Skip to content

Chapter 139

Chapter 139

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

ta kuma sakewa, sai kuwa ta d'ago kanta jin yana cewa. "To meyasa baki son Saifuddeen?. " Rashin sani yafi dare duhu shiyasa Zaleeha tacewa Ishaq. "Nakasasshe nefa shi gurgune kurma ne ta yaya zan aureshi da lfyata gurgunefa ananfa kuke cemin irinsu basa aure." da sauri ta mik'e tsaye jiki na rawa ta koma gefe dan jin yadda ishaq ya buga table dake gabanshi tare da buga mata tsawa. "To sai me!? Shi nakasasshe ba mutun bane!? Ko shi nakasasshe baida ikon auran lafiyayyiyar mace!? To wlh Zaleeha kinyi ganganci wannan furucin naki, ni babu taimakonki da zanyi in sha Allah sai Saifuddeen ya aureki ko zaki mutu ne. Get out of my office!." Ya k'areshe mgnar da k'arfi tare da mik'ewa tsaye. wanda saida mutanen cikin babban parlour nan suka jiyosu. Ita kuwa Zaleeha cikin tafasan zuciya ta juya ta fita dan yanayinshi ya bata tsoro. Daga nan gidansu Rashida ta nufa, nan ta tasa Rashida a gaba tana kuka. Murmushi Rashida tayi tare da cewa. "Hmmmm Zaleeha kenan to ni mai zance miki, kin dai san bazan baki goyon bayan ki bijirewa iyayeki ba, in dai k'awancenmu na gsky ne, sannan da kiketa mai-maita shi nakasasshe ne ke kinada tabbacin a haka zaki k'arene. Zaleeha kifa farga ki dawo nitsuwarki kin gani ko wlh wlh dani Saifuddeen yace yana so na rantse miki da zatin Allah da hannu bibbiyu zan amshi soyayyarsa, Zaleeha inafa gaya miki kada kiyiwa kanki sakiyar da babu ruwa, kibi umarnin iyayemu ki samu rabauta duniya da k'iyama in zaki farga ki farga Ki daina wanna yarintar." Cikin tsananin takaici ta ture Rashida da tasa hannunta tana share mata hawayenta a hatsale tace. "Sai yau na gane asalinki Rashida, ke farin cikima kikeyi da wannan abun har dariya kikeyi ko?." Da sauri Rashida tace. "Tabbas farin ciki nakeyi abinda baki saniba, ko jiya muna tare da abokan ango, d'azuma na dawo daga can anguwar tasu federal law cos, layin Sabana hospital, wurin shagon Bash wani tela ne. Can suka kai kayayyakin d'inkinmu na biki naki da namu na k'awaye kuma komai yayi kyau, anjima kuma zasu zo batun shagulgulan da za'ayi." Cikin mmki da tarin takaici Zaleeha tace. "Shegiya yar iska a ina kika sansu?." Dariya Rashida tayi tare da cewa. "A wayar wani ɗan kawuna Jabeer naga hoton Saifuddeen sai yake cemin abokinshi, harma an kai lefe. to nan nake ce mishi ai mune k'awayen amarya, kinga daga nan komai yazo da sauk'i mu yanzu shirin bikin mukeyi babu kama hannun yaro. nice nan na kaiwa telan kayanki yadda zai d'inka komai dai-dai dake." bazata fa juri jin tatsuniyar Rashida da ɗan kawunta Jabeer da sauran abokan Saifuddeen ba don haka ta zari car key d'inta ta bar gidan. Ita ko Rashida murmushi tayi tare da cewa. "Ayyah Zaleeha zuk'ar zuciya da rud'in shaid'an na d'awainiya da ke sun hanaki ganin nagartan Saifuddeen. Fatana Allah ya sanya al'khairi a aurenku." Ishaq kuwa Zaleeha na fita ya biyo bayanta ranshi a matuk'ar b'ace, parking lot ya nufa ganin haka Ado drivarnshi ya biyu bayanshi bud'e mishi marfin motar yayi. Bayan ya shiga ya maida marfin ya rufe, sannan ya shiga yaja motar suka fita, suna hawa kan titin da kyau Ado ya juyo ya kalli uban gidan nashi cikin girmamawa yace. "Ina zamu je?." A takaice yace. "Gidan Saufuddeen." A parlour'n Ummi ya samu Saifuddeen shi kad'ai, kamar babu kowa a gidan. bayan sun gaisa ne da salon yadda suke mgna, Ishaq ya rubutawa Saifuddeen duk yadda sukayi da Zaleeha yanzu, yana gama karanta text d'in ya gyara zamanshi kana ya fuskanci abokin nashi cikin lumshe ido yayi wani tattausan murmushi tare da rubuta mishi. "Cool down my friend. kada ka damu da duk abinda zatayi." cikin jin haushi Ishaq fuskaci abokin nashi da kyau kana yace. "Saifuddeen ka hak'ura da Zaleeha mana tunda ba ita kad'ai bace d'iya mace, ita mafa macece kamar kowa ya za'ayi wasu na binka kai kana binta tana ci maka zarafi, na gaji Ka rabu da yarinyar nan, yarinyar da ikirari zata mutu in ka aureta kayi zuciya ka barta mana." A hankali Ummi ta zame ta zauna a kujerar da Saifuddeen ya baiwa baya, ishaq kuma ba ganinta zaiba. Gaba d'aya jikinta rawa yakeyi. Tsoronto d'aya kada k'iyayya tasa Zaleeha ta cutar mata da d'anta, ya zatayi in wani abu ya kuma samun Saifuddeen d'inta d'a mafi soyuwa a zuciyarta d'an da yake k'arar da lokutanshi wurin sama mata farin ciki da kare martabarsu. tuni hawaye na zirya a kumatunta dan tana tausayawa zuciyar d'an nata da Allah ya jarbaceshi da son matar da bata sonshi. Shi kuwa Saifuddeen kanshi ya jujjuya kana ya fara rubutawa ishaq mgna kamar haka. "Uhmmm Ishaq ai duk cikekken masoyi zai jure karan tsana. Zai jure kai kawo da zirga-zirga ako ina. Kuma bazai nufi masoyinshi da hatsala ba. Kuma ai ba'a son fushi a so sai dai hak'uri da juriya domin yin fushi a so alamun rashin nasara ne, in sha Allah dole ne fa sai Zaleeha ta shigo gidane dolen-dolenta sai taga aikin ginennen tab'on nan da tace sai na shayar da ita ruwan mmki, barni da ita zata gane kurenta!." cikin mmki Ummi ta zuba musu ido ganin sun tafa kuma ishaq ya saki wani irin shak'iyin dariya. "Saifuddeen kenan ya iya sarrafa harshe gashi daga fushi yasa ishaq dariya ko meye ya rubuta mishi sai Allah." Ummi Ke fad'i a ranta lokacin data mik'e ta nufi bedroom nata dan bata son Saifuddeen ya gane taji zancensu. Ita kuwa Zaleeha daga gidansu Rashida gidan Hajja inna nufa, tana shiga kawai ta tasa hajja inna a gaba ta bud'e wani sabon shafin kuka. Zakariyya ne dake gugun kayanshi dana Ziyada ya ajiye dutsen gugan tare da cewa. "To yau kuma me aka miki?." cikin kuka take cewa hajja inna. "Wallahi bana sonshi dan Allah ki cewa Baba malam yayi hak'uri kada ya min auren dole." shiru tayi jin hajja Inna ta ja wani dogon tsaki, kana ta b'alli tsallin goro ta afa a bakinta tare da taunashi, kai ta karkace tare da cewa. "To me ruwana a ciki, aure ne dai dole fa sai an aurar dake, na gaji da zamanki a gidan d'ana." Dariya sosai Zakariyya da Ziyada keyi sabida abin na hajja Inna ba mutunci. suna cikin dariyar suka jiyo muryar Hayatuddeen da sauri Zakariyya ya tarbeshi cikin murna suka ruggume juna irin yar ruggumarnan ta gefe. kana suka zauna bisa 2 sitter. Bayan sun gaisa da Hajja Inna ne Ziyada ta gaida Hayatuddeen cikin mmki Hayatuddeen yake tambayar meyasa Zaleeha kuka, Zakariyya ne yayi dariya tare da cewa. "Wai kuka take dan za'a mata aure." Dariyar shak'iyanci sukayi mata cikin dariyar Hayatuddeen yace. "Ato yarinya da kin san kina tsoron auren mai yasa zakisa gaye ya turo iyayenshi." Ziyada ce ta d'an kalleshi cikin yanayin d'an sabonta dashi tace. "Ya Hayatuddeen ai bata son mijin ne shiyasa take kuka auren dole za'ayi mata." da sauri ya matso kusa da Zaleeha wacce keta kuka hajja Inna kuwa nata aikin auna mata harara, cikin sanyi yace. "Allah sarki Adda Zalee gsky ba'ayi miki adalciba a dai wannan zamanin mace kekyawa big girl kamarki ace an miki auren

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148