Skip to content

Chapter 118

Chapter 118

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,206 words 0 views Progress saved
Download Book

Zaleeha kamar ta mutu dan baƙin ciki, dan tasan abinda yasa Ya Ahmad ɗin nata yayi musu haka. Bilkeesu kuwa gyara kwanciyarta tayi tana kallon film d'in Sanam Teri Kasam da ake haskawa a tashar MBC Bollywood. Biyar dai-dai Ahmad ya shigo tare da ishaq. Kai tsaye parlour'n Saifuddeen suka nufa. zaune suka sameshi bisa wellchair ɗinshi, mai kalan golding ash. Wani irin murmushi Ahmad yayi tare da cewa. "Fatabarakallahu fi hasanil Kaliƙin, tsarki ya tabbata ga ubangijin sammai da ƙassai da yayi wannam kyakyawar halitta." Ishaq ne ya amshi zancen da cewa. "Masha Allah!." Murmushi Saifuddeen yayi wanda yake sanye da wata ɗanyen yadin getzner mai azabar kyau kalar dark green mai turuwa, irin dark mai shinng ɗinnan, yayinda aka zubawa kayan wani fitinennen ɗinkin half jumper and pencil trouser, daga wuyan rigar kuwa aka watsa mishi wani tattausan zaren surfani. yayinda ya murza wata kyakyawar hular damanga mai ratsin dark green akansa, daga ƙafansa kuwa wasu irin fitinannun toms mai kalan shaddarsa yasa, ƙiran company'n Gucci, me matuƙar tsada, still kuma zazzafan agogon company'n Gucci ne ke ɗaure atsintsiyar hannunsa wanda kuɗinsa kaɗai ya haurawa 80k, sai wayarshi ƙiran iphone 11 pro max daya zura cikin al'jihun gaban rigarshi, wanda abayyane ta saman al'jihun rigartasa, kake iya hango kyawawan camera's ɗinta guda uku dake jere reras, biyu asama ɗaya aƙasa. Yanayin shigar tasa ta matuƙar ƙara fito da farar fatarshi kai ka rantse da Allah cewa balarabe ne. Sajen nan nashi yayi wani lub-lub yayiwa fuskarsa ƙawanya sai sheƙi da ƙamshi yake, red colour lips ɗinshi sai shinning skeyi tamkar an shafa mishi mai a kansu. Shida kanshi ya sarrafa whellchair ɗinshi suka fito zuwa parlour. Ummi suka samu ita da Hayatuddeen azaune. gabanta suka tsaya cikin shirinsu na fita, murmushi tayi tare da godewa Allah daya bata wannan kyakkyawan ɗan, cikin gane batun da ya mata tace. "Allah ya kaiku lafiya, ya dawo daku lafiya, Allah ya baku nasara da sa'a kan abinda zakuje nema. Allah ya sadaku da al'khairin dake cikin tafiyar ya rabaku da sharrin dake tare da tafiyar." Da "Amin." Suka amsa baki ɗaya. Shi kam Saifuddeen wani sanyi da farinciki ne suka rufeshi sabida addu'o'inta gareshi. Shiko Hayatuddeen sai hotuna yaketa musu. Daga nan suka fita, har bakin gate Hayatuddeen ya rakasu, saida yaga sun fita sannan shima ya ɗauki machine ɗinsa ƙirar UD, ya nufi gidan Inna dan zaije wurin Zakariyya. Su Saifuddeen kuwa suna isa G.R.A. Ahmad ya rinƙa bin ƙwatancen da Baffa Ali yayi musu, suna isa bakin gate ɗin suka danna horn, sunyi biyu ana uku aka wangale musu makekem gate ɗin. Cikin nitsuwa Ahmad ya dai-daita parking ɗin motar, a hankali ya buɗe marfin motar ya fito cikin shigarsa ta al'farma, both ɗin motar ya buɗe tare da fiddo whellchair ɗin Saifuddeen, ta inda yake yazo, buɗe mishi murfin motar yayi kana ya gyara mishi keken. Yayinda tuni Ishaq kam ya fito. Yana gama gyara zamanshi kan whellchair ɗin sai ga Ahmad ya fito daga cikin gidan hannunshi riƙe da Unaisa ganinsu yasa cikin sauri ya nufi inda suke, ganin haka Ahmad Abban farida ma ya saki fuska kana ya nufi inda suke hannu suka bawa juna, Abban Farida ne ya fara magana, inda yace. "Assalamu alaikum." "Ameen wa alaikassalam, barkanku da zuwa." "Yauwa barka dai." Murmushi yayi tare cewa. "Ahmad yayan Zaleeha." cikin sakin fuska Abban Farida yace.. "Ni kuma Ahmad yayan Saifuddeeen." Murmushi sukayi baki d'aya, sannan suka taho inda su Ishaq ke tsaye, cikin tsananin son Saifuddeen ya sunkuyo ya bashi hannu sukayi musabaha, sannan suka gaisa da ishaq wanda shi sam bai gane cewa Ishaq makaho bane. Jagora yayi musu zuwa BQ inda dama yasa Lubna ta gyarashi fes tunda safe. Bayan sun zauna ne yace. "Bari naje na turo muku ita ko." cikin fara'a Abban Farida yace. "Ayi haka babban yaya." "Ai anyima." ya bashi amsa yana ɗan murmushi, kana yafice daga cikin babban falon BQ ɗin. Shiru sukayi kowa da abinda ke ransa, shi kuwa Saifuddeeen azkar yakeyi azuciyarsa cikin nutsuwa. Zahira yasa ta kai musu abin sha, kana ya nufi side ɗin Mama. A Parlour Mama ya samesu suna hira sama-sama dan kowacce da abinda takeyi. cikin tsare girar sama data ƙasa yace. "Ke Zaleeha tashi kije BQ kinyi baƙi." wani irin tsuke fuska tayi tare da yamutsa fuskar kana tace. "Baƙi kuma ya Ahmad." Ya Habune da yanzu ya fito ɗakin Mamansu yace. "Ke shi sa'anki ne yana miki Magana kina zaune, Zaleeha kifa kiyayeni nagafa baki da kunya ji kike kamar kin kamomu ko?." Da sauri ta jujjuya mishi kai tare da miƙewa jiki na tsuma domin ita dai Allah ya sani tana tsoron ya Habu da Ya Aminu mugayene na bugawa a mujalla yazu zasuce zasu kai mutun mari. "Maza ɗauko mayafinki ki ɓace mana daga nan." Da sauri ta nufi ɗakinta, shi kuwa ya fice daga falon. A zatonta yana nan shiyasa tayi maza ta fito tana mai yin rolling kanta da ɗan kwalin lafiyayyar Arabian gawn ɗin dake jikinta, ganin baya nanne ta zumbura baki tare da cewa. "Bilkisu muje ki rakani." Kai bilkisu ta jujjuya tare da cewa. "Tab ina cikin kallon wannan film ɗin ai babu inda zani, Rashida ta rakaki mana tunda ta gama zanen da takewa Aunty Lubna." Ahmad ɗinne ya kalli Rashida cikin bada umarni yace. "Rashida rakata ko." "To" tace tare da miƙewa ta ɗauki mayafinta. Suna gab da fita aka tafi talla, ganin haka Bilkeesu ta miƙe tare da cewa. "MBC Bollywood iyayen talla sun tafi, muje inga sahibin namu kafin in dawo sun gama tallarsu na tsiya." dariyan mugunta Rashida tayi, kana suka nufi BQ. Shi kuwa Ya Ahmad parlour'n Baba Malam ya nufa. Yana shiga ya samesu da Mamy da Mama da kuma Baba Malam ɗin. Gefen da littatafan addini wanda suke jere ya nufa yana mai cewa. "Baba Malam su Saifuddeen sun zofa." kai ya gyaɗa alamun to kana yace. "Ka tura mishi Zaleehan" "ai tama tafi." ya bashi amsa yana me zama kusa dashi, kai ya ɗan kwantar cikin sanyin sauti yace. "Naji tausayin Saifuddeen baba ya bani tausayi, mutun kyakkyawa matashi Allah ya jarabceshi da nakasa mai zafi, wlh Baba sai ka ganshi yama fi kyau a zahiri akan a hoto, in dai Zaleeha ta yarda dashi to haƙiƙa tayi dace da miji managarci, domin sam nakasarsa bata zame mishi kasawa ba, in ka ganshi kamar ba kurmaba, haka inba dan wellchair ɗin da yake zaune a kaiba bazaka taɓa cewa gurgu bane." Cikin mamaki Mama ta ƙara haɗe fuska tare da cewa. "Wai maganar me kukeyi hakane ban gane inda kuka dosaba, Gurgu kurma wurin waye yazo!?." Cikin isa da tsare fuska Baba Malam ya mata bayanin komai akan Saifuddeen ya ƙara da cewa. "Kuma ni yamin na yaba dashi muddin bata fidda waniba to niko zan aurawa Saifuddeen ita!." Kaƙa ƙara ƙaƙa wayyo Mama ina wuta ta faɗa ciki, don baƙin ciki da takaici, cikin tsananin hatsala da takaici tace. "Kurma! gurgu!? Yar tawa zaku haɗa baki kuce gurgu zaku aura mata? ai Wallahi bazata taɓa saɓuwa ba." Mamy ne tayi saurin cewa. "Kiyi mata fata da addu'an abinda yafi al'khairi zaifi akan mugun furuci baki san inda rabonta yakeba." Wani irin

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148