Chapter 138
Chapter 138
yasa ta nufi d'akin a hankali ta shiga bakinta d'auke da sallama. sai kuma tayi turus a baki k'ofar ta tanya cikin tsananin kad'uwa da firgita, ido ta zubawa Maryam dake tsakiyar akwatunan ta bubbud'esu gaba d'aya tana nunawa Any Aisha kayan, Yayinda Mama kuwa da yayarta Ruda suke kan gado fuskokin nan nasu tamkar suyi ruwan jini kuma tuni sun barbaɗe ƙofar falon Mama da maganin da Ruda ta kawo wanda aka basu tabbacin in dai Zaleeha ta tsallakashi tofa bazata lamunci zaɓin mahaifin nataba zata tashi hankalin kowa har sai an janye batun auren. cikin sanyin murya Anty Aisha take cewa. "Allah ya sanya al'khairi yasa gidan zamanta kenan iya rai da mutuwa." Maryam ce tace Amin Amin. sai kuma suka juyo suka kalli Ruda dake cewa. "Tir da addu'arki Aisha bakinki ya sari guntun kashi, kifa kalli wannan zuk'ek'iyar budurwa ki fasalta zamanta da gurgu kuma kurma musaki mara amfani kice Allah yasa gidan zaman tane. Ke kuma Maryam da yake baki da hankalin da kishin yar uwarki harda wani cewa Amin." ita kam Zaleeha tamkar an dasa tane a wurin ta kasa tantance abinda kunnuwanta ke jiye mata daga bakin Maryam dake cewa. "Addu'a ita ta dace da Zaleeha tunda dai wannan abun yin Allah ne, ko ana so ko ba'a so in Allah yayi ita matar Saifuddeen ne dole taje gidanshi, kuma ke Mama kin san halin Baba malam me amfanin bad'i babu rai, yak'in da babu nasara ai gwara yin mubaya'a du du dufa auren nan saura sati d'aya ne rak." Da sauri Zaleeha tasa tafin hannunta ta dafe k'ahon zuciyarta dake gab da tarwatsewa, idanunta ta rumtse da azabar k'arfi kanta ta fara jujjuyawa tare da zamewa ta durk'usa gaban Mamansu murya a hargitse tace. "Bana sonshi, bazan zauna da shiba, wlh mutuwa zanyi in aka had'ani dashi please Mama kiyi wani abu a kai." Maryam ce ta d'an kalleta a tausashe dan tasan irin abinda Zaleeha keji a ranta tunda itama a dole aka had'ata da Ya Aminu amman gashi yanzu da tayi biyayya tabi umarnin iyayenta tana ganin ribar haka, duk da zafin zuciya irin na ya Aminu zama yake kamar bawa a gareta, baya son duk wani abinda zai sata zubda hawaye. shiyasa a hankali tace. "Zaleeha kiji tsoron Allah kiyi biyayya ga mahaifinmu zakiga ribar hakan kada ki bari rud'in duniya ya Kaiki ya baroki. Ku dena yakice Saifuddeen dan nakasarsa dan babu wanda yasan k'arshensa, kuma in baka mutuba to ba'a k'are maka halitta ba, shimafa bada larurarnan aka haifeshi ba, kaso 95 cikin 100 ba haihuwarsu ake da nakasaba a duniya suke samu. Kaso 5 ne na cikin 100 ake haifarsu da nakasa, because muma bamu da yak'inin a haka zamu k'are rayuwarmu." Cikin tsawa da masifa Mama tace. "Rufe min baki hegiya mara zuciya, mai mugun fata mu nan in sha Allah lfy lau zamu k'are rayuwarmu. Kuma wlh wlh muddin ina raye Zaleeha bazata zauna da wannan gurgunba. Dan ke kinada macecciyar zuciya sun tankwaraki kin zauna a dole to banda Zaleeha." Cikin sanyi Maryam tace. "Kiyi hak'uri Mama ki gafarceni in furucina ya sosa miki zuciya." ita kuwa Zaleeha mik'ewa tayi ganin sunk'i su sarara bare su saurareta, ficewa tayi daga gidan a guje. A Cikin gidan kuwa, Anty Aisha ce ta kalli yayun nata cikin kafiya da fad'in gsky tacewa Mama. "Da hankalinki da tunaninki kike biyewa zugar wacce kin san batayi imani da Allah da manzonsa ba, bare ta yarda da k'addara mai kyau ko sab'aninta." A zafafe Ruda tace. "Ke Rebeka ni kike gayawa haka?." cikin tsuke fuska da tsawa tace. "An gaya mikin! K'arya nayi ne, imanin gareki tunda har yanzu baki samu tsarkin zuciyaba, kina kafura, mara lissafi zata zauna tana bin zugarki, lallai ke yar uwata ce kuma yayata Amman baki da hurimin kirana da Rebeka call me Aisha in bazaki iya ki bari." A zafafe tace. "don't call me Rebeka again." Sai kuma ta juya ta kalli Maryam tace. "Maryam tashi mu tafi, ni dai ina bayan Baba Malam daga yau kuma zamu fara shirye-shiryen auren nan." A hankali Maryam ta maida akwatunan duk wurin zamansu, sannan ta mik'e tabi bayan Anty Shatu kamar yadda suke kiranta kenan... Mama kuwa da kafurar Yayarta Ruda, nan sukaci gaba da tubka da warwara, suna tubke yadda auren Zaleeha da Abdussalam, kana suna warware auren Saifuddeen. Ita kuwa Zaleeha tana fita kai tsaye (Jonapwd) ta nufa tuk'in takeyi tamkar wacce zata bar garin. tana shiga harabar wurin tayi parking, cikin sauri ta fito gaba d'aya ida nunta dishi-dishi suke mata, kai tsaye office d'in Ishaq ta kutsa kanta sam bata iya amsawa mutanen nata gaisuwar da suke mata. shi kuwa Ishaq tun tana babban parlour yajiyo mgnar Sani na mata sannu da zuwa so koda aka turo k'ofar office nashi aka shiga yasan itane. Tana ganinshi kawai sai rauni ya rufe masifarta dan iya tsawon zamanta da ishaq a matsayin yayanta Ahmad take kallonshi ishaq yanada mutunci a ida nunta gashi last time ta surfa musu rashin ɗa'a kuma daga nan yake fushi da ita, a hankali taja kujerar dake fuskantar wacce yake zaune a kai ta zauna. sunkuyowa tayi ta kifa kanta bisa glass table dake tsakiyarsu kawai sai ta saki wani irin mawuyacin kuka mai cike da rauni da tarin k'uncin rayuwa. cikin tsananin mmki Ishaq ya zubawa saitin inda yakejin kukan idanu tamkar yana ganinta. sai kuma yayi shiru kamar baya wurin yana jin sautin kukanta na ratsa kunnuwanshi. Kusan tsawon 10 minutes tana kuka, bai kulata ba, ita kuma bata bariba, har 20 minutes har ta zarta rabin awa tana kukan bil hak'k'i da gsky. daga jin kukan kasan daga cikin zuciyarta yake fitowa kukane mai tattare da k'una da tsoro, sosai Ishaq ya fara jin tausayinta na kamashi ai ko ba komai ita macece kuma mai rauni. cikin sanyin sauti yace. "Ya isa, ya isa haka Zaleeha kada ki cutar da kanki." jin haka sai kukanta ya k'aru cikin kukan murya a raunace tace. "Malam Ishaq bana sonshi, wlh bana sonshi, na tsaneshi, inada wanda nakeso wanda ya bada ranshi da lfyarshi domin kare mutun cina pleaseeee Ya Ishaq kace mishi ya janye batun aure a tsaka ninmu, wlh muddin akayi auren nan cikin mu biyu dole d'aya zai rasu." Sosai ya nitsu yana jin kala manta sai ya kuma ji alamun tazo tana durk'ushe a gabanshi a hankali tace. "Dan Allah Ya Ishaq ka zame min Garkuwa na mana a karo d'aya dai a rayuwa ta, dana rok'eka abu dan Allah dan annabi kaji tausayi na mana ka rabani dashi kar in rasa raina please ya Ishaq kada ka bari ayi min auren dole." Sai ta kuma kife kanta bisa d'aya kujerar taci gaba da kuka. Sosai raunin ishaq ya halarto kan zuciyarshi, me zai hana ya taimaketa, to amman bari yaji meyasa bata son Saifuddeen, a hankali yace. "To waye kike son?." murya a raunane tace. "Ban sanshi ba?." fuska cike da mmki yace. "Ina yake to me sunanshi?." A hankali tace. "Duk ban saniba sau d'aya muka tab'a had'uwa shiyasa a gidanmu ake cewa wai ba mutun bane al'janine." Da sauri yace. "Yes al'janine mana nima haka zance, tunda shi gaibune." kuka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148