Skip to content

Chapter 39

Chapter 39

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

sauran tsirarun mutane, cikin tattausan lafazi yaci gaba da cewa. "To fili dai na yaran d'an uwanka ne kamar yadda kasha jaddada min na kuma fahimceka baka son shiga hakk'insu ne ko ince kana gudun kar ka zama sanadin rabuwansu da kadarar mahaifinsu, to nima bana son takuraku ko in saku yin abunda bakuyi niyaba, to amman ba yadda zamuyi domin wannan filin ya kasance fili mafi girma da daraja gashi a bakin hanya gashi a bakin kasuwa gashi babban filine to wannan dalili yasa idanun manyan masu hannu da shuni ke kan filin dan duk abinda akeso za'a iya yi a wurin, hakan yasa tun makon daya gabata hukumar ACCESS BANK suketa yi mana zirya, na gaya musu duk yadda akayi a baya to sai sukayi ta k'ara farashin yadda zasu sayeshi sama da yadda sauran suka sayeshi a baya, har ta kai da sun ninka kud'in, to shiyasa nace bari dai in sanar muku in kun amince la basa in kuma kunk'i amincewa bani da abin cewa, sai dai kuma dole ku dage kuyi koda shaguna ne a wurin domin kauda idanun mutane." jin yayi shiru alamun ya dasa aya ne yasa Waziri cewa. "Wannan gsky ne babu dole cikin cinikin, amman kuyi k'ok'arin gine wurin in har bazaku saidaba." cikin kamala Bappa Ali yace. "To ba matsala ai Alhamdulillahi tunda zuwa yanzu Saifudddeen ya girma ya kuma mallaki hankalin kanshi, ya kuma ji komai dan haka zamuje gida zamu tattauna duk abinda ya dace, kana in mun yanke hukunci zamu zo mu sanar muku, amman yanzu sai munje mun sanar da mahaifiyashi da k'annenshi dama yayarshi." gyaran murya Garkuwa yayi tare da cewa. "To ba matsala muna jiranku sai munji shawarar da kuka tsaidan." Shi kuwa Saifuddeen wani kekyawan murmushi yayi wanda ya k'ara baiyana asalin kyanshi kai ya jinjina musu alamun sai kun jimun. To da haka dai sukayi sallama suka tafi gida. Koda suka koma gida kai tsaye sashin Ummi suka nufa inda suka shige har cikin d'aki kana Saifuddeen ya kira Rahma, nan Bappa Ali ya musu bayanin duk yadda sukayi da sarki, to ita Ummi cewa tayi ba matsala a kamfanin Mtn d'in hayan filin ko ba komai ai zasu rink'a samu ribar filin, shima Bappa Ali ya amince da hakan hakama Saifuddeen da Rahma, to duk dai sun amince bayan sun gama mgnar wannan filin sai kuma Bappa Ali ya kalli Ummi cikin mutuntaka da tausayinta a matsayinta na yar goggonshi kuma matar yayanshi murya a tausashe yace. "To sai kuma batun filin su Saifuddeen d'in na bakin kasuwa ya kuka gani, kun ga dai tsawon shekara ake bibiyar filin wanne hukuncin kuka yanke?." shiru Ummi tayi ta nisa cikin nazari tana tuno mafarkin da tayi kwana biyu da suka gabata inda taga Abbansu Saifuddeen tamkar a zahiri yana ce mata. "Kada ki hanashi saida filin, a saida ki kuma bawa Saifuddeen kud'in kada ki damu d'anki zai kula da komai." to a ranar wuni tayi tana nazarin wanne filin ne zata bari su saida sai yau ta samu amsar dan haka cikin nitsuwa tace. "Ni dai a karan kaina na amince a saida filin, dan banga amfanin zaman nashiba tunda ba komai muka gina a wurinba." sai ta kuma kalli Saifuddeen cikin kula da yanayinshi tace. "Babana ko kana da kud'in da zaka gina mana shaguna ne a wurin?." da sauri ya girgiza mata kai dan shi Allah-Allah yake su amince a saida filin, murmushi tayi tare da cewa. "To ya ka gani ka amince a saida ne?." murmushi yayi tare da lumshe mata ido kana ya bud'esu a hankali sannan ya zaro woyarshi tare da rubuta mata. "A tambayi Adda Rahma dasu Raihana in sun amince dai to ni na amince na kuma amincewa Hayatuddeen tunda shi har yanzu k'ara mine." yana gamawa ya mik'awa Ummi bayan ta karanta ta mik'awa bappa Ali shima yana karan tawa ya mik'awa Rahma, koda ta karanta murmushi tayi tare da zubawa k'anin nata idanu cikin sanyin muryarta tace. "Ni na amince Raihana da Raliyya kuwa amincewar Ummi itace tasu, tunda suma har yanzu yarane gwara Raihana za'ace ta kai matakin balaga." murmushi yayi tare da mata alamun ta kira Raihana. Koda ta kira wota da akayi mata bayani sai ida nunta suka cika da hawaye cikin rawan murya tace. "Bappa Ali ka cewa Hamma Saifuddeen yayi duk abinda ya dace a kan duk abun da mahaifinmu ya bar mana ba sai an nemi shawararmu ba." itama Rahma sai cewa tayi. "Damu da kadararmu ai duk kaine Garkuwarmu." to nanfa suka tsaida mgna akan za'a saida filin. Cikin ikon Allah a kwana biyar aka gama duk mgnar filin da za'a kafa services d'in da kuma filin da za'a gine Access bank. Jin kud'in hayan filin services d'inma ya matuk'ar bawa Ummi Mamaki inda sukace duk shekara zasu biya one million, sannan filin bakin kasuwar kashi uku suka rabashi in duka ce kashi biyu zasu saida d'aya kuma zasu ajiye kasan cewar filin k'atone eka-eka ne bila adadin, to bankin sun amince dan kashi biyun zai ishesu suyi gininsu mu samman in sunce bene zasuyi har filin zai zarta zatonsu, million biyu da dubu d'ari uku da hamsin aka karkare cinikin a cikin fadar masarautan dukku, ranar ma Saifuddeen bai je kasuwaba. Sai washe gari tun da sanyin safiya suka tafi shida Salisunshi, koda yaje sauri-sauri ya raba ledodinshi kana ya wuce shagon Alhaji Kabiru inda yayi kicibis dashi yana shirin fita zaije gidan Alhaji Sani, koda Saifuddeen yace mishi zai sari magin ya samu kud'in da ake buk'ata sosai Alhaji Kabiru yayi mmki, dan haka sai ya d'aukeshi suka tafi gidan Alhaji Sani, shima kanshi Alhaji Sanin yayi mmki sai sukaji tsoron sharrin zamani dan haka sukace dole sai yazo da manyanshi an gaya musu ina ya samu kud'in, bai damuba ya basu tabbacin zai kawo manyan nashi. Koda suka dawo kasuwa ranan bai saida pure water ba, gidansu Ishaq ya wuce, ya kuma yi sa'a ya sameshi a gida nan ya tad'a mishi komai nan take kuma Ishaqn ma ya bashi k'arfin guiwa ya k'ara da cewa. "Alhamdulillahi dama jibi Ya Rabi'u zai shigo Gombe kaga zai zauna maka matsayin lawyernka mai kare dukiyarka da kadarorinka sannan yasa hannu a lamarin dan gudun kada su cutar da kai ko su damfareka zan kuma sanarwa Babanmu ma dan ya kasance da saninshi." ruggumeshi Saifuddeen yayi tare rubuta mishi sak'on godiya. daga nan ya koma kasuwa ya d'an zazzagaya da ruwan. Shi kuwa Ishaq Saifuddeen yana tafiya ya sanarwa babansu tare da neman shawararshi ya amince ya kuma basu k'arfin guiwa sannan ya kira barrister Rabi'u ya sanarmishi komai yace ba matsala sai ya shigo Gomben. Shi kuwa Saifuddeen koda ya koma gida, cikin nitsuwa yayiwa bappa Ali bayanin komai. Cikin nisan nazari da zurfin tunani Ummi da Bappa Ali da Rahma suke karanta duk bayanin da ya musu, tun randa ya fara kai kaya shagon Alhaji Kabiru da yadda yake sonshi da yadda ya samu su Alhaji Sani suna tattauna batun tallan sirri da company maggi ta kawo musu, da yadda yaje ya sameshi da mgnar da yadda ya gaya mishi batun yawan kud'in sarin da ake buk'ata, ya kara musu da cewa ya

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148