Skip to content

Chapter 37

Chapter 37

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,206 words 0 views Progress saved
Download Book

suke komawa. Yana fitowa yayi al'wala yayi sallan magrib yana fitowa ya samu Salisu na jiranshi, daga nan bakin Al'kasim suka tsaya nan suka d'anci abinda ya sauwak'a sannan suka wuce Dukku. Bayan kwana uku da zuwan su Alhaji Sani wurin Alhaji kabiru suka kuma zuwa, kan su jaddada da mishi batun kadafa ya d'auki abun a shirme ya dai ce musu yana nan yana tabin wad'anda yake bin kud'in. Iya bukku kuwa ,tun randa suka koma ko mai sunan Saifuddeen taji an kira sai gabanta ya faɗi. A cewarta ba ita ba dukku har gaban abadan, dannan wannan kurman matashin daya zubda mata haƙora biyu a karonsu na forko. Tofa tabbas in antayi artabu dashi a karo na biyu kanta zai sare ya bata a tafin hannunta, Goggo Ummi kuwa da Bappan ta sunji daɗin hakan a ransu, kuma sunada niyar sake ziyartarsu. Yau tunda Saifuddeen ya gama raba ledanshi kana ya yawata da tallanshi har la'asar bayan anyi salla ne ya nufi gidansu Ishaq dan sunyi dashi zaije su Ahmad da Saminu da Mudassir ma duk sunyi dasu zasuje dan sun kwana biyu basu had'uba, Hud'u dai-dai duk suna had'e a d'akin Ishaq yayinda gari yayi duhu sabida tasowan hadari, Mama kuwa tuni tai ta musu hidima dan dama sun ce mata danbun zogale sukeso, nan suka zube suna hira sunaci, Ahmad ne ya kalli Saifuddeen da yayi shiru alamun nazari had'iye abincin bakinshi yayi sannan ya kalli Saifuddeen tare da cewa. "Saifuddeen kaci dambun mana." Kai ya jujjuya mishi alamun bazai cima, cikin kula yace mishi. "Meyasa bazaka ciba?." Mudassir ne ya d'auki ledan pure water ya b'ula kana yashanye fiye da rabi sannan ya kalli Ahmad tare da cewa. "Ka manna Saifuddeen da zab'en abinci ai baicin dambu." jin haka yasa Ishaq mik'ewa tare da cewa. "Yes haka nefa kaga ni nama mance bari inje in gayawa Mama tayi mishi d'anwake dan na lura yana son abincin mata." dariya sukayi baki d'aya sannan ya fita, Saminu kuwa gyatsa ya d'anyi tare da cewa. "Au ashe dama d'an wake cimar matane?." kai Saifuddeen ya jujjuya mishi alamun a a kam. fitan Ishaq ba jimawa sai gashi ya dawo nan sukaci gaba da hira. Bayan kamar awa d'aya da rabi sai ga Imran ya shigo da tire, kai tsaye gaban Saifuddeen ya ajiye, sannan ya juya ya fita, shi kuwa Saifuddeen tiren ya jawo wanda aka cika d'an madaidaicin pilet da d"anwake sai dafaffan kwai guda uku a sama sai mai da magi da yaji, nan ya fara ci sosai yaji dad'in d'anwaken, Mudassir ne ya kalleshi tare da cewa. "Oga ba tayine?." hararanshi ya d'anyi tare da nuna mishi kulan dambun cikin mishi alamun kunci nabanku. Ahmad kuma tab'e baki yayi tare da cewa. "Ahab barshi da d'anwake ko rabi nai bazai ciba zaice ya k'oshi, sai dai ka ganshi yana ture pilet d'in." ana cikin haka Allah ya sako iska mai sanyi wanda yake nuni da hadarin ya watse lokaci d'aya gari ya washe. Shi kuwa Saifuddeen baici rabinba ya ture pilet d'in kana ya mik'e ya shiga bathroom, nan sukayi ta mishi tsiya wai yana nan kamar kifi, wonka yayi yana fitowa ya bud'e durowan Ishaq ya canza kaya sannan ya kallesu tare da musu alamun shi zai tafi, sai ya kuma kamo hannun ishaq tare da mishi alamun ya tafi, nan suka mik'e duk suka fita daga nan duk suka salami juna. K'arfe 11:15 pm Saifuddeen ya mik'e tsaye tare da ninke sallayan da yayi sallan shafa'i da wutiri, a kanshi bakin katifarshi ya zauna tare da yin addu'a ya shafa a jikinshi sannan ya kwanta ta b'arin dama. Can misalin k'arfe biyu dai-dai ya farka bakinshi d'auke da addu'a, a hankali ya bud'e idanunshi yana mai tuno mafarkin da yayi, salati ya kumayi ya sanarwa mahaliccinshi, jingina yayi da jikin pillow sai ya kuma lumshe idanunshi tare da son nazartan mafarkin nashi, sai ya kumayi saurin bud'e idanun nashi dan ganin abin ya dawo mishi tamkar yana ganinshi a majigi, a hankali ya mik'e ya fito tsakar gidan nasu inda ya samu ashe anyi musu ruwan sama kamar da bakin gwarya, cikin nitsuwa ya wuce bandaki fitsarin da ya matseshi yayi sannan ya fito bakin barandan k'ofan d'akinshi ya tsuguna yayi al'wala sannan ya mik'e ya shiga d'akin kana yayi ta nafilfilinshi. Washe garin da rana irin rana tayi fed'e-fed'e d'innan lokacin gari ya d'anyi zafi sai inuwan gajimare kad'an-kad'an, sosai ya saida kayan sanyin koda ya gama kafa na uku, sai ya wuce shagon su Jabeer nan sukayi ta hira har aka kira salla bayan sunyi salla kuma sai ya wuce shagon Alhaji Kabiru yana isa ya samu yaran shagon duk sunata hidiman jera kayayyakinsu bisa dukkan alamu sarin da sukayi ne ya iso, shi kuwa Alhaji Kabiru yana cikin shagon bisa alamu lissafi yakeyi, ganin haka sai Saifuddeen ya tsallaka ya shiga ciki can kusa da shi ya zauna cikin body language ya gaida Alhaji Kabiru da tuni ya gama lissafin ya had'a takardun wuri d'aya, cikin mutuntaka da dattaku ya amsa gaisuwar Saifuddeen, sai ya kuma kalleshi ganin yana mishi alamun tambyar ina woyarshi, murmushi yayi tare da cewa. "Wayata gata a aljihuna." kai ya jinjina mishi kana ya mishi alamun ya fitar da ita zasuyi mgna, gane hakan ya sashi zaro woyar, daga nan ya suka fara mgna ta inbox nasu suna musanyan text messages, sosai Alhaji Kabiru ya nitsu yana kallon text d'in da Saifuddeen ya tura mishi inda yake cewa. "Assalamu alaikum, Alhaji ya gida ya kasuwa, Allah ya taimaka." sai ya rubuta mishi amsa da. "Wa alaikassalam lfy lau Saifuddeen, Amin Amin. Naga kamar muhimmiyar mgna kakeson muyi, kada ka damu ka d'aukeni kamar mahaifinka ni ina ina jinka tamkar Isma'il d'ina." Sosai Saifuddeen yaji dad'i mgnar hakan ya sashi murmusawa tare da rubuta mishi. "Ngd matuk'a Alhaji." sai ya kuma yi shiru bai kuma rubuta komaiba ya rasa ta ina zai faro zancen gane haka yasa Alhaji Kabiru dafa kafad'unshi cikin bashi k'arfin guiwa yace. "Ina jinka." shi kuwa rusunar da kai yayi tare da rubuta mishi. "Kayi hak'uri Alhaji ka gafarceni ranan asabar d'in da ya gabata, ka kirani na kawo maka ruwan sanyi, inda nazo na sameka da bak'i to nayi laifin fahimtar maganganunku, sai dai kuma naji ina sha'awar sanin kasuwancin da suke tallata maka, in akwai damar da nima zan iya sa hannuna a ciki nima zanyi." yana tura text d'in sai ya sunkuyar da kanshi, shi kuwa Alhaji Kabiru murmushi yayi bayan ya gama karantawa cikin kekyawan fahimta ya dafa kafad'un Saifuddeen wanda ya sashi d'ago kai ya zuba mishi ido alamun jin na bakinshi. Gyara zama yayi tare da zuba mishi idanu cikin sanyin sauti alamun yana son su sirranta zancen yace. "Me zai hana zaka iya mana, ai duk abinda mai ji zai iya na kasuwanci in sha Allah zaka iya, sai dai kuma fa wannan al'amarin da kamar wuya." da sauri Saifuddeen ya gyara zama tare da fuskantarshi yana mai kallon motsin bakinshi ta yadda zai fahimceshi da kyau shi kuwa Alhaji Kabiru cikin tsarkakan zuciya ya fara mishi bayanin kasuwancin. "Company Maggi ne suka kawo mana tallan Maggi a sirrance a matsayinmu na manyan dilolin maggi,

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148