya da wannan gobe wancen, Baffa daga yayi niyyar yi mata magana Ma'u zata hanashi, takan ce in ba'a barta taje makaranta ba ina zata samu mijin aure, dole badan yaso ba ya barta tayi abin da taga dama.. "Bani omo malam Ado, ! dauko mata kullin bulan omo biyar yayi yace "jeki kiyi amfani dashi, na bar miki kudin ki siya silifas naga naki ya tsinke, murmushi tayi tace "nagode Adamu, "ba komai suwaiba kedai ki daina yawo ba takalmi, gyada mishi kai tayi ta wuce cikin gida, kallo ya bita dashi hade da girgiza kai cike da tausayawa, duk wannan abun da sukayi a idon Baffa wanda yazo shiga da mota gida, wani abu ya darsu a ranshi ya shiga gida yayi parking... "Kanason 'yata Suwaiba? Daburcewa Adamu yayi da yaji tambayar yace "a'a Alhaji, ai tafi karfina, in ba cutarwa ba ta yaya zan auri mace cikin gata alhali ni din ba kowa bane, dariya Baffa yayi yace "in dai kanajin zaka iya zama da ita to zan aura maka ita, washe baki Adamu yayi yace "suwaiba mace ce mai kawaici da hakuri Alhaji, waye zai kita a matsayin mata, bana tunanin akwaishi, murmushin farin ciki Baffa yayi yace "kaje ka shirya, rana ita yau zan daura muku aure, godiya sosai Adamu ya tsuguna yayi ma Baffa sannan ya wuce cikin gidan da yake gadi dan sanar dasu.... Koda ya fada ma Suwaiba nan take ta amince saboda a ganinta gara taje tayi bauta mai dalili, domin ta gaji da aikin jakin da takeyi.... Ranar da aka daura auren duk wani masoyin Suwaiba saida yayi mata bakin cikin karewa da kaskantaccen mutum irin Adamu mai gadi, shi kuwa Muntari gani yakeyi Hakkinshi ne ke bibiyarta shiyasa ta dade batayi auren ba a karshe ta auri mai gadi... Rayuwa mai cike da jin dadi da rufin asiri daidai gwargwado sukeyi, gidan da ya dade yana tari ya siya mai dauke da daki biyu da kitchen nan aka kaita, sosai take jin dadin zama dashi dan dama sun saba, shekararsu biyar da aure ta samu cikin Hafeez bayan ta fidda rai, lokacin Zainab Mummy ta haifi yarta Raudha, dakatar da haihuwar tayi ta hanyar allura saboda ita a ganinta in dai zata cigaba da haihuwa tofa tabbas mata zata haifa, wannan jinin zuri'ar mahaifinta ne kamar yadda suka canfa, a lokacin da aka haifi Hafeez ba karamin girgiza mummy tayi ba, ta dinga tambayar suwaiba yadda akayi ta samu namiji a haihuwar farko wanda saidai tajishi a gari ba'a zuri'arsu ba, ko da ta tambayeta saidai tayi murmushi tace "daga Allah ne, tun daga haihuwar Hafeez abubuwa suka fara dan ja baya saboda mai gidan da Adamu ke gadi ya bar garin, jikin gidanshi ya manna shagonshi da babu isassun kaya a ciki, dama da albashin shi yake cika shagon yayi hidimar gida, babu wanda a cikin yan uwanta yake taimaka musu, a ganinta basai ta fito ta fada ba sun san bata dashi... Shekarar Reemah 15 ta tafi karatun gaba da secondary sokoto, hazakar ta tasa aka dinga promoting dinta har Allah ya kaita jami'a, anan ne ta hadu da Gaddafi dan 400l, sanadiyar haduwarsu saboda ya kasance hazikin da ake ji dashi a engineering department, ko wani irin science course ya iya, kuma yana koya musu dan su biyashi ya samu na siyan hand out, zuwan Reemah ne yasa suka shaku, itace siyan hand out da komai nashi, shiyasa baya kasa a gwiwa gurin kowa mata karatu, ko da ya gama makaranta ya fito da first class babu wanda ya lura dashi bare yayi yunkurin bashi aiki, ajiye takardunshi yayi ya dawo cikin school yana hada tutorial dan a dinga biyanshi, tausayinshi yasa Reemah tayi ma Daddy magana har ya amshi takardunshi ya samar mishi babban aiki a lagos, tun daga lokacin kauna mai karfi ta kullu a tsakaninsu har ta kaisu ga aure... A shekarar Farko Allah ya azurta ta da ciki,, lokacin Mummy ta fidda rai da haihuwa saboda dadewar da tayi, bata san akwai dan makale a tare da ita ba, Tsirar Haihuwar su kwana tara ne, domin Reemah ta haihu da kwana tara Mummy ma ta haihu, wannan abun ga mutanen "Da", bawani abun kunya bane, murnar Samun Musaddiq ba a gurin mummy bane kadai, har da kakanninshi da babanshi da ya dauki dukkan so ya daura mishi, gata babu irin wacce (Mukhtar) Hilal da Musaddiq basu gani ba, babu tafiyar da Daddy zaiyi ba tare dasu ba.. Kamar yan biyu haka suka taso, kansu daya, kayansu iri daya, kamanni ne kadai suka banbanta shi Hilal fari ne musaddiq kuma Baki ne irin bakin barebari, gasu da jikin girma Masha Allah, komawar su Reema Cypros ne ya raba su, amma kafin nan koda yaushe suna yare..... Bangaren Halima kuwa tunda tayi karyar makaranta sun tura ta china karatu shikenan su Goggo suka hau suka zauna ba tare da bincike ba, yawon barikinta ta tafi yi da kuma neman kudi, saida ta zama hamshakiyar kanta sannan ta waiwayi gida bayan shudaddun shekaru, ko da ta dawo saida ta gyara gidansu dan acewarta bazata iya zama a irin gidan ba, Sana'arta ta business ta cigaba dayi tunda dai yanzu ta gama rikewa tasan babu wanda zaizo yace zai aureta, abu daya gareta wanda za'a yabeta dashi shine duk irin duniyancin ta bata yarda da karunwanci ba saboda shegen kyankyami gareta, shekaru da dama bayan dawowarta ta hadu da wani mayaudarin yaro mai tsantsar *SIHRUL KALAM* a take ya baibayeta ta fada tarkon kaunarshi, bata tsaya dogon bincike ba ta yarda ya aureta, hatta sadaki ita ta biya mishi saboda shaukin samun wanda ya furta mata kalmar so... Sai bayan auren ne ta gane yaudararta yayi, yazo ne kawai dan ya kwashi dukiyarta yayi gaba, ko da ta fahimci haka bata dauki zafi ba dan ita mai bashi dukiyarta ne, abin da ya tsiro dashi na shigowa da mata gidane yafi tunzurata har ta kai ga aikata kisa a gareshi cikin rashin sani, A kotu ne aka fahimci cewar tana dauke da cikinshi na wata hudu, koda ta fahimci hakan saida taci kukan dana sanin zuciyarta marar kyau, Kotu bata yanke mata hukunci ba har sai ta haifi dan dake cikin ta ta yaye, haka kuwa akayi har cikinta ya isa watan haihuwa, kamar hadin baki dukka ukun ya'yan Baffa cikin garesu, Husna aka fara haifa, washe gari Nadiya ta biyo baya, haihuwar Badariyya tayi gardama saida aka yanka Leemah, ba karamar wuya Badariyya ta ba mahaifiyarta ba, bayan awanni da yi mata aikin aka fahimci jikin nata babu dadi, cike da kwarewa doctors ke aikinsu amma ina abin yaci tura, aikin mala'ika da na mutun ba daya bane, Ashe leemah ajalinta ta auro har ta haifo mishi 'ya, ba karamin tashin hankali duk suka shiga ba na rashin yar uwarsu, musamman Goggo da tayi karamar hauka... mummy ce ta

Table of Contents

Chapters

156 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156