Chapter 8
Chapter 8
yace. "Saifuddeen kasha ruwa zakaji sanyi a ranka." a hankali ya fara shan ruwan domin jin zuciyarshi yake tamkar ana soya mishi ita, ajiyan zuciya ya rink'a sauk'ewa akai akai kana hawayenshi suka tsagaita, Ya Nuruddeen d'inshi ne ya fad'o mishi a rai, tabbas da yana raye da bazai bari kukansu ya tsanantaba, wani numfashi yaja kana ya kalli Malamin nashi da yake ce mishi. "Tashi muje woje Saifuddeen muje ka tsaya a sallaci gawan mahaifinka, kayi mishi addu'a a madadin kukannan da kake mishi, ka sani dukkan tsanani yana tare da sauk'i in sha Allah muna zatawa d'an uwanka da mahaifinka rahama, kada kayi musu kuka domin su mutanene na gari musu imani da tawakkali basu da abakan musu bare na fada ko gaba, ka sani babu maraya sai rago, kuma nakasa ba kasawa bace. Kada kayi ta kuka domin kukanka shi zaisa yan uwanka kuka, kuma kukanku shi zaisa mahaifiyarku kuka har ta kai ga ta kamu da wata cutar ka daure ka jumre ka zama Garkuwarsu." Cikin tsanani rauni ya mik'e tare da yi mishi alama da yaji zai bari, daga nan sukaje suka sallaci gawar kana aka kaita makwancinta. Nan aka zauna zaman makoki. Yau akayi sadakan Uku, duk da haka Bappa Ali dasu Malam Ashiru da Baba Hamisu dasu Saifuddeen d'in suna zama dan akwai masu zuwa gaisuwa. Bayan sallan azahar ne duk suna zaune a gindin bishiyar limis dake harabar massalacin k'ofar gidan nasu, wasu maza su uku sukazo wanda kusan abokan Abban ne bayan sun gaisa ne d'aya daga cikinsu ya zurawa Saifuddeen idanu yana kallonshi ido cikin ido, shi kuwa Saifuddeen bai kauda idanshi bane dan ganin mutumin yana jujjuya kai alamun zaiyi mgn to sanin in ba kallon bakinshi yakeyi ba bazai gane abinda yake fad'anba shiyasa ya tsurawa mutumin ido, shi kuwa mutumin cikin jujjuya kai yace. "Allah sarki duniya mutuwa bata zabi, Allah bai barin wani dan wani yaji dad'i." sai ya kuma kalli su Bappa da Malam Ashiru da suke jinjina kai sannan ya meda hankalin shi ga Saifuddeen tare da cewa. "Da ana bawa mutuwa zab'i ai da an bata zab'i ta d'auke wannan nakasasshen ta bar Nuruddeen da shike kula da rayuwar k'annenshi." da sauri su Bappa Ali suka zaro ido tare da cewa. "Subahanallahi Mala Bala wannan wanne irin mugun furuci ne?." kai jinjina musu tare da jaddada musu cikin rashin iya mgna yace. "A ai gsky ne Malam Ashiru shi wannan dame zai amfani kanshi ma bare ya amfami wasu, yaron dashi da dutse bashi da banbanci ai su Rahma sun tagaira da mutuwa ta d'auke Nuruddeen ya bar musu mara amfani, ko su da kansu ai zasuce da mutuwar ta had'a uban nasu dashi wannan kurman ta yashe su ta bar musu Nuruddeen." cikin tsananin b'acin rai Malam Ashiru yace. "Kai tafi daga nan gaisuwa kazo ko cin zarafi?." Bappa Ali kuwa ya gaza cewa komai sai idanu ya zubawa Saifuddeen wanda ya rumtse idanunshi da tsananin k'arfi dan azabar b'acin ran kalaman da Mala Bala ya mishi gashi abokin mahaifinshi ne ba daman ya mishi wani abun. Sauran abokansu biyun da suka zo tare da Mala balanne suka mik'e cikin jin haushin kalamanshi suka sallami su bappa Ali tare da basu hak'uri sannan suka tafi. A daran wannan ranar Saifuddeen yayi kukanda bai tab'a yiba, inda yake ganin inama shi mutuwar ta d'auke ta bar Ya Nuruddeen d'inshi a ranar mutuwar ta dawo mishi sabuwa a ranshi, tausayinsu Rahma da Ummi ya hanashi sukuni ya zaiyi ya kula da rayuwarsu? haka dai kwanaki sukayi ta tafiya Randa akayi sadakan bakyai duk yan uwa suka watse gida ya rage su kadai. Hakan yasa suka zauna sukayi ta kuka. Washe gari da safe duk suna tsakiyar gidan time to time in Ummi ta kallesu sai tayi ta zubda hawaye. ganin haka duk sai jikinsu yayi sanyi, Rahma kam tuni kuka takeyi dan ita kam rayuwa ta mata zafi ba miji ba uba ba yayansu jigonsu, wanda suke ganin zai zama gatan nasu kuma gashi kurmane. jin kukan Rahma yasa Ummi tsananta kukanta, shi kuwa Saifuddeen idanu ya rumtse sabida ba abinda yafi tsana a duniya kamar yaga hawayen Umminshi, Raihana kuwa ruggume Hayatuddeen tayi tana kuka Raliyya kuwa su Faruq ta ruggume. Suna cikin haka sukaji sallama, cikin sauri Ummi ta d'ago kanta jin muryar Bappanta k'anin babanta da Goggonta, sai matar Bappan nata iya bukku muguwar mace, shiyasa Ummi take rayuwa tamkar bata da dangin Uba. da sauri ta taso ta nufi Goggonta, kan taburma suka zube nan raunin Ummi ya tashi ganin danginta kife kanta tayi kan cinyar Goggo Rabinta d'in ta saki wani marayan kuka. itama Goggo Rabi kukan takeyi dan tausayawa d'iyar yayanta. hakama Bappa idintan shima kukan yakeyi dan tausayawa rayuwar Ummi da yaranta, ita kuwa Iya Bukku sai wani mugun kallo na rashin imani take bin su Rahma dashi. Yayinda shi kuwa Saifuddeen ita ya zubawa idanu ganin mugun kallom data juyo tana yiwa Ummimshi. cikin tausayawa Goggo Rabi ta d'ago Ummi cikin sanyin murya tace. "Kiyi hak'uri Bisije dukkan tsanani yana tare da sauk'i, ki dena musu kuka Allah yana sane dake da marayunki." murya a disashe Ummi tace. "Goggo Rabi ya zanyi ina zan shiga a duniyar nan inji dad'i wa zai rik'e min yarayuna wazai tallafawa maraicina dana yarana da marayun jikokina?". sai ta kuma juyowa ta kalli Bappa idin nata cikin rawan murya tace. "Bappa ya zanyi wa zai zama gatanmu wa zai zama garkuwarmu, tunda shima bappan su Rahma ba wadata yakeda shiba, sana'ar me zanyi in rik'e yarana?." kafin Bappa idin yayi mgna tuni iya bukku ta cab'e mgnar da cewa. "Wannan kurman d'an naki mai kama da dutse shi baida amfanin komai ne?." sai ta kuma tsuke fuska dan bata son bappa idi yace zai d'aukesu su koma garinsu dasu, da sauri ta kauda kanta lokacin da ta kalli Saifuddeen sabida wani irin mugun kallo daya watsa mata. sai kuma ta tsuke fuska kana taci gaba da cewa. "In dai bazai amfanekiba ai sai ku jefar dashi ku huta da ciyar da mai zubin mutanen b'oye yaro tun yana k'arami ni tsoro yake bani dan wannan kyawun nashi ya zarta na mutanen mu. in kuma bazaki iyaba, tunda ke jakar 'ya'yace akan yaranki zaki mutu, to sai ki shiga cikin gari kije gidajen masu kud'i kina musu share-share da wanke-wanke da girki, suna baki dubu 6 a wata kullum kuma kina kwatsawa zugan yaran naki tuwo, nasan harda k'anzo zasuke baki." wani irin mugun kallo da tsana Saifuddeen yake cilla mata, domin tunda yake a duniya bai tab'a jin mgnar da tai mishi zafi kamar wannarba, kana bai taba jin mutun mai munanan kalamaiba kamar iya Bukku ba. Goggo Rabi kuwa kai ta rink'a jujjuyawa alamar batajin dad'in kalaman da matar yayan nata takewa d'iyar yayanta marigayi. Bappa idi kuwa sunkuyar da kanshi yayi dan yasan motsi kad'an zaiyi iya Bukku zata solleshi. Raihana ce ta share hawayenta tare da murgud'a mata baki kana tace. "Allah ya kiyaye Umminmu tayi ai katau a gidajen wasu, kuma Hamma Saifunmu ba k'aton banza bane kurwarshi kur sai dai kici kanki wlh yafi k'arfinki, har zakice mishi baida amfani to in sha Allah aniyarki
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148