Skip to content

Chapter 117

Chapter 117

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,209 words 0 views Progress saved
Download Book

mai taken. "So makaho ne, kamar walƙiya ya kamani, gashi na zautu al'umma sunata nunani!." Sai kuma ta yi magana a hankali, inda tace. "Da fatan dai kuna jin daɗin waɗan nan zafafan waƙoƙin da muke kawo muku daga tasharmu ta Vission FM. Ku gyara zama domin jin waƙarmu ta ƙarshe sakamakon ganin lokaci na hararanmu. Sai ta kuma saki wata zazzafar waƙa mai tsuma zuciya, inda jarumar ciki ke cewa. "Zo muyi zance masoyi na kajiya." Sai ta kuma sai-sai-ta waƙar tare da dai-dai-ta muryarta data waƙar tana bin baitin. "Karda ka kauce, kasa ai mini dariya. Saida na tace na zaɓo ka guda ɗaya, babu irinka aduk faɗin duniya." Sosai akejin muryarta na tafiya da sautin waƙar. Dai-dai lokacin kuma Baba malam da Ya Ahmad da Aminu, suna gidan Inna wacce ya samu tana jin radio. Cikin kaɗa kai tace mishi. "Ka jiko Bashiru ka haifi zabiya mawaƙiya, Kaji da kunnen ka ko, Yanzu aka gama gabatar da shirinka na masu imani, Kajita ko ita kuma amara zabiya kantalla mai son kiɗe-kiɗe da raye-raye kamar jikar dujjal." Shiru baba malam yayi cikin jin kiɗan da Zaleeha ta ƙure ta haɗe da muryarta yana hawa mishi kai. Kai ya jujjuya dai-dai lokacin da take bin waƙar inda ake cewa. "Kai d'aya gaiyya mazaje kubi baya. Babu irinka na duba duk nahiya!." Cikin takaici Ahmad yasa hannu ya kashe radio'n, dan ya lura ran mahaifin nasu ya ɓaci sosai da sosai, shi kuma sam baya ƙaunar duk abinda zai ɓata mishi rai ko ya taɓa ƙimarshi. Ita kuwa Zaleeha cikin Shauƙi ta gama gabatar da shirinta kana ta fito. A bakin ƙofa suka haɗu da Bilkeesu mai gado, dan zata shiga gabatar da shirin labaran duniya. Cikin kula tace. "Kadafa ki manta Dukku, gobe da yamma zamuzo gidanku nida Rashida zamuje gidan Adama ta haihu muyi mata barka." Kai ta jinjina tare da cewa. "Ba matsala sai kunzo dama gobe ba inda zanje." Daga nan sukayi sallama, a bakin motarta ta samu Raveel dariya ya mata tare da cewa. "Gani nazo muyi zance kar ai miki dariya, ni d'aya gaiya na isheki a duniya, dukka buƙatunki zanmiki ba inkiya." Murmushi tayi dan dama ai Raveel natane yanada abin dariya dasa mutun Shauƙi. Motarta ta shiga tare da cewa. "Kafi kyau a hakanka ka zauna matsayin abokina." Murmushi yayi tare da rufe mata k'ofar motar. Kai tsaye gidan Addanta Maryam ta biya dan tace mata, Yau awaran couscous takeso tayi mata. A dinning table suka zauna tana cin awaran da aka soya da ƙwai. Sai miyan tarugu damn albasa da dusan kifi. Cikin kula Maryam tace. "Kina addu'o'in da na baki ko?." Kai ta kaɗa mata tare da cewa. "Inayi Addana inata rok'on Allah ya baiyana minshi ya kawo minshi gareni in har shidin al'kairi ne a gareni." Cikin sanyinta da haƙuri tace. "Yauwa yar uwata, ki kuma rage jin kiɗe-kiɗe ki yawaita jin karatun Al'Qur'ani. Ƙinga inma aljanine kamar yadda mama ke faɗi zai rabu da ke." Kunun ayan dake gefenta ta kurɓa tare da cewa. "Mutun nema my Adda na, ina sonshi, ina son abuna." Murmushi maryam tayi kana tace. "Allah ya tabbatar miki da al'khairi!." "Amin Amin." Tace tare da miƙewa, ta ɗauki kular da Maryam ɗin ta cika da awaran tace a kaiwa Aunty Lubna da ya Ahmad. cikin kula Maryam tace. "Ki tsaya kiyi salla mana." Kai ta jujjuya tare da rataya hand bag ɗinta kana tace. "Kin san baba malam baya son in kaiwa dare a waje." Kai ta gyaɗa mata kana ta rakata har wojen motarta. Bayan anyi sallan ishane, Ya Habu ya shigo falon Mama inda ya samu Zaleeha da Zahira da Aunty Lubna suna hira, cikin yanayinshi na rashin sakin fuska dan shi ya gadi rashin fara'ar Mama amman shi yanada mutunci fuska a haɗe yace. "Ke Zaleeha kije Baba malam na ƙira." Da sauri ta dafe ƙirjinta tare da cewa. "Ya Habu meya faru?." "In kinje ai zakiji." ya bata amsa ataƙaice, jin hakane yasanya ta miƙe da sauri tare da zumbula hijabin sallanta, wanda yake har ƙasa ta nufi parlour'n Baba malam ɗin. A bakin ƙofar parlour'n tayi kiciɓis da ya Ahmad, cikin sauri ta kamo hannunshi tare da cewa. "Please ya Ahmad muje ka rakani dan Allah!." Murmushi yayi sannan yace. "To muje." Shiru sukayi baki ɗayansu a gaban mahaifin nasu, yayinda Aminu ke gefe riƙe da wani littafi. Ganin shirun yayi yawane murya na rawa tace. "Baba malam gani." tsareta yayi da ido kana yace. "Na ganki ai, ke nake jira inji ko kin fidda tsayeyye kamar yanda na umurceki." Kai ta jujjuya a hankali kana tace. "A'a." Murmushin girma yayi tare da cewa. "To ba matsala, ni na zaɓa miki, zai zo gobe ki ganshi, in ya miki shike nan, in kuma bai mikiba ba dole na baki kwana biyar daga goben sai ki kawo wanda kike so, In kuma har kwana biyar ya cika baki kawoba to tabbas zaɓina ya zama naki." Da ƙarfi ƙirjinta ya wani irin wawan bugawa, take tsoro mai tsanani ya rufeta, da sauri ta rumtse ido jin Ya Aminu na cewa. "Gobe da yamma zaizo kuga juna kada kije ko ina." Kai ta ɗago da nufin zatayi magana kenan. Baba Malam yace. "Tashi kije sai da safe, Allah ya muku al'barka." Da kyar ta iya cewa. "Amin. " kana ta miƙe ta fita. Kafinma ta isa falon tuni hawaye sun ɓata mata fuska. kai tsaye ɗakinta ta nufa. Da sauri Aunty Lubna tabi bayanta tsaye ta sameta ta kifa kai jikin gini tana rera kuka. Kamota tayi suka zauna kan gado. Cikin sassauta lafazi tace. "Meyasa bazaki zama jaruma ba wurin tinkarar matsalarki abu kad'an ki fara kuka." Cikin zubda ƙwalla ta gaya mata abinda Baban nata ya gaya mata. Gyara zama tayi tare da share mata hawayenta kana tace. "To ai da sauƙi tunda har yanzu dai an baki damarki, ki kuma dage da addu'ar Allah ya kawoshi gareki kafin kwanakin da Baba malam ya faɗan su cika. Kuka ba naki bane addu'ace ta kama ceki." cikin jin ƙarfin guiwa ta gyaɗa kai. Haka dai tayi ta rarrashinta har ta sake. Sannan ta fita ta koma side ɗin Mamy, inda ta samu tuni Mamy ta tafi wurin Baba malam. Ɗakin da take sauƙa idan sunzo ta shiga, nan ta samu Ahmad ɗin na yiwa yaransu addu'a. yana gamawa suka dawo parlour'n Mamy nan yake bata labarin komai a kan Saifuddeen, shiru tayi a ranta tana cewa nakasasshe kuma? a fili kuwa lafewa tayi jikin mijinta. A can wurin baba malam kuwa sosai yayiwa Mamy bayani sanin tanada nisuwa kuma Alhamdulillahi don ai ita tasan Saifuddeen farin sani. Ita kuwa Mama Allah-Allah takeyi girkinta yazo, ta shigar da batun Abdussalam a wurin baba malam, akan zata ce mishi Zaleeha ta amince dashi. Washe gari da yamma ƙawayen Zaliha Bilkisu da Rashida suka zo, inda tuni itama ta shirya, har zasu fita Ahmad yace kada su fita su bari sai gobe in yaso suje, ya fake da yasan Rashida ta iya zana lalle yace ta zanawa Lubna. Sosai suke ganin daraja da girman Ya Ahmad ɗin, dan haka ba musu suka amince. Nan Rashida ta fara zanawa Aunty Lubna lalle, ita kuwa

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148