Skip to content

Chapter 9

Chapter 9

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

kanki zata kom...!" da sauri tayi shiru dan bugun da taji Ummi ta kaimata a baki tare da cewa. "Raihana ki kiyayeni fa, banfa miki irin wannan tarbiyarba maza tashi ki bar nan." cikin sanyi ta mik'e tare watsawa iya Bukku harara kana tace. "Kiyi hak'uri Umminmu bazan k'araba." Goggo Rabi kuwa ji tayi kamar ta goya Raihana dan dad'in ta sulle iya Bukku. shima bappa idin dad'i yaji. shi kuwa Saifuddeen, Ummi ya zubawa ido yana karanto bac'in ranta, sai ya kuma juyawa ya kalli Rahma da ta sunkuyar da kanta hawaye na zubo mata. itako Iya Bukku cikin masifa da rashin mutunci tace. "Kaji hegiyar yarinya mai kama da aljan kujiye min fitsarerriyar yariya da uwarta bata haifeta da bisimillaba, ke har kin kai ki zageni? to na fad'a bashi da amfani, ai da yana da amfanin da ya tsare muku maraicinku, ya zauna kamar dutse ya wani zuba min shegun idanunshi ya had'e wannan fuska tashi mai kama data al'jamu." sai ta kuma ja tsaki kana ta mik'e tsaye tare da juyowa ta kalli Saifuddeen da zuciyarshi ke tafarfasa da sauri ta kauda idonta daga kanshi sabidah arararda yake watsa. cikin k'arfin hali tace. "Wannan da gani rabi mutum ne rabi aljan, mutun da aljan. Dan duk zuriyar kakanunku babu kekyawa kamanshi wannan kyau bana Allah da annabi bane, hege mai jajen kunnuwa da labban baki." sai ta kuma juyo ta fuskancesu baki d'aya kana tace. "Bisije in kin yarda da shawarata wlh ki kaishi bakin kogi dan da gani wannan d'an ruwane, in kuma kingi to ki bashi k'ok'on bara yaje yayi ta bara a cikin Gombe nasan wasu ko dan kyanshi zasu bashi sadaka, tunda nakasasshene bararce kawai aikinshi ai." cikin zafin rai Rahma ta mik'e tare da tsuke fuska kana tace. "Bamu jikiba! aniyar kura tabi daji! k'anina ba nakassashe bane, domin nakasar zuciya itace sahihiyar nakasa ba nakasar gangan jikiba. In sha Allah har abadan Saifuddeen bazaiyi bara ba, in Allah ya yarda hannunshi bazasu tab'a rik'e k'ok'on baraba. Kuma acan zuriyarku ne ba kyawawa mu ki kallemu gaba d'ayanmu ba mummuna ki kuma bincika zuriyarmu kab kyawawane waya ce miki Baddukke yana muni bare bak'i, to mu mune dukku jinin Dukku bamu da mutuwar zuciya, bare muyi maula, ki kama bakinki sai randa muka nemi al'farma a wurinki kafin ki gaya mana ba sugari, in kyawun Saifuddeen ke baki tsoro to sai dai ki makance. Ke! da kin san k'uruciyar Abbanmu sanda yanada lfy da suma zakiyi in kin ganshi, dan haka mu kyau gadanshi mukayi ki dena cewa k'anina d'an ruwa eh!." shiru Ummi tayi dan tasan Rahma nada hak'uri k'ureta akayi, Raliyya kuwa sai harara taketa dokawa iya Bukku, Goggo Rabi kuwa murmushin jin dad'i take. Bappa idi kuwa tsorone ya rufeshi yasan in sun koma zaisha rashin mutunci dan sunfi kwana biyar da jin mutuwar tace bazasu zoba da yake can garin Hashidu suke. shi yayi ta lallabata kan dole su zo, to yasan kanshi zata huce cewa zatayi da gayya yasata suka zo dan jikokinshi suci mata zarafi, shiyasa duk sai ya tsure da yake dama mijin tacene. Ita kuwa iya Bukku mari ta yarfawa Rahma, wanda yasa suka mik'e gaba d'ayansu kana cikin masifa tace. "To me amfanin kyan naku? Uban naku da yayi kyau d'in ina da aljani ya rayu a jikinsa ya zama mahaukaci tuburan. To wane rana kyan naku ya muku, tunda gaki ke bazawara baki auruba ga kuma kitika-kitikan yan mata har biyu suma basu auruba, wata k'il basu da ko mashunshini, gaya min me amfanin kyan naku, uwar rashin kunya?." gaba d'aya jikin Saifuddeeem b'ari yakeyi sabida zafin zuciya irin na kurame, ita kuwa Rahma rik'e hab'arta tayi tana kuka hakama Ummi. Itako iya Bukku cikin iya bak'ar mgna taci gaba da cewa. "To tunda baki san amfanin da kyan naku zai mukuba, ni bari in gaya miki, kuje ku fara *KARUWANCI* nasan tabbas zakuyi kasuwa, kuyi karuwanci ku tara kudi dan nasan shima wannan Saifuddeen aljanin uban naku kanshi zasu dawo dan haka kuje kuyi karuwanc...?" bata kai ga k'arishe mgnarba ta kurma wani irin razanenne ihu da ya cika unguwar baki d'aya. bata ida dawowa haiyacintaba ta kuma kurma wani azabebben ihu, sabida wasu zafafan maruka da Saifuddeen ya yarfa mata, wanda a take sai ga hagwaranta a biyu a k'asa. Ihu ta kumayi jin yasa k'afarshi ya tad'eta ta zube kasa rakacab ji kake d'im kamar an tila kayan wonki, cikin rufewar ido da fita haiyaci Saifuddeen ya zaro ball inshi ya tsula mata d'aya zai kuma na biyu ne Ummi ta rik'o hannunshi tana kuka tana cewa. "Saifuddeen ka rufa mana asiri muji da maraicinmu, gaishemu fa sukazo yi." Raliyya kuwa da Raihana sai murmushin jin dad'i suke yayinda Hayatuddeen yake tsalle yana cewa. "Allah shi k'ara Ummi barshi ya dakata hegiya mai k'aton d'uwawu." iya Bukku kuwa ai tana samun Ummi ta rike mata Saifuddeen cikin tsananin gigita da tsoro, ta mike ta wawuri takalmanta a hannu gabas ta nufa a gigice sai ta kumayi kona tayi yamma kana ta juyo arewa, ganin har yanzu dai bata gane hanyar fitarba sai ta kuma yi kudu cikin tsananin gudu ta fita tare da cewa. "Rabi, malam ku fito mugudu, aljanin sun motsa dama ba nace muku ruwa biyu bane shi ku fito mu gudu karya kashemu." ita kam Goggo rabi niyarta zata tsaya, to ganin yayanta yabi matar tashi a guje shiyasa itama tabi bayansu a saba'in suka bar garim Dukku akan baburdin Bappa idin. A cikin gidan kuwa Raihana da Raliyya da Hayatuddeen sai su kalli juna kana suyi yar dariya. Cikin fad'a Ummi ta watsa musu harara, kana ta fuskancesu da kyau dan duk sun tsaya sunyi cirko-cirko sun tasa a gaba cikin nuna b'acin ranta tace. "Dariyar me kukayi? dan baku da wayo baku san halin da muke cikiba, wani farin cike muke dashi da har zai saku dariya? kema Rahma da nake miki kallon mai hak'uri ashe ba haka bane." sai ta kuma nuna Raihana tare da cewa. "Duk kece kika jawo abinnan da baki tanka mataba da tayi ta bari, amman sai kika tsafe ido zaki zageta bayan kunsan ba hak'urine da itaba." sai ta kuma juyawa ta kalli Saifuddeen nan take sai zuciyarta ta raunata cikin zubda hawaye da rawan murya tace. "Babana meyasa kayi haka? ka mance yanzu bamu da kowa a duniya dole muna buk'atar taimakonsu." cikin tsananin kunar zuciya ya tsuguna k'asa ya fara rubutu da sauri yayinda hannunshi har rawa yakeyi dan bac'in rai. "Dan Allah Ummi karki sake cewa bamu da kowa, kin mance munada Allahn daya haliccemu shine mai rayawa mai kashewa mai badawa mai hanawa shine wanda ya mana gida biyu duniya da lahira, shine mai azirta bayinshi a duk sanda yaso shine yake ciyar da dukkan abin halitta, kuma muma shine zai cidamu, shine gatan kowa kuma muma zai zama gatanmu baifa mance da muba. Ummi koke da kike yarsu dame suka amfaneki a rayuwarki? bare mu jikokin d'an uwansu da ya rasu shekaru da dama. Ummi ki kalleni nayi al'k'awari in sha Allah zan nema da k'arfina da lfyta zan kula daku iya iyawata, karki sake kaiwa kowa kukanki ki kaiwa Allah shi

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148