Chapter 10
Chapter 10
zai biya miki buk'atunki ba gajiyawa bare gori. Ummi kiyi min addu'a ki sanya min al'barla in sha Allah ni d'innan zan cidaku in kuaa shayardaku in jinyaceku in suturtaku." ita kam Ummi ta kasa cewa komai sai ido ta zuba mishi domin yana tsugune sai rubutu yakeyi in inda yake ya cika kana sai yaja baya yanayi jikinshi na rawa cikin zubda hawaye taci gaba da bin rubutun da yakeyi tana karantawa. "Ummi rabuwarmu dasu shiyafi al'khairi domin muddin tana zuwa tana fad'i mana mugayen kalamai wata rana zan karya mata wuya, Ummi na karkiji tsoro in sha Allah k'annena bazasuyi karuwanciba ni kuma bazanyi baraba bare maula, kema bazakiyi aikatauba, ki kalleni ki gaya min dukkan matsalarki kiyi shawara dani ko k'annena kada ki gayawa kowa matsalarki ki sirranta matsalarki damu yaranki. Insha Allah zan fara neman sana'ar yi dan rik'eku ke dai ki samin al'barka." Rahma kam sai hawayenta take shartewa, su Raihana kuwa sai binshi suke suna karanta abinda yake rubutawan. Ita kuwa Ummi da sauri ta isa inda yake hannunta tasa tsakiyar kanshi cikin k'arfin hali tace. "Ya Allah kayiwa wannan bawa naka Saifuddeen al'barka ya Allah ka yalwata mishi samunshi hagu da dama rabbi ka al'barkaci duk abinda ya tab'a ya wahidun k'ahhar ka bud'a mishi k'ofofin samu gabas da yamma kudu da arewa. Ya Allah ka kauda asara da gafala da tab'ewa daga gareshi dashi dama dukkan yan uwa musulmai, ya rabbil izzati ka al'barkaci rayuwar Saifuddeen ka raya minshi ka shirya minshi ka bashi arzik'i mai al'barka wanda musulmai da musulunci zasu al'fahari dashi ya ka bud'a mishi k'ofofin samu ka yalwata arzik'inshi." kasan cewar tunda ta dafa kanshi ya d'ago kai ya kalleta shiyasa yake gane abinda take cewa, yana kallonta still yatsarshi na k'asa yana. Rubuta "Amin Amin Ameeen ya rabbil izzati". daga nan suka zauna tayi ta musu nasiha mai ratsa jiki. Bappa Ali kuwa da matarshi suna side d'insu sam basu san meya faruba. A daren ranar Saifuddeen yaje ya samu Bappa Ali da fefanshi da biro, nan yake neman izinin bappan nashi da kuma shawarshi cewa. A d'auki machine d'in Nuruddeen a bawa wani d'an mak'ocinsu Salisu wanda shima d'an acaba ne to dama na haya yake karba, to kuma an karb'e machine d'in wai mai ita zai saidata ya cikata ya sai sabuwa, ba musu bappa Ali ya yarda dan yasan ko ba komai balance d'in zai taimakesu, shi kuwa Saifudden gyara zamanshi yayi kana ya rubutawa bappan nashi cewa. Kullum da safe in Salisu zai tafi zai bishi su tafi tare, in yaje zai shiga cikin kasuwan Gombe zai nemi sa'ar da zaiyi." da fari Bappa Ali yak'i kasan cewar yanaga Saifuddeen d'in kurma ne, to amman da suka dunguzuma sukaje wurin Ummi sai ta kauda kai yadda Saifuddeen d'in bazai ga bakintaba tace. "Ba matsala Ali barshi yaje, in mun hanashi zaiga ko dan yanada nakasane, mukuma bamu son hakan to amman ai kasuwa saida jari, amman tunda yace a barshi yaje,to mu barshin in yaje yaga ba abinda zai ai zai bar zuwa, mu kuma bishi da addu'a Allah ya taimaka mishi." cikin sanyi bappa Ali yace. "To shake nan ba matsala Allah ya bashi sa'a." "Amin Amin." sukace baki d'aya. Daga part d'in Ummi woje suka fita, sukako yi sa'an samun Salisu a harabar matsallacin k'ofar gidan nasu. Nan bappa Ali ya mishi bayanin yadda sukayi, aiko dad'i kamar ya kashe Salisu, ya kuma yarda da shared'in zaike zuwa da Saifuddeen su kuma dawo tare. A take bappa Ali ya bashi Key d'in machine d'in. sannan ya wuce cikin sangayarsu ya fara ratsa tsakiyar d'aliban nasu. shi kuwa Saifuddeen gida ya koma ya sanarwa Ummi yadda sukayi, ita ko Ummi sai addu'a da samishi al'barka takeyi. A daren ranar Ummi da Rahma da Raihana da Bappa Ali kusan kwana sukayi sunayi mishi addu'ar samun madafa da sa'a. Shi kam Saifuddeen baiyi bacci a ranar bare ya rumtsa, Kwana yayi yana neman yardar Allah da sanya al'barkanshi ya bashi sa'a a cikin k'udurin da yayi. Washe gari da sanyin safiya Saifuddeen ya shirya bayan ya karya Salisu ya shigo yace su tafi. gaban Ummi ya tsuguna kanshi ta dafa tare da sa mishi al'barka. sannan su Rahma suka mishi addu'a baki d'ayansu kana suka fita suka tafi. Suna shiga Gombe Salisu ya wuce dashi k'aramar kasuwa, gab da San Hussen mall ya ajiyeshi, kamar yadda sukayi tun jiya da dare, bayan ya sauk'ane Salisu ya kalleshi tare da cewa. "Ana yin sallan magrib kazo ka tsaya a nan, dan zanzo in d'aukeka mu tafi in munyi sa'a bayan isha mun isa Dukku." cikin nuna alamar ya gane ya gyad'a mishi kai alamar toh. Salisu na ganin haka yaja machine inshi gaban wata yar budurwa data tsaidashi, lokaci d'aya suka shirya kud'in da zata bashi kana ta hau yaja ya tafi. Shi kuwa Saifuddeen juyowa yayi ya zubawa makeken wurin San Hussain d'in idanu a lokacin tun forkon-forkon bud'eshi kana wurin ba'a wani gyarashi sosaiba kamar yanzu ba, ajiyan zuciya yayi lokacin daya karanta sunan wurin, sai kuma ya k'auda kai kana yayi tafiya kad'an yazo dai-dai mashigar kasuwan, inda zai bulla ta babban layin na k'aramar kasuwan. ida nunshi ya lumshe kana ya bud'esu a hankali hannunshi ya had'e wuri d'aya kana ya fara karanto addu'o'i yayi kusan 16 minutes yana addu'o'in kana ya shafa a fuskarshi kasan cewar da d'an sanyin safiya ne wurin bai cika jama sosaiba kuma kowa sauri yake ya wuce ya isa wurin sana'arshi ya bud'e. bayan ya shafa addu'ar ne yayi bisimillah tare da d'ago k'afarshi ta dama ya shiga cikin kasuwan. Sannan ya mik'e gabanshi samb'et, yana tafiya a hankali. har yazo dai-dai wani babban shagon seye da sayarwa inda mata keta shiga da fita irin masu zuwar sassafen nan shagon kuma cike yake mak'il da atampopi, shadda, laces, material, voyels, su wagbari, gyalulluka. da dai sauransu, ido ya zubawa yaran shagon kowa na hidiman gabanshi. a hankali ya kalli saman shagon inda yaga an rubuta. Alhj Ishaq, murmushi yayi dan sunan mai shagon ya tuno mishi sunan abokinshi wanda kusan sau biyu kenan yana zuwa Dukku bayan Abba ya rasu. juyawa yayi d'aya sashin inda yaga wani k'aton shagon mai cike da gyalulluka da dogayen riguna, kana ya kalli d'aya sashin inda yaga k'aton shagon saida takalma, sai kuma kusa da inda yake shagon masu saida yadin hijabai ne da masu d'in kasu. shiru yayi sai ya kuma ci gaba da tafiya ganin ya b'ata kusan 30 minutes a wurin. A hankali yake taku har ya isa konan shagunan alhaji Yawale, shiga yayi nanma ya dad'e a tsaye sai kuma yayi baya ganin kusan irin kayayyakin wancan shagon ne daya wuce, kan babban layin ya dawo kana yaci gaba da tafiya, Dai-dai shagunan ba mishkila ya tsaya yana kallon yadda mutane ke cike a wurin mazansu da matansu yara da k'anana, ido ya d'an zubawa yaran shagon ganin kowa da abinda yake aunarwa kuma awu mai kyau irin awunda musulunci ya yarda dashi, sunan shagon ya kalla sai kuma yayi murmushi ganin sunan shagunan ba mishkila a ranshi yace. "Eh tabbas kam ba mishkila." A takaice dai a wanan ranar kam kusan aikin daya wuni
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148