Skip to content

Chapter 99

Chapter 99

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
Download Book

d'in da zai hana keken weelchair gangarawa da wucewa a sauk'ak'e. Sosai aka gyara side d'in. A washe garin ranar Ahmad yasa aka kawo mishi gadon samfarin royal bed kana da kujeru suma royal d'in. Aka canza mishi AC bedroom aka dawo dashi parlour kana aka sa sabon AC a bedroom d'in. Hatta labulaye da carpet da blanket da beshid sabbin Ahmad yasa aka saka komai na d'akin lemon green and white ne sosai kalan ya haska d'akin, Kayayyaki sabbi dal-dal Ahmad ya sayo yazo ya jera mishi kananu na d'inkawa kuma shida kanshi ya fito da kekken d'inkin Hayatuddeen ya fara yayyarɗa mishi ɗinkunan zamani d'inka mishi. Sosai Ummi take cikin farin ciki. Adda Rahma kuwa a kwanakin kullum sai tazo. Yau kwana biyar kenan da fara tashin Saifuddeen, suna zaune shida Hayatuddeen wanda ya kira Ummi video call sai hira da dariya suke, nan Raliya ta amshi wayar ta nuna mishi yadda aka gyara mishi side d'in da zai zauna. Murmushi yayi cikin jin dad'i da begen komawa gidan Cikin ahlinsa. Shiko Hayatuddeen kai ya jinjina kana yace. "Oho wato abinma son kaine, da yake Hamma ne zai zauna a nan kalli yadda kuka wani gyara d'akin tamkar makwancin shugaban k'asa. Wato nine jaki in na ga dama in kwan a k'asa ko?." Cikin kewar sangartarsa tace. "Ohoho my autanmu kaima ai yanzu side naka tas yake in kana soma sama zaka koma, inda Hamma Saifuddeen yake da." Cikin jin dadi yace. "Wayyo Allah kice na zama alhajin sama." Dariya sukayi baki d'aya kana suka d'anci gaba da hira daga bisani suka salami juna. Yau mako biyu kenan cib da fara tashin Saifuddeen zaune, Kuma Alhamdulillahi tuni an gama mishi duk wani abinda ya dace na sallamarsa da shared'in duk bayan wata shida zaizo a duba jikinshi. Tuni Hayatuddeen ya gama musu dukkan shirin komawarsu da taimakon Dr Malik Khan. Nanda kwana biyu jirginsu zai d'aga zuwa Nigeria. A cikin asibitin. Saifuddeen na konce shi kuwa Hayatuddeen yana harhad'a duk wani abu nasu domin gobe da asuba jirginsu zai tashi. a hankali ya zubawa d'an uwan nashi idanu ganin yadda jikinshi ke rawa kar-kar- kar tamkar mazari idanunshi sunyi jazir, gaba d'aya jijiyoyin kanshi sunyi rud'u-rud'u wani irin zufane ya yanko mishi a take, da sauri ya matso gaban gadon cikin tsananin fargaba da tsoro murya a birkice Hayatuddeen yayi kanshi jiki na rawa. Sai ya kumayi dib ya tsaya wuri d'aya da yake ganin Hamman nashi na jujjuya mishi kai alamun karya matsoshi. Idanu ya zuba mishi cikin kad'uwa sai kuma ya rink'a kame jikinshi ganin Hamman nashi so yake ya durkusa, cikin ikon Allah kuma sai gashi a durkushe bisa tsakiyar gadon. Kusan a tare suke sauk'e numfashi, Dai-dai lokacin kuma Dr Anan da Dr Malik Khan suka shigo. Samunshi a haka yayi matuk'ar sasu farin ciki nan take suka k'ara gwadashi, kana suka dank'a mishi takardar sallama da sharad'in duk bayan watanni shida zaizo. Nan Dr Anan ya kara ink'anta mishi durkuson nasa. Washe gari bayan an idar da sallan Asuba Dr Malik Khan yazo ya d'aukesu, da kanshi ya Kaisu Hilton international Airport Mumbai. Bai bar airport d'inba saida yaga tashin jirginsu. Abuja Amina kuwa yau satinta biyu kenan tana neman Hayatuddeen bata samunshi a waya, gaba d'aya abin ya dameta, gashi yanzuma ta kira layin baya tafiya, kai ta rausayar kana tace. "Allah yasa dai lfy, sai anjima da yamma zan kuma gwadawa." Gombawa d'iban fari. Yau gidan Ummi a cike yake, Raihana mutanen kd ma tun jiya tazo da Affan d'inta. Adda Rahma kuwa itama yau sammako tayi. Hakama goggo Dada da Aunty Mina. Farop da Adam sai tsalle suke yau Uncles nasu zasu dawo. Salisu ma ya kawo Salimanshi. Gida ya kacame da shirye-shiryen tarban Hamma Saifuddeen...! To AL'amarin Zaleeha fa ya girmama, Domin har Ruqquya saida aka mata dan duk an d'auka gamo tayi. Shi kuwa Baba Malam ya sani sarai babu wani gamo, ba iska a jikinta sai dai zallan iskanci inji Kakarsu da fad'i. Maryam Zahira kam su dai a dole Zaliha gamo tayi, Zeyada kuwa da Zakariyya da suke wurin Hajja Inna suma mgnar kakarsu suka bawa amanna Zaliha bata da wani iska sai zallan iskanci. Ya Ahmad d'inta kuwa wanda kwanan suka dawo Nigeria shida matarsa dan watansu bakwai a Istanbul. kasan cewarshi mai nitsuwa da hak'uri da k'aunar kannenshi suna dawowa da kwana d'aya ya taho gombe. Shiyasa yau gaba d'aya Baba Malam ya tarasu, ya jaddada musu cewar Zaleeha fa tanada sauran dama na mako biyu ta fidda miji cikin tarin masoyanta, in kuwa ta sake mako biyun nan ya cika bata tsaida gwaniba to tabbas shi zai mata zabi kuma tayi kuka da kanta. Koda aka tashi taron bayan Ya Ahmad d'in nata tabi suka shiga parlour Mamy gabanshi ta durk'usa cikin zubda k'walla tace. "Ya Ahmad ina sonshi, bayan shi babu wanda nakeso dan Allah ka bawa baba malam hak'uri ya rufa min asiri kada ya rabani dashi." Hannunta ya jawo ya ajiyeta gefenshi cikin nitsuwarsa yace. "Kin san a duniya bamu da kamar Baba Malam ko Zaleeha.?" Kai ta gyada mishi alamar eh, shi kuwa cikin sanyin yanayinshi yaci gaba da cewa. "Kin san wayeshi a wurina nida Maryam da Ziyada da Habu, bama iya jurar ganin b'acin ransa, bama iya lamuntan duk wani abu da zai tab'a mana daraja da mutuncin mahaifinmu, Zaleeha koda nace miki ina tare dake namiki k'arya, zancen gsky bayan Baba malam da Ya Ameenu nake babu yadda za'ayi kiyi ta zaman jiran gaibu, abinda ni ganima nake Al'janine , to tayaya zamu lamunci ki zauna zaman jiranshi. Kawai dolenki dollen dolene ki Zab'i d'aya daga cikin masoyanki. Ko Abdussalam ko Managernku ko Raveel ko kuma wannan abokin nawa Al'amin wanda yayi ta nace miki zuwanki Abuja last year. In kuma kinki tsaida gwani da kanki to wllahi Allah kenan Baba malam zai zaba miki cikin su." kife kanta tayi a kafadarshi tare da sakin nakasasshen kuka tare da cewa. "Na shiga uku ns, wlh ya Ahmad ina sonshi." shigowan Ya Ameenu ne yasa ta mik'e da sauri ta wuce side d'insu kai tsaye bedroom d'in Mama ta wuce bisa gado ta fad'a tana kuka. Cikin takaici Maman ta harareta tare jan dogon tsaki kana tace. "Shirmen banza kawai ni dai ina gaya miki wallahi ko bakya son Abdussalam sai ya aureki yaro d'an manya jikan sarakuna har zakiyi ta wainashi da me kika fishi kyau ko asali ko gata, ni dai ina gargad'inki kada ki bari Malam ya miki zaben tumun dare yadda yayiwa Maryam auren dole to bazan lamunci a miki hakaba, shiyasa gwara ki bar batun wancan aljanin da ya taimakeki ki rik'e Abdussalam yafi miki." wannan shine rana zafi inuwa k'una jin kalaman Mamane yasa ta mike ta koma d'akinta taci ga da koke-kokenta... Tafiya tayi nisa cikin sararin samaniya, kowa na harkan gabanshi, autan Ummu kuwa jinshi yake a takure. Hayatuddeen ne ya d'an juyo ya kalli kekyawar matashiyar dake gefenshi. Wacce duniyar Khanywood keji da ita wacce tauraronta ke harbawa a fagen rawa da wak'a. a hankali yace. "Asma'u Ahmad Matawalle," Sai ya kuma d'an juyawa ya kalleta a hankali yace. "Masha Allah. To Ashema tafi kyau a TV da

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148