Skip to content

Chapter 90

Chapter 90

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

tayi nisa acikin duniyar tunani. Ummi kuwa jin sauƙan hannu akan kafaɗanta ne yasanyata ɗagowa da sauri ta kalli wanda ya dafatan, da fuska Raliya tayi arba wacce ta marairaice tuni idanunta sun tara k'walla. A hankali ta kuma juya ganinta zuwaga Rahma wacce ta fara mgna cike da sanyin murya haɗi da tausayawa tace. "Dan Allah Ummi kidaina sa kanki adamuwa, Ummi idan kika kasance acikin damuwa akullum natabbata Saifuddeen idan yasani bazai taɓa yafewa kansa ba, Ummi kinfi kowa sanin Saifuddeen sam bayason damuwarki, dan Allah Ummi kidaina sanya kanki adamuwa Saifuddeen addu'a yake nema daga gareki damu baki d'aya , sannan Ummi kada kimanta addu'an uwa yana da matuƙar tasiri akan ƴaƴa, please ki tausaya mana ki dage da yi mishi addu'a!" Wani irin dogon Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da ɗan rausayar da kanta gefe tana mai son maida hawayenta amman ina ta gaza tuni sun zubo mata bisa k'unshinta, haƙiƙa shiga damuwa yazame mata dole, tunda ɗanta mafi soyuwa agareta yana cikin wani irin mawuyacin yanayi a hankali tace. "Ina yimasa addu'a akullum akuma ko yaushe Rahma, sannan nakasa ɓoye damuwata akansa, ke uwace Rahma kinsan irin tsananin so da kuma ƙaunar dake tsakanin ɗa da uwa, wannan ƙaunar fiye da itace ke tsakanina da Saifuddeen, kuma kisani ko ban nuna damuwata afili ba to tana nan kwance acikin zuciyata tana cina!". ta ƙare maganar murya araunane. Hawaye ne suka cika idanun Raliya har suna kwaranyowa kan fuskarta yayinda itama Rahma ida nunta suka cicciko da hawaye, tabbas idan harsu da suke ƙannansa suna tsananin jin ciwonsa ajikinsu, sannan kuma suna tsananin tausaya masa, basu da wani fata daya wuce samun sauƙinsa, to ya Ummi da take mahaifiyarsa zataji? ƙoƙarin maida hawayen da suka cika idanunta tasomayi tare da sadda kanta ƙasa murya asanyaye tace. "Kiyi haƙuri Ummi In sha Allah Saifuddeen zai samu lafiya, zai warke yazama cikakken mai lafiya, Saifuddeen d'inmu shine jigo kuma farin cikin mu, In sha Allah ko dan wannan Allah zai dubemu ya bashi lafiya, don bamu kaɗai keda buƙatarsa ba mutane dayawa daga waje suna da buƙatarsa!". Murmushi Ummi tayi tare da cewa. "Allah Yasa!". Da "Ameen". Raliya ta amsa kana ta miƙe ta wuce ɗaki don duba Adam yaron Adda Rahma dake bacci koya tashi. k'arfe biyar dai-dai na yamma Zaleeha ta shigo cikin gidan radio vision FM gombe. Driving takeyi cikin tsananin nitsuwa a hankali take tafiya, yayinda take sa hannunta tana goge sirarun hawayen dake zubo mata time to time. parking tayi kana ta fito kai tsaye d'akin watsa shirye-shiryen su ta nufa, a bakin k'ofa tayi cikibis da Raveel wanda ya gama gabatar da shirinsa kenan ya fito da nufin zai kirata domin tazo ta gabatar da program d'inta. Murmushi yayi tare cewa. "Yar halas kink'i ambato yanzu nake kiranki a raina." sam hankalinta da nitsuwarta basa jikinta bare ta kulashi ratsawa gefenshi tayi a bakin k'ofar shiga ta cire takalmanta masu d'an karen tsini, kana ta zura silipas dake wurin sannan ta kutsa kai cikin d'akin. Shi kuwa Raveel jingina yayi da jikin gini ya zuba mata idanu yana kallonta ko k'ebta idonshi bayayi koda ta shiga ta meda k'ofar ta rufe sai ya lik'a idanunshi kan takalmanta. Ita kuwa Zaleeha tana shiga cikin d'akin watsa shirye-shiryen nasu wani azabebben bege da shauk'in son ganin fuskar da ta tab'a gani sau d'aya ya d'arsun mata a rai. A hankalin ta zauna kan kujerar zaman nasu, Kana ta ɗauki wannan ɗan abu da suke sawa a kai ta saka wanda yake isa har zuwa kan kunnensu ta jawo ta sank'ala. Ji tayi zuciyarta na sarrafa gangar jikinta, madadin ta gabatar da program nata mai taken Babu nakasshe sai rago, kawai sai ta tsinci kanta dafuskantar na'urar tasu da kyau tare da zab'o wak'ar da take jijjiga sirrin zuciyarta. can cikin gidan Radio kuwa cikin mmki managernsu ya kasa kunne a na'urorinsu na tantance abinda suke watsa jin sautin sassanyar wak'ar da Zaleeha ta sake, dan ya hango shiganta, da sauri ya kalli agogon dake fuskar wayarshi ganin ai lokacin gabatar da shirinta har ya shiga da 3 minute. Da sauri ya jingina jikin kujerar jin ta d'an rage sautin wak'ar. Yayinda mutanen cikin garin gombe da kewaye ke jinta dan shirinta yanada matuk'ar farin jini, musamman a wurin nakasassu, wanda yanzu hakama duk inda nakasasshe yake yana jinta sanin lokacin nasune. A hankali take jin sautin wak'ar da tasa yana ratsa mata jiki da jini har zuwa cikin zuciyarta a hankali ta bud'e bakinta ta fara bin wak'ar. Yayinda akejin muryarta na gaurayewa da muryar mawak'an dan ta rage sautin hakan yasa abin ya had'e yake bada wani sok'o mai armashi wanda da zaran kajita kasan wani takewa baitukan, lumshe ido tayi tare da bin sautin waƙar a hankali take cewa. "Soyayyar dake raina bazan sauya ra'ayi ba." sai kuma ta bud'esu tare daci gaba da cewa. "Nayi lullubi kamar na ango da amarya." sai kuma ta d'an d'aga sautinta kad'an taci gaba da rere wak'ar. "So yanada dad'eeeee maso dashen wani ya shiga haushi." sai ta kuma d'an k'ara volume na radio kana taci gaba bin waƙar. "Soyayya ta zahiri ba'ayi mata gudun barewa." sai kuma wani sassanyan shesshek'a ya danne mata harshenta wanda kowa yaji salon yadda muryarta ke fita zai iya gane tana kuka da zubda hawaye take bin wak'ar cikin tsananin tausasa lafazi take cewa. "In nayi rashin sautinka zan fad'a k'inshi ruwa. Idan har na barka aban sona bani da kowa. Dana ganka sai na wadatu da k'oshi bani yunwa. Duba ka gani tsuntsun k'auna ya zana barewa. Girgije samani tai lub-lub, lif tana zubar ruwa. Ga itatuwa koraye d'orowa da sanwa." sai kuma ta lumshe idanunta hayenta suka samu daman zubowa sannan taci gaba cewa. "Munshiga ginin sha'awa ga iska tana kad'awa. Da k'auna tabi jiki an komawa wa da k'anwa. a hankali ta lumshe idanunta yayinda hawayenta sukaci gaba da kwaranyowa, tana ganin wayarta nata kawo haske alamun ana kiranta amman bata da tunanin d'agawa, murya na rawa taci gaba da bin baitukan wak'ar a hankali take cewa. "Jikina yana jurar rab'ar wata soyayya. sai kuma ta d'an d'aga murya da ɗan ƙarfi kana tace. *"Nayi adanin soyayyata bani baiwa kowa!* Barewa batayi gudu d'anta ya rarrafaba, *Soyayyar dake raina bazan mata kishiya ba.* sai kuma ta lumshe ida nunta kana ta buɗi baki a hankali ta taci gaba da raira wasu baitukan da yafi kama da amsa take bawa ƴan Nakasa ba kasawa bace fans 2, murya a tausashe take cewa. *Mai sukar masoya bai san sirrin zuciya ba.* _Idan na rasata jiki bazai daina bariba_ *baniwa masoyi rowar tattausan lafaziba.* _K'auna ke gushe haushi so bazai canja wuriba So in yayi kewar gani aso bazai tsayaba."_ Tana ganin ana danna mata danja alamun akwai matsala amman bata kulaba, saima ta k'ara d'aga muryarta ta gaurayeta da muryar mawak'a har nata yana d'an d'ara na radio take cewa. *"Bani bada rancen k'auna bazanyi aroba!.* *Na dad'e ina rarrafe cikin masu soyayya!.* *Gashi nayi fincinkawau misalin gudun barewa!.* Hakafa tayi ta sakin wak'ok'i masu jijjiga zuk'atan masoya wanda duk yaji yasan abin daga cikin zuciyarta ne. Koda akazo dan a shiga a ankarar da ita sai

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148