Skip to content

Chapter 63

Chapter 63

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

str zuciyarshi da jikinshi na cike da fargaba da tsoron halinda martashi Rahma zata shiga in taji abinda ya samu d'an uwanta, ya rasa tudun dafawa, a fili yace. "Ya ilahi ya mujubbat da'awati ko taya zan sanarwa Rahma." sai kuma yayi sauri zaro woyarshi Ishaq ya kira, bayan sun gaisa yace. "Kun isa lfy,?." "Lafiya lau Alhamdulillahi." gyara zamanshi yayi tare da kallon k'ofar corridor d'in part d'in Raihana sannan yace. "Kun samu Dr Aliyu ko?." "Eh to gsky mun samu tarba daga wurin Doctors har uku to gsky ban sanan wanne ne Dr Aliyun ba a cikinsu." cikin sanyi yace. "Zakaga Dr Aliyu shima nakasasshene ai domin shima yanada matsalar spanal cord kuma shine big doctor a k'asarnan in dai a wannan fannin ne, uban gida nane kuma wa nane d'an kawuna." cikin jin dad'i Ishaqa yace. "Alhamdulillahi, hakan yayi kyau domin dama shi nakasa ai ba kasawa bace, kuma ya yi mana k'arin bayani kan mu kontar da hankalin mu, Alhamdulillahi kuwa tuni ya farfad'o kuma yana cikin haiyacin sa, so zuwa gobe da safe zasu fara bincikan adadin zurfin ciwon." lumshe ido Dr Adnan yayi kana yace. "To Allah ya kaimu, in sha Allah nima gobe zan taho please kuke kontarwa Ummi hankalinta." "In sha Allah ba matsala." cewar Ishaq. Kana daga nan sukayi sallama, shi kuwa Dr Adnan Dr Aliyu ya kira bayan sun gaisa yake mishi godiya tare da tambayar ya mai jikin, so shima Adnan ya samu d'an nitsuwa duk da cewa Dr Aliyu ya tabbatar mishi cewa Saifuddeen ya samu nakasar lakkar bayanshi. bayan sun gama woyar ne yana d'ago kanshi ya hangi Rahma tsaye bakin k'ofar kitchen ta kafeshi da ido gaba d'aya jikinta tsuma yakeyi tuni hawaye sun jik'a fuskarta, mutuwar zaune yayi domin tabbas yasan taji duk wayar da yayi dasu, dan sam hankalinshi bai bashi ko tana kitchen ba. Ita kuwa matsowa ta farayi a hankali take taku still jikinta na rawa, gabanshi ta tsaya tare da tirtsetsen cikinta, da sauri yasa hannu ya jawota jikinshi kan cinyarshi ya ajiyeta, suna fuskantar juna, murya na rawa tace. "Me kuma zaka boye min Ya Adnan me zaka boye min? gaya min me zaka boye min. wani abune kuma ke tinkarar rayuwarmu? meya samu d'an uwana? ina yake, waye zai nak'asa Saifuddeen ne ko Hayatuddeen gaya min wani hali Ummi ke ciki?." gaba d'aya ta birkice ta gigitashi da tambayoyinta yama rasa wanne d'aya zai amsa mata kuma tana k'ara tuno mishi fargabar da Ummi ke ciki. Kawai sai ya had'eta da k'irjinshi ya ruggumeta da k'arfi kana ya fara magna cikin dakiya yace. "Madadin kiyi mishi addu'a sai kiyi mishi kuka? kin san halin da yake shiga duk sanda yaga hawaye a kwaranya a idanunki, meyasa rauninki yake yawaita, da can baya da juri na sanki to meyasa bazaki ruggumi k'addaraba, ki godewa Allah a cikin dukkan lamarinki." tunda yace mata kin san baya son kukanki ta gane Saifuddeen ne, to wani zafin ya wuce inda hawaye yake fargabarta da nitsuwarta duk sun had'u sun hargitse sun danne hawayenta, sai tayi wani azabebben murmushi da yafi kuka zafi cikin sanyi tace. "Alhamdulillahi ala kulli halin, ya Allah ka fini sanin waye Saifuddeen ya Allah ka fini sani adadin mutanen da ya zame musu uwa uba yaya k'ana, ya Allah ka fini sanin rauninshi dana mahaifiyarmu ya haiyyu ya k'aiyyum ya zirjalali wal ikram ya Allah ka bashi lfy ka d'aga kafad'un shi." da sauri Dr Adnan yace. "Amin Amin, Ameeen ya rabbil izzati." daga nan yayi ta bata baki da nuna mata ciwon baiyi tsanani ba. Amman duk da haka daren wannan ranar itama sam bata rumtsaba. Raihana kuwa har dare Allah baisa ta tuno da Affan ba domin tunda suka dawo data haura sama d'akin Saifuddeen kuka tayi tayi, sai bayan sallan isha da Amira 'yar Alhaji Kabiru ta dawo mata da shi itama haka ta kwana yiwa d'an uwanta addu'a. A can Abuja kuwa, tunda asuba matar ya Rabi'u Aunty Mami ta tasa yar aikinta gaba suka shiga kitchen, dan Ishaq ya gaya mata da sanyin safiya zasu koma asibitin. bayan ta gama komai ne ta d'auki na su Ishaq da yayanshi da Hayatudddeen ta kai musu bisa dinning table dake nan men parlour nasu, inda tunda suka dawo masallaci suna nan zaune suna tattauna matsalar inda shi Hayatuddeen yake cewa shi yafi son a fita woje da Hamma Saifuddeen nashi yaci gaba da cewa. "Ance Jermaine itace k'asar da tafi shahara da kwarewa ta fannin wannan ciwon, ni kam da zan samu mu fita dashi." ya k'arishe mgnar yana mai kallon Ishaq da yanayin neman izini. Cikin tausayawa Ya Rabi'u yace. "Ba matsala ! Hayatuddeen in sha Allah tun da Dr Aliyu yasa hannu kan lamarin so ko can Jermaine aka kaishi iya abinda yace zasu ce, kana nasan zaiyi duk abinda ya dace in kuma yaga fitar da shid'in nema maslaha to tabbas, nasan zai bada dama a fitar dashi, kuma zai shige mana gaba yadda komai zaizo da sauk'i. Yanzu ku matso muyi breakfast saimu hanzarta zuwa, tunda ya shaida mana kwana zai a asibitin kana da safe zai dubashi kafin ya tafi gida." cikin lumshe ido irin na marasa gani Ishaq ya d'an shafa kan Hayatuddeen tare da cewa. "Zo muje kaci abinci in sha Allah Saifuddeen zai samu lfy." haka dai sukayi ta bawa juna k'arfin guiwa. Ummi kuwa sam ta gaza samun sukuni, abinda ta sanine bazata iya cin abinciba, amman ganin yadda Mami ta matsa akan dole taci abinci yasa tace. "Bani tea kawai in sha." cikin jin dad'i Mami tace. "Yauwa Ummi gwara kici wani abu kafin ku tafi domin, bamu san yaushe zaku dawoba, kuma shima zama da yunwa cutane." amsar cup d'in tayi tare da cewa. "Sannu Mami Allah ya saka." Amin tace tare da mik'ewa ta fida dan ta bata wuri, tasan in tana nan ba sha zatayi zabida sabida poolaku irin na al'ummar Dukku. ita kam Ummi ji take tea d'in tamkar da mad'aci aka tafashi ba sugar ba. Haka dai ta d'an sha rabi nai, kana ta kimtsa ta fito dan Hayatuddeen ya kirata akan tazo su tafi, tare da Ya Rabi'u da Aunty Mamin suka tafi, ita Ummi da Aunty Mami suna motar ya Rabi'u shiko Hayatuddeen key d'in mota ya Rabi'u ya bashi kana suka taho shida Ishaq. Shi kuwa Ahmad Abban Farida kenan, yana gama kimtsawa ya kira Hayatuddeen cikin sa'a ya d'aga bayan sun gaisa ne yake cewa. "Hayatuddeen wanne asibiti kuke ne?." cikin sanyi yace. "Ya Ahmad kazo ne?." da sauri yace. "Eh nazo kuma ban san inda kukeba." meda hankalinshi yayi bisa tuk'in da yake kana yace. "Kana ina yanzu inzo in d'aukeka?." masauk'in da yake ya gaya mishi hakan yasa ya juya akalar motarshi ya nufi Royal Hotel, a harabar hotel d'in suka sameshi, ba tare da b'ata lokaci ba ya shiga kana suka juya suka tafi. Su Ummi kuwa suna isaya Ya Rabi'u ya nemi ganin Dr Aliyu nurses en suka ce mishi ya d'an jira nanda 20 minutes. dan yanzu yana woyane, haka yasa suka zauna a yar farfajiyar gaban office enshi, bayan kamar 15 minutes su Hayatuddeen ma suka iso tare da Ahmad nan

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148