Chapter 26
Chapter 26
wota mata kuma lokacin biyar saura aifa yace kawai su tafi gida, to dama shima Salisu ya gaji kawai sai suka kama hanyar dukku. Suna isa gida Hayatuddeen da Faruq suka tarbeshi, da murnarsu bayan ya ajiye ledidin yayiwa Ummi alamun tayi musu ferfesun zabbin da asuba suci ko da biredi da tea ai kam Raihana murna ta rink'a wai zata huta yin miyan asuba. Shi kuwa gefen Rahma ya zauna sai ya kuma manna kanshi a kafad'arta cikin nuna tsantsar alamun gajiya domin Saifuddeen yana da tsoron wahala to kuma Allah ya jarab ceshi da ita, cikin tausayawa ta shafa fuskarshi dan gaba d'aya jikinshi rawa yakeyi, cikin tausayawa tace. "D'an uwana sannu yau azumin da wuya anyi rana." ido ya lumshe yana mai jin azabebben k'ishi, a hankali ta kalli Ummi da tuni idonta sun cicciko da hawaye, sai ta kuma kalli Raihana cikin sanyin murya tace. "Raihana kai mishi ruwan wonka." da sauri ta mik'e duk da tana jin wahalan azumi amman tasan dole ya fita shan zafin rana, a randar tab'onsu ta d'iba saida ta cika mishi botiki sannan ta kai mishi bayan gida wanda yana wonke stab dan shi kad'ai ke amfani da bayan gidan tunda Nuruddeen da Abba suka rasu Hayatuddeen har yanzu bayan gidansu Ummi yake zuwa. Tana kai ruwan taje ta d'auko mishi kondon sosonshi ta kai mishi sannan tace. "Hamma na kai ruwan." kai kawai ya iya gyad'a mata kana ya k'ara lafewa jikin Adda Rahmanshi, jin hannun Ummi a kan gishinsa ne ya sashi d'ago kai ya zuba mata idanu, ganin alamun zatayi kuka sai ya yunk'ura ya mik'e jiki na rawa, cikin sanyi tace. "Babana baka da lfy ko." kai ya jujjuya mata a hankali kana yasa hannunshi kan cikinshi da yake a d'akale bafa irin d'akalellen cikin maceba a a irin nasu na maza, sai ya kuma nuna mata mak'oshin sa alum k'ishi yakeji, cikin kula tace. "Je kayi wonka zakaji sanyi Babana." Kai ya gyad'a mata sannan ya juya a hankali ya shiga kayan da zai sa ya d'auka sannan ya shiga bandakin, yana shiga ya zare kayan jikinshi duka sannan yaje ya zauna bisa dutsen wonkan da yaketa shek'i da yake a inuwa yake baiyi zafiba, surarshi ya k'arewa kallo idon ya zuba kan mararshi a ranshi yace. "Hmmm yau kam kaji haza bayan baccinma har b'uya kayi ka koma cikin cikina ko?." sai kuma ya fara watsa ruwan. To Alhamdulillahi da yayi wonkan ya ji dama-dama gashi yana fitowa ana kiran salla, al'wala yayi wanda tuni Ummi na gabanshi rik'e da dabino da surki mai d'umi, dabinon ya amsa addu'a yayi kafin yaci guda uku, da sauri ya jujjuya kanshi alamun shi bazai sha surkinba. infa da sabo Ummi ta saba don haka yake ba komai yake ciba kuma zai tace maka yana jin yunwa kana kawo mishi abinci in ya tsakuri kad'an sai ya cire hannu wai ya k'oshi. da sauri Hayatuddeen ya mik'o mishi pilet d'in su kankana to nan ya amshi fork a hannun Raihana sannan ya fara sokawa jikin kankanan da Rahma ta zuba mishi madara da sugar kad'an sabida ta sanshi da son zak'i, ido kawai Ummi ta lumshe tana kallonshi sai yana tuno mata k'uruciyar Abbanshi, bai shanye rabinshi bama yayi wani sassanyan gyatsa tare da mik'ewa wai ya k'oshi kenan, jin ana tada kabbarane yasa Ummi bata hanashi fitaba, shi kuwa kama hannun Hayatuddeen yayi suka fita zuwa masallacin. Suma su Ummi sukayi haramar yin sallan. Bayan an idar da salla, suna fitowa, Mudassir, Warisu, Salisu. Suka nufi cikin gidansu Saifuddeen kai tsaye a babbar taburmar da Ummi ta saba shimfid'a musu suka zauna. Rahma mace ta mik'e a hankali ta fara jero musu abin motsa baki, kankana da ayaba da dabinon suka fara ci, sunaci suna hira Rahma kuwa ita da kanta ta matso gefensu zama tayi tare da yi musu harara sannan ta jawo kulan dake gabanta cikin fidda numfashi tace. "Daga yau bazan sake biye mukuba, kun sani yi muku yambos wallahi ba k'aramar wuya na shaba kirba doyan nan wuya gareshi, gashi Raihana k'in tayani tayi wai ai nike biye muku." Saminu da yanzu ya shigo tare da Saifuddeen ne ya harari Raihana tare da cewa. "Yan ubanci zatayi mana shareta Adda Rahma ran salla ke kad'ai zamu bawa barka da salla." tab'e baki Raihana tayi tare da cewa. "Kada ku bani mana ni dama ban rok'aba." Muddassir ne yayi d'an gyaran murya kana ya kalleta cikin tsuke fuska da bada umarni yace. "Ni bazanma ci wannan yambos d'inba, yanzu ki d'an soya min dankali." tura baki tayi tare da mik'ewa tana cewa. "Ni wlh na gaji kuma yunwa nakeji." Ummi ce ta d'anyi dariya kana tace. "Zo Raihana taho nan ga dankalin dama na soyawa Bappa Alinku na kuma d'iba musu zoki basu nasan Mudassir so yake ya wahal min dake." da sauri Saminu yace. "To ni kuma indomi nakeso mai ruwa-ruwa yaji yaji da al'basa." dariya sukayi baki d'aya dan sun san bazata iya musa mishiba, sai kuma suka zuba musu ido jin tana ce mishi. "Yanzu ne kakeso ko sai kun taso daga tabsir ne zan maka?." ido ya lumshe kana ya zuba mata ido cikin sanyi yace. "Ki huta sai mun dawo zamuyi aikin tare." Ummi kam kauda ido tayi Warisu kuwa da Salisu tuni suketa hirarsu, Mudassir kuma tuni ya zuba musu yambos d'in har ya fara ci Adda Rahma kuma tea tai ta had'a musu, nan suka fara ci sunaci suna hira. Shi kuwa Saifuddeen gefen Ummin shi ya rab'a a hankali ya konta tare da d'ora kanshi a cinyarta, gyara zamanta tayi dan yaji dad'in konciyar, kanshi ta d'an shafa cikin ido ta zuba mishi ganin sosai fa ya rame hancin shi zuwet har bisa baki idanunshi sun k'ara fitowa, farinshi ya k'ara baiyana cikin kula ta kalleshi ganin ita yake kallo tace. "Tashi mana Babana kaje kaci abinci da yan uwanka ai zakafi jin dad'in cin." sanin in bai ciba hankalin ta bazai konta bane ya sashi yunk'urawa ya tashi zaune sannan ya amshi cup d'in da Adda Rahma ta cika da zazzafan tea mai k'auri sai k'amshi yake, gyara zamanshi yayi kana ya mik'awa Warisu hannunshi alamun ya bashi abinda suke ci d'in, ganin Warisu zai kwatso mishi da yawane ya sashi nuna mishi yatsa d'aya alamun guda d'aya zai bashi, kauda kai wWrisu yayi kana ya mik'o mishi guda biyu, fuska ya d'an had'e dan shi cikinshi ya cika da ruwan da yaketa sha, ya kuma san Ummi zata sashi dole ya cinye biyun da ya sako mishi, haka kuwa akayi dole ta sashi yaci sannan ta samishi soyayyan dankalin turawa, nanma yanaci yana d'an korawa da tea d'in a haka dai yaci kad'an. Jin an fara kiran sallan isha yasa suka mik'e duka dan yin al'wala, dai-dai lokacin kuma Ahmad ya shigo shida Raliyya, da sauri Rahma tace. "Ke Raliyya meya kawoki a daren nan?." kai ta d'an rausayar tare da gaida su Saifuddeen sannan ta zauna gaban Ummi cikin sanyi tace. "Kai Adda Rahma ai nida Ya Ahmad ne muka zo nayi kewanku ne especially Hamma Saifuddeen, shiyasa nace yau mu taho tare kuma tare zamu koma." Cikin fad'a Saifuddeen ya mata
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148