Chapter 27
Chapter 27
alamun da kada ta sake biyoshi gwara tazo da rana. kai ta gyad'a mishi kana itama ta d'auki buta dan yin al'wala. Su kuwa suna gamawa suka nufi masallaci koda akayi insha akayi asham, suna fitowa suka shiga cikin gida ruwa suka sha sannan suka nufi hanyar fita dan tafiya wurin tabsir kamar kullum, har sunje bakin k'ofar fita Ummi tace. "Ahmad ka dawo da wurifa ku tafi kasan Raliyya yanzu zatayi bacci anan." juyawa yayi ya d'an kalli Raliyya cikin lumshe ido yace. "Shike nan in tayi bacci sai in goyata mu tafi gida abinmu." Warisu ne ya d'an bugeshi tare dayin k'asa da murya yace. "Kai a gaban Ummin kake mata wannan kallon kamar wani tsohon maye." ita kuwa Ummi cewa tai. "Asheko yau sai dai ku kwana anan." dariya sukayi kana suka fita, Raihana kuwa da sauri ta isa gaban Saminu da shi yanzu yake shan ruwan, cikin kauda kai ta mik'o mishi dabinon data ciko hannunta dashi guga bakwai ya tsinta kana yace. "Ya isa sai mun dawo." "To". tace dashi a sanyaye. Daga nan suka fita suka tafi masallacin fad'an Dukku. Ita kuwa Ummi ita da kanta ta shiga kitchen dan k'arisa aikin ferfesun zabbin data fara dan tasan yau Rahma ta gaji sosai, Raliyya kuwa k'ofan bappa Ali ta nufa wurin Aunty Nina, Raihana kuwa Attaruhu da al'basa ta d'auko tazo ta zauna gefen Rahma da keyiwa su Hayatuddeen homework shida Faruq, d'an k'aramin bilandan dake hannunta ta had'a kana ta yayyanka su ta jajjagasu sannan ta juye a roba mai marfi, Hayatuddeen kuma saura su kankana da ayaban da akaci ya d'an rage guntayen yake ci shifa a dole baya son cin abu mai nauyi a rayuwarshi. Ummi kuwa a kitchen tuni gidan ya cika da k'amshi dan zabbin sunji kayan had'i bayan ta gama zuba komai ne sai ta rufeshi bisa rushin yaci gaba da bararraka, tea ta kuma tafasawa ta d'ura a filas sannan ta fito gudan dubu ta bawa Hayatuddeen ya sayo musu sabon biredi, guda biyu, da sauri ya mik'e ya amshi kud'in yana zuwa ya kwaso biredi har guda hud'u. Yana shigowa ganinshi da ledodi har biyu yasa Rahma cewa. "Kai amman dai kai kam Hayatuddeen kaga ta kanka shin ba biyu aka aikeka ba?." da sauri Ummi tace. "Barshi ai bazai b'aciba nida nakeda samari yanzuma sun kusa dawowa." Raihana ce ta d'an harareshi kana tace. "Ai shiyasa yake komai na sakalci sabida yasan ba abinda za'ayi mishi ana tab'ashi kad'an Ummi da Hamma Saifuddeen zasuyi ta fad'a." sai ta kuma kalli Rahma daketa dariya tace. "Baga irinta nanba ai harda ke ake sakaltashi." dariya sukayi baki d'aya ganin yana yiwa Raihana gwalo, Raliyya kuma da yanzu ta shigo dungure k'enyashi tayi nan suka fara 'yar tsamarsu ta sak'o da sak'o. Daga bisani suka zauna suna hira cikin nitsuwa Raliyya ta gyara zamanta sannan ta fuskanci Ummi a hankali tace. "Ummi Ya Ahmad yamin d'inki kala biyu ya kuma sayamin takalmi da mayafi ya kuma yiwa Faruq da Adam ma, sai ya kuma yiwa Hayatuddeen dashi da Hamma Saifuddeen iri d'aya." cikin mamaki Ummi tace. "To shi Ahmad duk samunshi a kanku zai k'are ne, yayi ta zaman d'inki yana shan wuya ya kuma k'arar da samunshi a kanku ai wannan d'awainiya tayi yawa." cikin sanyi tace. "Wlh yana wahala kam Ummi kwana fa yakeyi yana d'inki, to amman kuma yana samun kud'i kinsan ya iya d'inki wasu ma daga bajoga da Ngalda duk shi suke kawowa d'inki gashi nan dukku duk ba wani tela daya fishi iya d'inki kinga fa duk zuriyar gidan sarki shi suke bawa d'inki tunda Ya Saminu ya hadasu dashi." sai ta kuma kalli Raihana tare da cewa. "Ai naga kema Ya Saminu ya bada aiyi miki dunkuna har kala uku, d'aya atampa ce d'aya kuma lace d'aya kuma shadda ce kedashi iri d'aya." shiru tayi kamar bataji ba dan kunya takeji bata son a gane Ya Saminun sonta yakeyi tunda yace mata sai ya gama karatunshi, dan yanzu yana level 2 a G.S.U kunsan duk abokan Saifuddeen sun wuceshi da shekaru biyu sanadin nakasar daya samu ta sashi tsagaitawa da karatunshi sai daga baya da Nurudden ya kawo shawarar ya fara zuwa gombe dashi yana kaishi makarantar kuramen. so shi Saminu shiyasa bai fiye zaman Dukku ba Salisu kuma kusan shine ya rik'e kakarshi inna shatu, Mudassir kuwa yanzu iyayensu hankalinsu na kan karatun Ya Adnan da yake karatun likita yakeyi shiyasa basu bi ta kan mudassir ba tukun tunda sunaga shi Adnan ya kusa gamawa ason ransu sai sun gama da Adnan sannan su dawo kan Mudassir. Warisu kuma yak'i ya nemi sana'a sai dogon buri to shima mudassir ai da yanada sana'a da duk sun d'auki nauyin karatunsu tunda su ba nauyin ciyar da wasu a kansu, to Saminu kuma da yake d'an gatane dan sarki kuma shalelenshi shiyasa tuni yayi nisa a karatunshi shiyasa ma yakeda damar yiwa Raihana hidima Ganin Raihana tayi kamar bata jisu bane yasa suka kauda zancen. Suna cikin haka suka jiyo hayaniyarsu Ahmad alamun sun dawo daga wurin tabsir d'in. Bayan sun shigo duk suka zauna bisa taburma sunata hirarsu ta abokai matasa, ganin Ahmad ya sake ko a jikinshi kamar ba har Shabewa zasu komaba ne yasa Ummi ce mishi. "Kaida zaku tafi kuma shine harda konciya kallifa har tara da kwata tayi." sai ta kuma juyo ta kalli Raliyya dake konce kanta bisa sallayar da aka ninnenke. "Ke maza tashi ku tafi." cikin alamun bacci tace to, Saifuddeen kuwa gyara zama yayi tare fuskantarsu cikin body language yace dasu. "Ba inda fa zaku tafi a daren nan ku bari gobe kwa tafi da safe." ido Ahmad ya zaro tare da cewa. "To uban wa zaimin d'inkunan da na yanka na ajiye da kake cemin mu kwana." hararan shi Saifuddeen yayi tare da rubuta mishi. "Uban uwarka ne zai maka d'inkin." dariya Ahmad yayi sosai yayinda Ummi taketa hararansu tare da ce musu. "Kada ku sake samin kawuna a shirmenku kuyi da iyayenku banda salihan iyayenmu kam da suka bar duniya da dadewa." cikin dariya Ahmad yace. "Yoh dama wa zaice iyayenshi ba salihaiba mu nan gani muke duk duniya ba salihai kamarku." shi dai Saifuddeen murmushi yayi had'i da shafa k'eyanshi da Ummi ta d'an dungura. kana sai ya kuma tsuke fuska sannan ya musu alamun, dolefa su Ahmad su kwana da shi kad'ai yazo kamar kullum da zasu rakashi so tunda ya taho da Raliyya kuma dole su kwana, ita kam Raliyya tuni ta b'ink'ire, shi kuwa Ahmad tsaki yaja tare da cewa. "Yaseen d'inku nanka sai bayan salla zan maka su, tunda dama gashi har yanzu baka kawosuba kuma kasan tun kafin azumi nake rufe karb'an d'inki amman da yake kai d'an gadarane da can da saya maka akeyi ma kullum wai sai ishirin da d'aya ga watan kake mik'o min dinkin ka kakuma samin naci dole in d'inka maka." Tab'e baki yayi tare da d'aga mishi girarshi duka biyu alamun dolenka ai, Warisu da su Salisu kuwa kanshi sukayi da cewa kadafa yayi musu al'k'awarin teloli. mik'ewa yayi ya nufi d'akin Saifuddeen tare da ce musu. "Kunga kada ku d'aura min jakar tsaba kaji su bini su tsatstsageni
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148