Chapter 61
Chapter 61
dake zagaye awurin saida Dr Adnan yahad'a zufa sharkaf sabida tashin hankali da fargabar dake tare dashi, kallo d'aya zaka yimasa kagane tsantsar tashin hankalin da ke shinfide akan fuskarsa cikin mutuwan jiki yayi isa office d'inshi, Cikin hanzari Ummi dake zaune akan sallaya tana jan jarbi, tamik'e tsaye tana mai zuba mishi ido tare da fad'in. "Baban Adnan yafarka kuwa?." saurin sai-sai ta nutsuwarsa yayi dan son boye tashin hankalin da yake ciki kana yace. "Ehm Uhmm ba..ba..bakomai fa Ummi in sha Allah zai farka in Allah ya yarda ba wata matsala." ita kam Ummi cikin rashin gamsuwa da maganarsa tafara magana cikin zubda kwalla tanafadin, "Ka fad'amin halin da yake ciki in yamutune ma kada ka boye min dole inyi imani da k'addarata." da sauri su Raliya dasuke zaune agefe suma bayan sun idar da sallah suka taso. Hayatuddeen dayanzu dawowarsa daga masallacin dake cikin asibitin,shima ya'iso da sauri, ganin haka yasa Dr Adnan cewa. "Ummi baifa mutuba zo kuganshi ma." kana ya juya yayi cikin room d'in dasauri suka rufamasa baya,can suka hangosa kwance ga na'urori sakale ajikinsa da sauri suka nufi jikin gadon,idanunsa arufe ruf bayako motsi, abinda zainuna maka cewa yanada rai shine numfashin shi da yake ja tacikin na'uwar jan numfashi. cikin rauni da fargaba jiki na rawa Ummi tariko hannunsa yayinda hawaye ke kwaranya a idanunta murya na rawa tace. "Saifuddeen wanene yayimaka wanna illa haka? waya zalincemu zalumci mafi muni arayuwar mu? memuka tare masa?." a tare tajero tanbayar tareda kife kanta ajikin gadon ta saki sassanyan kuka. Hayatuddeen,da shima kukan yake ganin dan'uwansa acikin mawuyacin hali, Raliya Raihana duk kuku suke, Dr Adnan ma shima kukan yake babu mai rarrashin wani a cikin su zuwa can Dr Adnan yashare hawayen sa cikin hanzari yamaso kusa da Ummi muryarsa narawa ya kwakulo murmushi dole yace. "Ummi bawata masalafa ku kwantar da hankalin ku in sha Allahu zamuyi duk abinda yadace." cikin muryar kuka Ummi tace. "Adnan duba kaga halinda Saifuddeen yake cikifa sannan kace wai babu wata damuwa, ka duba ka gani nice yau a gaban Saifuddeen amma yagaza d'aga ido yadubeni bare harya shiga farin ciki kamar kullum saboda ganina akusa dashi, lallai Saifuddeen d'ina yana cikin mawuyacin hali." sai ta kuma rik'e hannunsa tamatse acikin nata tanamai cigaba da kukan, da sauri Dr Arabi yaturo k'ofar da sauri dan duk abinda suke yanajinsu daga cikin offece insa,ya'isa ciki tareda d'aura wata na'urar dake rike a hannunsa asaman kirjin Saifuddeen dan da alamun bugun zuciyarshi ta tsananta da sauri yace. "Ummi ku d'an je waje zamuyi aiki yanzu." dakyar Ummi tasaki hannun Saifuddeen ta fita tana cigaba da sharar kwalla, su Raliya ne sukabi bayanta. Hayatuddeen ko wayar Saifuddeed ya d'auka wanda yagani agefensa sanna yafita, sunafita Dr Arabi yahad'a na'urar daya d'aura kan kirjin Saifuddeen, kana ya juyo yana fuskantar Dr Adnan tare da cewa. "Haba Dr Adnan a matsayin ka na Dr bai kamata karika kashewa majin yatanka guiwaba, kamata yayi karika karfafa musu goiwa surika sawa aransu majinyacinsu zaisami lfy, amma kaima kazauna agabansu kana zubda hawaye ai sai ka saka musu kokwanto azukatansu, tabbas nasan shakuwar dake tsakanin ka da Saifuddeen, so hakuri zakayi kabasu kwarin goiwa akan samun saukinsa sai kaga komai yatafi dai-dai." a hankali Dr Adnan yashare hawaye kana yace. "Hakane amman kaima kasan dai akwai babbar masala, bazan tab'a iya mik'ewa ya tsaya da kansa ba,bazai iya morar kansa ba, saboda illar da suka yimasa agadon bayansa zuwa kugunsa,bansan tayanda zansanarwa Ummi wanna mummunar labarin ba" a hankali Dr Arabi yace. "Nasani,to amma ya zamuyi da ikon Allah, shi ya halicci Saifuddeen kuma ya fimu sonshi kuma insha Allah shi zai zama gatanshi, yanzu dai ya kamata musan menene mafita." shiru Dr Adnan yayi saboda tunanin hanyar data fi dacewa don dole a wuce da Saifuddeen Abuja. Koda Hayatudden yafita Gefe yakoma yazaro wayarsa a'al'juhu dan tun jiya yake akashe yakunna sanna yasaka wayar Saifuddeen acikin aljuhun, bayan yakunna wayarsa saiya lalub'o number Ishaq wato babban abokin Saifuddeen, yana d'agawa yace. "Hello Hatuddeen yau kuma gaisuwar sassafene za'ayiwa Hamma Ishaq." cikin raunin murya yace. "Ina kwana Hamma Ishaq." da sauri yace. "Lafiya lau, Hayatuddeen." bayan sungaisanne Hayatuddeen yake ce masa. "Hamma ishaq muna asibiti Hamma Saifuddeen bashida lfy." ba k'aramin tashin hankali Is'haq yashiga ba dajin cewa abokin sa na'asibiti wanda jiya da yamma suka rabu lafiya-lafiya sannan kuma yanada tabbacin cewa bakaramin ciwo bane zaisa Saifuddeen yakwanta a asibiti. shiko Hayatuddeen katse wayar yayi yakoma inda su Ummi suke, jugum-jugum sukayi kowa da abinda yake sakawa azuciyarsa. sunan zaune har gari yayi haske. Karan ababen hawane yacika cikin harabar asibitin motoci da mashunan guragu irin masu tsada da kyau wanda zasu iya kaiwa 23 kana sai wasu motoci kusan guda 6 wanda sukeda tambarin (Jonapwd) Gombe state chapter all the best! bi ma'ana tambarin k'ungiyar nakassasu ta jihar wato Joint national association of persons with disabilities. kuma kowani mashin guda mutane biyu ne ke kansa,haka sukarika faka mashin d'in suna sauka akansa,abin mamaki mutanen duk nakasassune, sai dai bazaka tab'a banbance makafin cikiba domin babu sanduna a hanunsu bare yan jagora kana suna cikin tsabtacecciyar shiga ta alfarma mafi akasarinsu sunfi kama da ma'aikata, kuramen ciki kuwa bazama ka tab'a zaton sunada wata nakasa a jikinsu ba, guragu kuwa sai dai ka gane da sawun wasunsu da suke a shanye wasu kuma da sanduna suke dan tokarawa gaba d'aya sun cika harabar asibitin kuma ba hayaniya bare sowa suna komansu cikin tsari da wayewa fiyema da masu ji da gani yayinda wasu ke ambaton. "Ya Allah! kabaiwa d'an uwanmu Garkuwarmu lfy, idan kacire manashi a cikinmu bamu san ya zamu k'are da rayuwaba dan munsan cewa zamu tagayyara mudawo abin kyama abin gudu acikin al'umma sunai mana kallon wasu hallitu na daban." makafin cikinsu nata fad'in. "ku kaimu inda yake?." Mutane sukarika fitowa daga cikin asibitin, wad'anda suke gefe da asibitin wato mazauna gefen asibitin suma suka shisshigo,danganin taron mutanen dasuka shigo cikin asibitin. Dan ganin abinda kefaruwa,jama'ar dasuka fito dan kallon mutanen sunsha mamakin jin kallama da ya kefita abakin wadanna nakasassun,sai ambaton Saifuddeen suke, jama'a duk suka cika da alhinin jin sunan wanna bawan Allahn dasuke ammaba,to waye shi dahar wadanna mutanen zasu nuna damuwarsu da tashin hankalinsu akansa,lallai wanna mutumin komai akayi adaline,sosai a garesu domin wasuma sunyi zaton ko zanga-zangar lumana nakasassun keyi, gurin ya kacame da hayaniyar mutane dake tambayar meke faruwa. Hayatuddeen ne yamik'e tsaye da sauri yace. "Ummi mutanen Hamma Saifuddeen ne sukazo dan naji sunata kiran sunansa bari naje wurinsu." kai kawai Ummi ta'iya gyad'a masa alamar toh. Hayatuddeen yafito farbajiyar asubitin suna ganinsa suka nufi inda yake suka zagayeshi,suna fadin. "Ina Saifuddeenin d'inmu yake kanunama inda yake." hannu sa yad'aga sama yana juyashi, tare da yin sauri ya isa gaban Ishaq cikin girmamawa yace. "Ya ishaq barka da zuwa." da sauri ishaq ya mik'o hannu ganin haka shima Hayatuddeen ya mik'o mishi hannu tare da cewa. "Gani nan Ya ishaq." da sauri ishaq yace. "Yauwa Hayatuddeen ta ina Saifuddeen yake muje mu ganshi." cikin d'an murmushi Hayatuddeen yace. "Hmmm kai ishaq kullum lamarinka akwai k'arfin hali da iya ruggumar k'addara wai muje mu ganshi sai kace kana gani." shima Ishaq murmushi k'arfin hali
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148