Chapter 78
Chapter 78
tsananta ne jin tafin hannunshi bisa hab'arta yana share mata hawayen tare da jujjuya mata kai kana yana wani irin sihirtaccen murmushi mai cike da zallan tawakkali da yarda da k'addara, Hayateddeen kuwa kanshi ya kife bisa pillow da kan Hamma Saifunshi ke konce goshinshi ya manna da hab'ar d'an uwan nashi kuka yakeyi mai cin rai da cushe farin ciki murya na rawa yake cewa. "Dukkan jarrabobinmu sukan riskemu da tsananin zafi da tarin k'una, ko yaushe ciwo ko mutuwa basa zabi duk inda Allah ya aikosu nan suke zuwa, mutuwa ta yashe mana jigonmu, yayinda kowa ya yanke k'auna sai ubangiji ya sauk'ar da k'udurarnsa bisa d'an uwana da duniya ke ganin bama zai amfanin kanshi bama bare ya amfane mu, Hamma Saifuna ya karya zaton mutane da suke ganin nakasa kasawa ce, ya tashi ya tsaya kaida k'afa ya shiga rana dare zafi sanyi ya ratsa duhu da ruwa da iska na damuna dan tsaida hawayenmu ya zame mana Garkuwa kana bongo abin jingina jigonmu abin al'faharinmu." sai ya kuma taso ya kalli Hamman nashi da yaketa juya musu kai murya na rawa yace. "Wallahi! Wallahi!! Wallahi!!! da ana canza ciwo da na canzashi ya dawo kaina, da ciwo bazai kuma rab'ar d'an uwana ba da ina da dama da na tsare maka dukkan wata cutar da zata kai ga tab'aka bare ta nakasa mana kai." Ummi kam ta kasa cewa komai sai sunkuyar da kanta tayi k'asa tana zubda hawaye tare da ambaton Allah. Shiko Saifuddeen jawo Hayatuddeen yayi bisa k'irjinshi ya rink'a shafa kanshi cikin alamun lallashi kana ya d'auki woyarshi da d'aya hannun rubutu yayi mai yawa ya mik'a wayar ga Ummi. ba tare da ta kalleshi ba ta amshi woyar, sabida hawayen dake kwaranya a idanunta yasa take ganin rubutun bibbiyu d'ad'd'aya rumtse idonta tayi hawayen da suka cika mata idon suka zubo sannan ta fara ganin rubutun a dai-dai kana ta fara karanta abinda ya rubuta mata "Ni kam Saifuddeeen bani da wani ciwo da zai firgitani koya tayarmin da hankalin a duniya, kamar yadda ganin hawayen Ummi na da k'annena zai sani d'imuwa, zuciyata na k'untatuwa in naga hawayenki, Ya Nuruddeen ya bar komai a hannu na bisa ya k'inin zan hana idanunku zubda hawaye, ya Nuruddeen ya shaida min nakasa ba kasawa bace, ya gina min zuciyata da rayuwata ta yadda zan iya zame muku Garkuwa duk da nakasata, Ya Nuruddeen ya haram tawa hannuwana rik'e k'ok'on bara ya damk'a min Al'k'alami da da jarumta. Ummi ya zanyi da raina? sai yaushe zanyi nasarar tsaida hawayenki? Sai yaushe zan saku farin ciki, Ummi bani da baki dana fad'i miki irin k'unar da zuciyata keyi in naga zubar hawayenki bana jin k'unci a kan larurata sai naga hawayenki na zuba. Ummi kalli yadda Hayatuddeen ke kuka tamkar zai shid'e wannan ya nuna min gazawata ce kenan, ni nasan Ya Nuruddeen bai tab'a barina na zubda kwallaba, to ya akayi ni na kasa hanaku zubda naku hawaye ko dai nakasa tace sila? yanzu Ummi kema kuka kikeyi su Rahma Raihana Raliyya kuwa ya zasuyi, Kalli kunsa Ahmad ma kuka, kalli ishaq bawan Allah da baya ganima kukanku ya sashi kuka, kalli Dr da kanta kun sata zubda hawaye, shin Ummi kin mance imanin bawa baya cika har sai ya yarda da k'addararshi mai kyau ko akasin haka." tuni wani azabebben kuka ya kwabcewa Ummi wanda yasa ta kife mishi woyar gefenshi tare dasa hannunta tsakiyar kanshi ta shafa sumanshi har zuwa kan goshinsa sai kuma ta juya ta fita da sauri, domin tasan in yaga tana kuka zai birkice, Abban Farida kuwa, hannu yasa ya kamo Hayatuddeen suka fita. Yayinda tuni Dr Batulu kuwa tabi bayan Ummi, shi kuwa Saifuddeen hannu ya mik'o ya kamo na Ishaq kamar yadda suka saba, shi kuwa Ishaq murmushin k'arfin hali yayi still kuma hawaye na kwaranya a idanunshi murya a raunace yace. "Ya Rabi'u yace in gaidaka da jiki. Kana sak'on gskysuwa daga k'ungiyarmu sunayi maka fatan samun sauk'i." hannunsu ya k'ara hadewa tare da jijjigawa alamun ya gode. daga nan sukayi d'an hirarsu sannan Ishaq ya fito. Nan ya samu Dr Batulu da Abban Farida sunata lallashinsu. ganin lokacin salla ya kusa yasa suka, sallami Dr Batulu suka tafi ba tare da Dr Adnan ya fitoba. Shi kuwa Dr Adnan ya dad'e tare da Dr Aliyu yana mishi k'arin bayani, inda yace mai tunima an fara mishi alluran, sannan kada su damu zai rink'a taho mishi da abincin daya dace yaci, a nan asibitin Dr Adnan yayi sallan isha kana daga bisani suka shiga wurin Saifudddeen shida Dr Aliyu d'in. suna shiga suka samu, nurse biyu maza masu gyara mishi jiki kamar taimaka mishi yayi wonka da al'wala da da juyashi ya fuskanci Al'k'ibllah yayi niya yayi sallanshi a koncen. Suna shiga su kuma suka fita dan sun gama mishi shirin baccinsa, Yana ganin Dr Adnan yayi murmushi tare da lumshe ido kana ya bud'esu ya kalli Dr Aliyu dake zaune bisa welchair d'inshi, a hankali ya mik'o mishi hannu sukayi musabaha, cikin kula Dr Aliyu yace. "Ya jikin?." lips enshi ya motsa alamun da sauk'i kana ya jinjina kai, shi kuwa Dr Aliyu cikin tausayawa yace. "In sha Allah in an fiddaka zuwa India nanda wani d'an lokacin zaka fara tashi zaune da kanka." da sauri Dr Adnan yace. "Allah yasa." Amin Dr Aliyu yace kana ya duddubashi sannan suka d'an k'ara bashi k'arfin guiwa da sama mishi nutsuwa sannan suka fita, a bakin harabar wurin Dr Aliyu da Dr Adnan suka had'u da Nurse d'innan Amina, da sauri ta iso inda suke, cikin shigarsu ta nurses wanda sunyi mata cib a jikinta sai d'an k'aramin hijabi, hannunta na cikin haljihun gefe da gefen rigardata da iya karta guiwa, rusunawa ta d'anyi tare da cewa. "Sir barka da dare." "Barka dai Amina Usman Jada." murmushi tayi dan yadda ya kira cikekken sunanta, gaida Dr Adnan tayi kana tace. "Sir bari inje in bashi maganinshi, zan wuce gida." jim ya d'anyi kana yace. "To ba matsala amman dan Allah kiyi sammakon zuwa, kinga na damk'a amanar wannan aikin a hannunki, dan naga bafulatanine d'an uwanki." cikin girmamawa tace, "In sha Allah ba matsala zan taho da wuri". daga nan sukayi sallama ita tayi ciki su sukayi woje. A hankali ta tura k'ofar ta shiga bakinta d'auke da sallama, kasan cewar idonshi biyu yana rubutawa Ummi text ne yasa yaga shigowarta, baibi ta kantaba yaci gaba da sarrafa woyar tashi, ita kuwa gefenshi ta tsaya, tana harhad'a alluran da zatayi mishi, bayan ta gama ne ta d'an matsoshi, tare da d'an zuba mishi idanu, kallonshi takeyi tamkar tauraro, gashin girarshi ta zubawa idanu wanda suke tamkar an zanasu da gazal sunyi lub lub dasu kana hancinshi zuwat har baki lips inshi jazir sai shek'ek'i sukeyi, ido ta lumshe tare da cewa. "Matarka taji dad'i koda ranta a bace yake in taga kekyawan fuskarnan taka farin cike zai kauda bak'in cikin." lip's enshi ya d'an tsotsa ta ciki dan yana kallon motsin bakinta ta cikin fuskar woyarshi. So ya gane duk abinda tace. ita kuwa yatsunshi ta zurawa ido yadda yake sassarafa wayar tamkar shi ya halicceta, lips enshi ta kuma kalla kana tace. "Wannan labban
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148