Skip to content

Chapter 2

Chapter 2

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,204 words 0 views Progress saved
Download Book

sauran yayunshi tuni ya meda hankalin kan hadda da sauran littafai da ake musu a isilamiyarsu. Saifuddeen yana ta murnar zai tafi JSS two wata rana kwatsam ya tashi da wani irin azabebben zazzabi mai tsananin zafi, kwana yayi yana firgita, da safe kuwa yana tashi sai mura ba tari amman yanzu yanzu hancinshi na zubda ruwa kana hancin yayi jazazir hakama idanunshi, ganin haka Ummi ta kama hannunshi taje ta nunawa wata makociyarsu tsohuwa iya shatu kakar Salisu abokin Saifuddeen, tana nuna mata jikin Saifuddeen d'in. Tana gani tace k'end'ace bak'on daurane zata fito mishi ga kuma azabebben zazzab'in sank'arau daya rufeshi, haka yasa ta nemi tsink'aro da gero ta barzasu ta jik'ashi da ruwa sannan ta kurba sai ta fesa mishi a jikinshi, cikin ikon Allah kafin dare duk Sun feso sun fito birjink a jikinshi har cikin tafin k'afafunshi zazzabin sank'arau kuma tamkar zai hallakashi. Koda dare yayi Ummi ta d'aukeshi suka koma side inta, abu kamar mafarki koda gari ya waye sai aka samu jikin Saifuddeen yayi sumut duk bak'on dauran nan ya b'ace ya koma cikin jikinshi ya k'ume yaro sai karkarwa yakeyi dan zafin zazzabi ga kuma sank'arau da ya hanashi sukuni wanda har cikin kunnenshi yakeji yana bada sautin dummmm, ba irin mgnanin da ba'a bashi amman sunk'i su kuma fitowa a lokacin kuma ba'a wani damu da batun asibitiba ko riga kafinshi ba'a fiye yiba a garin. haka dai Saifuddeen yayi ta shan wahalar sheretuwannan da zazzafan zazzab'in sank'arau daga k'arshe yayi sanadin kuram tashi. Wannan al'amari ba k'aramin girgiza family ensu yayiba don Saifuddeen yarone mai shiga rai, gashi da nitsuwa da al'kunya iyaye da da 'yam suna matuk'ar sonshi ran da aka gane Saifuddeen ya zama kurma a ranar anga tashin hankalin Bello Abba kenan hakama Nuruddeen daya dawo makaranta aka gaya mishi, kuka yayi tayi dan duk k'annenshi yafi k'aunar Saifuddeen Hayatuddeen kuwa lokacin shekaranshi 4 so baisan meke faruwa ba yakan dai yi kuka in yaga suna kuka. A Daren ranar jikin Abba ya tashi a wannan ranar ne karo na forko da ya rink'a ihu tamkar yaro k'arami. K'arfe biyu dai-dai na dere ya kama hannun Saifuddeen dake bacci ya mik'ar dashi, kana ya jashi suka fito haka ya rink'a janshi koro-koro duk inda suka samu masallaci sai ya sashi suyi Al'wala suyi nafila raka biyu kana suci gaba da tafiya. Saida akayi sallan asuba sannan suka dawo gida, nanma dan yaga Saifuddeen d'in yanata kuka. Suna dawowa Ummi ta jawo d'anta ta ruggumeshi cikin kuka take tambayarshi ina sukaje, baki ya bud'e da nufin ya kuma gwada yin mgna amman ina ya kasa, hakan ya sashi kife kanshi jikin gini yana wani irin gurnanin azabebben kukan da duk mai imani sai ya tausaya mishi babu mai sanin zafi da kun'an da yakeji a ranshi sai wanda ya tab'a shiga irin wannan halin ace an haifeka lfy ranatsaka nakasa ta sameka, so yake ya bud'i baki ya yiwa Umminshi bayanin yadda yakeji amman ina Allah bai bashi damar hakanba ganin ya kuma kife kanshi jikin ginin ya sake zazzafan shesshek'an kukane yasa Yayanshi mik'ewa ya nufi inda yake. Da Sauri Nuruddeen ya kamoshi, hannu yasa ya tallabe kanshi cikin tsananin kuka da tausayawa k'anin nashi murya na rawa yace. "Saifuddeen...!!! BY *NAKASA BA KASAWA BACE* *PAGE 2* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡ _Ga masu buΖ™atar biyan kuΙ—in karanta wannan littafi na Nakasa ba kasawa bace.Ζ™owa a buΙ—e take, turo katin mtn na 300 kacal ta wannan layin 09097853276. Ko kuma ka/kiyi transfer ta bank account na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ka/kiyi screenshot shaidar biyanki ki turo min, sabida kids samu damar karantawa koda na gama free page_ "Saifuddeen magana kake son kayi ne?." cikin tsananin kukan ya rink'a gyad'awa Nuruddeen kai. Duk da k'arfin hali irin na Ummi tuni kuka takeyi dan tausayin d'an nata wanda yaci sunan babanta. shi kuwa Nuruddeen cikin mamaki ya kalli k'anin nashi cikin kad'uwa yace. "Kana ji nane idan nayi Mgna kana gane me nake cewa ne?." kanshi ya jujjuya kana ya zame hannunwan Nuruddeen daga rik'on da ya mishi sannan ya tsuguna a gaban Nuruddeen d'in tafin hannunshi yasa ya lailaiye yashin tsakiyar gidan nasu kana yasa yatsarshi ma nuniya ya fara rubutu da harshen fullanci yace. "Ya Nuruddeen bana jin kuma naji na kasa yin mgna, cikin mak'ok'orona kamar an cusheshi kunnuwana sunyi dim bana jin komai, Amman da ina ganin bakinku ina gane abunda kuke fad'a." sai ya kuma d'ago kanshi ya kalli Nuruddeen daya rusuna yana karantar rubutun yana kuka tamkar an musu mutuwa, hannu yasa ya share hawayen fuskar Nuruddeen d'in kana yaci gaba da rubutu da harshen hausa yace. "Ya Nuruddeen ku nema min mgni mana, insamu irink'a Magna kamar kowa, ku kaini a bud'e min kunnena mana in rink'a jin muryar Ummi na da naku ku rink'a hira dani." Ruggumoshi Nuruddeen yayi tare da sakin kuka murya na rawa yace. "In sha Allah zan nema maka mgni Saifuddeen zan tattare dukkan buk'atun rayuwata zan jinginesu zan gina taka rayuwar, don gobenka tayi kyau." Sai ya kuma tsaidashi tare da matsawa baya suna fuskatar juna yace. "Saifuddeen kana gane abinda nike fad'i maka?." kai ya gyad'a mishi, da sauri alamun eh yana ganewa, ganin haka Nuruddeen yayi wani murmushi da yafi kuka ciwo a zuciya tare da cewa. "Saifuddeen kayi murmushi kamar yadda nayi." ba musu yayi murmushin da har saida dimples enshi duka uku suka lotsa biyu na kumatun gefe dama da gefe hagu d'aya kuma na tsakiyar d'an gemunshi, murmushin ya kuma fad'ad'awa ganin itama Ummi tana murmushi still su duka hawaye na kwaranya a idanunsu, Abba kuwa tuni ya mik'e bisa taburmar dake tsakiyar gidan da yake konciyan zafine, kwanan woje akeyi, kuma har yayi baccin da ya kwana bayiba. Shi kuwa Nuruddeen hannunshi ya d'aura kan k'ahon zuciyarshi kana ya fara mgna yana murmushi still hawaye na zuba yake cewa. "Saifuddeen *Babu nakasasshe sai rago*, kasa a ranka ita. Nakasa ba kasawa bace, in sha Allah ni d'an uwanka Nuruddeen zan baka dukkan kulawa zaka rayu kamar ko wanne mai ji da gani da mgna, kada ka kareya shi nakasa baiwace ta Allah wonda yakewa wanda yakeso, lokuta da dama bahaushe na karin mgnar da kan zama izina misali inda suke cewa, wani hanin ga Allah baiwane." sai ya kuma sharte hawayenshi kana yaci gaba da cewa. "Zan nema maka mgni iya raina da mutuwa, amman kasa a ranka mgni baya canza k'addarar mutun, kasa aranka wani hanin ga Allah baiwace. Kasa a ranka Allah yayi maka rahamar tsare maka harshenka daga sobon Allah ne kasa aranka Allah ya tsare maka kunnenka daga jin zantuka na haram ne da aikata sabon Allah, kamar yadda haka abin yake ga makaho Allah ya tsare mishi idanunshi daga ganin Haram, Saifuddeen zan yi iya iyiwana kan ciwonka dana mahaifinmu har sai dai in yafi k'arfina." tuni Rahma da Raihana suketa kuka, Hayatuddeen ma dake gefen Ummi kuka yakeyi ganin yayunshi na kukan. Kuka sosai Ummi takeyi dan tausayin Nuruddeen yaro k'arami Allah ya jarab ceshi ya d'ora mishi nauyin jinyar uba da k'ani bugu da k'ari shike ciyar dasu, domin sam Abba baya iya noma makaranshi sai su murdeshi haka yasa

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148