Skip to content

Chapter 32

Chapter 32

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

shinkafa da miyar ganye wanda miyar asubane to da yake miyar da d'an yawa shiyasa ta tuk'a musu tuwo, a zatonta bazasu wani ciba amman kuma sai gashi sun cinye tas yau harda Saifuddeen da yake abinda yake sone Warisu ne ya d'anci kad'an. Bayan sun gama cine Ahmad ya firfito musu da d'inku nansu baki d'aya, sosai sukayi mmkin yadda ya gama d'inkunan cikin k'ank'anin lokaci kuma d'inkunan sunyi kyau sosai da salon tsarin d'inkunan wannan shekarun. Nan Saifuddeen ya bawa kowa nashi, duk sukayi godiya dama tuni Saminu ya kawo musu takalmansu da huluna Salisu kuma ya kawo musu ogogunansu. Daga nan duk sukayi sallama suka tafi sai Ahmad da yace yau nan zai kwana, to bayan su Mudassir sun tafine Bappa Ali da Aunty Nina ma sukazo yiwa Saifuddeen godiya nan sukaci gaba da hira, a nanne Saifuddeen yace dasu, Hayatuddeen zai rink'a zuwa wurin Ahmad ya rink'a koya mishi d'inki, to kuma duk sunyi na'am da hakan daga nan suka d'an tab'a hira sannan duk sukayi saida safe suka watse. Washe gari kamar kullum suna isa ya d'an shiga massalaci yayi baccin awa d'aya da rabi yana tashi yayi al'wala yayi walahanshi, yana fitowa kai tsaye layin da zai sadashi da kantin kori ya shiga, yana isa d'ab da kantin korin ya tsaya a bakin shagon Malam Habu mai saida mayukan shafa da turatuka powder da dai sauran kayan kolliya na mata, Sadiq na ganinshi cikin fara'a yace. "Barka da isowa Balarabe." murmushi yayi tare da mishi alamun bafulatani dai daga nan suka d'an gaggaisa da mutanen layin sannan ya isa dilansu na ledan yana zuwa aka bashi kamar kullum sannan ya fara zazzagayawa ya rabawa kowa. Koda ya gama sai ya d'auko omonshi nan yayi ta zagayawa sosai kuwa yau ya sayar koda ya gaji ya koma shagon Malam Habu ya zauna yana d'an hutawa dan yana son yaje gidansu Ishaq to ya kuma yanaga kada yaje ya samu basu isoba da wannan tunanin ya bari sai gobe yaje, cikin body language ya tambayi Malam Habu ko yasa inda gidan Baba Bella yake?." kai ya jujjuya alamun gsky bai saniba to amman sai ya bashi shawaran yaje ya tambayi Alhaji Aliyu dilansu na ledodin kenan dan yana kyautata zaton shi zai san unguwar da Dottijon yake, nan yake cewa Malam Habu ya mantane Alhaji Aliyu baya k'asar ya tafi umrah, to nan yace ya tambayi yan shagonshi wata k'il zasu sani, toh fa abu kamar da wasa ya tambayi duk mutanen da yake zaton zasu san gidan Dottijon nan baba Bello amman duk sai kowa yace ko unguwar da yakema basu saniba yayinda wasuma sai suke mmki da ce mishi ba yace kai jikanshi bane to ya za'ayi kai jikanshi baka san gidanshi ba sai mu. Shi kuwa Saifuddeen ribarshi na yau na omo dana leda harda riban omon jiya ya had'an kud'in 10k da nufin zai yiwa Baba bello ihsanin yayi hidiman salla, to kuma gashi ya rasa wanda yasan gidan, dole haka ya hak'ura sannan ya bawa malam Habu ajiyan wannan 10k d'in dan ya rigada yayi niyar wannan kud'in Dottijon zai bamawa. K'arfe biyar nayi Salisu yazo suka tafi Dukku. Washe gari kuwa ta kama ranar ne ishirin da tara ga watan Ramadan wonda ana zaton ganin watan salla yau ko gobe dan haka da zai fita tafiya gombe sai ya harhad'a duk sauran kud'ad'en da yake adanawa ya sasu a aljihu ya tafi dasu. To koda ya gama rarraba ledodinshi kamar kullun ya saro omonshi yayi ta yawatawa har aka k'arfe uku saura kwata bayan ya had'a ribarshi ya wuce ya maida omonshi daya rage, daga nan ya wuce shagon Alhaji Kabiru wanda ake saida duk wani kayan d'and'anon miya kama daga Magi, raico, onga gishiri kafi Mai, Manja, fulawa, madara, sugar, sufageti, macaroni, indomi. da dai sauransu suna bada sari suna saida kad'an-kad'an kuma suma shine ke saida musu ledodin da suke zubawa kostomominsu kaya in sunyi sayayya. Sun saba sosai da Alhaji Kabiru dan shima yanada d'anshi kurma shiyasa yake tsananin son Saifuddeen, yana isa bak'in k'aton shagon nasu ya zaro pepar da biro ya rubuta musu duk abinda yakeso, nan Alhaji Kabiru ya amsa da kanshi ya ware mishi duk abinda ya lissafa bayan ya gama sasu a leda cikin nitsuwarshi yace. "Masha Allah Saifuddeen Allah yasa Isma'il d'ina ya zama mai nagarta kamarka, kalli yanzu wasu manyan magidan tama basuyi azamar cefenen sallaba amman gashi kai tuni ka gama komai abinka." kai ya d'an sunkuyar tare da gyara hannun riganshi sannan ya d'ago kanshi tare da yin murmushi cikin girmamawa ya amshi ledan da yake mik'o mishi sannan ya bashi kud'inshi tare da mishi godiya da sallama sannan ya juya ya tafi. Layin masu yankan kaji yaje nanma ya sashi zabbinshi guda biyar ya bada kudi kana yace musu in sun gyarasu su sa mishi su cikin firij sai k'arfe shida da rabi zaizo ya amsa, dagana kuma ya sayi jan nama na dubu 3 sannan ya wuce layin masu tattasai, inda yaje ya sayi, Tattasan, attaruhu, tumatur, al'basa, kabeji, karas, green beans. Da dai sauransu, sai ya kuma sayi dankalin turawa kond'o d'aya, daga nan ya wuce shagon da yake saran pure water inda ya samu Rabi'u nan ya sayi katon d'in fanta da Coca-Cola sai rabin ledan molt sannan ya had'a duk su tattasai ya kai aka marked'a mishi sannan ya ware wasu tattasan da taruhu da al'basan kuma wanda ba'a marked'aba ko za'a buk'acesu hakan. Kana ya harhad'a duk abinda ya sayan a shagonsu Rabi'un dan yasan shi da masu nama suna kai har dare kuma dama ya gayawa Salisu yau sai anyi sallan isha zasu kama hanyar tafiya dukku, k'arfe uku da rabi dai-dai ya gama duk sayyarshi sannan ya nufi masallaci ganin anata haraman sallan la'asar, baya an idar da sallan ne ya kama hanyan gidansu Ishaq wanda shi kuma tun jiya yake zuba idon ganinshi. K'arfe hud'u saura mai machine ya sauk'eshi k'ofar gidansu Ishaq dake cikin tudun wadan nan layin fad'a, yana sauk'a ya nufi cikin gidan, tare da sallama a ranshi ya shiga. Mommy ya samu a tsakar gida mai aikinsu tana mata kitso, tana ganinshi ta fad'ad'a murmushinta tare da bud'a baki cikin d'aga sauti tace. "Wa alaikassalam lale marhabin da Saifudddeen Ishaq ina kake ga amininka ya iso." shi kuwa gefenta ya rusuna tare da gaita, shi kuwa Ishaq da Imaran da Mamansu kusan a tare suka fito, yana ganin ishaq ya mik'e ya nufi inda yake yayinda shi kuma ishaq k'amshi turaren Saifuddeen d'inne ke masa jagora, ruggume juna sukayi lokacin da suka had'u sai kuma ishaq ya sakeshi sannan ya ware hannunshi ya manna bisa fuskan Saifuddeen cikin raha yace . "Iye iyeh my friend watoma kai azumin nan k'ara maka kyau yayi ka ganka kuwa yadda kayi kyau." dariya sukayi baki d'aya dan ganin yadda Ishaq yakeyin abu kamar mai gani, shiko Saifuddeen wayar ishaq ya karb'a tare da rubuta mishi. "To kanari sarkin zance da wanne idon kaga kyan nawa?." da sauri ya kauce ganin Ishaq d'in zai kai mishi bugu shi kuwa Ishaq cikin fara'arshi yace. "To kai da wanne kunnen kaji abinda nace?." murmushi yayi tare da kuma rubuta mishi amsa

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148