Skip to content

Chapter 132

Chapter 132

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
Download Book

yana kallonta dan sam bai iya mata ƙarya." murmushi tayi tare da cewa. "Allah ya cika rayuwar auren naku da farin ciki." A saman lips inshi ya amsa da Amin. Sai kuma tasa hannu bisa bedside ta ɗauko cup mai ɗauke da zazzafan tea mai ganyen Na'a-na'a, ta miƙa masa. karɓa yayi tare da ɗan zuƙa a hankali, idonshi ya lumshe dan jin ƙamshin da tea ɗin keyi. Ita kuwa Ummi a hankali tace. "Sai da safe ko." Kai ya gyadɗa mata alamun "To." tana fita ta wuce bedroom d'inta, kwanciya tayi amman baccinta yak'i zuwa nazari sosai takeyi tana tsoron duk wani abu da zaizo ya cutar mata da ɗanta. Hayatuddeen kuwa a d'akinshi yana konce yayi ɗai-ɗai yana shan dadɗan sanyin A.C kana yana chatting da yan uwa da abokan arziki inda yaketa sanar musu date ɗin auren Hammanshi. musamman a dandalinshi na Instagram wanda yakeda mabiya sama da dubu 9 wanda kuma yawanci sabida pictures ɗin Saifuddeen ne da yake sawa, da kuma son jin ainihin waye shi, tarin tambayoyin da ake mishi bazai iya amsarsu ba, sabida da yawama a zatonsu Saifuddeen bazai iya aureba. Ganin tambayoyin sun mishi yawane ya rufe datan Instagram yana niyar buɗe WhatsApp sai ga kiran Amina ya shigo wayarshi video call. yana ɗagawa yayi dariya ganin yadda ta haɗe fuska, A ƙufule tace. "Dariya ma na baka kenan?." Cikin dariyar yace. "Hmmm to ni me nayi miki naga sai hararata kikeyi?." ajiyan zuciya ta ɗanyi tare da cewa. "Yau kwana biyar kenan ina kiranka baka ɗaga waya meyasa." da sauri yace. "Sabida nasan zakice in bawa Hamma Saifuddeen wayar, kuma duk sanda kike kira baya kusa shiyasa bana ɗagawa." baki ta ɗan taɓe tare da cewa. "Ai dai yanzu kam yana gida ko?." Miƙewa zaune yayi tare da cewa. "To amman ya shiga fa." Da sauri tace. "Please karkace komai ka kai mishi wayar. Dan Allah karkace a a." jin haka ya miƙe tsaye ya nufi ƙasa. Kai tsaye Side ɗinshi ya nufa inda Ummi ta rufeshi ta baya dan haka a sauƙaƙe ya shiga parlourn, a hankali yace. "Ni dai duk in da akace nawane sai ya koma kamar tirken doki, kalli yanzu parlour nan ko sarkin makka zai zauna a nan komai tsab-tsab sai ƙamshi tamkar da turare ake mishi mopping, kalli can kuma sama yadda banzayen nan su Imran suka wancakalarmin da parlour haka aka barminshi kamar wani maraya, to yaseen yau a nan zan kwana." Ya k'arishe mgnar lokacin da yake shiga bedroom d'in. Ita kuwa Amina sai dariya takeyi dan duk taji me yake faɗin. Yana shiga kai tsaye ya nufi kan gadon inda ya hango Hamman nashi na zaune wayar ya miƙa mishi cikin zumbura baki ya haura kan gadon ya konta gefen ɗan uwan nashi tare da rufe idanunshi wai shi yayi bacci. Murmushi Saifuddeen yayi tare da gyara mushi rufuwan da yayi dan yasan bazai iya jure kwana cikin sanyin dashi yake kwana ba, sai ya kuma juyo ya kalli fuskar wayar tashi daya miƙa mishi, da sauri ya rage idanun nashi ganin fuskar Amina ita kuwa, girarta ɗaya ta ɗaga mishi alamun ya dai. sai ta kuma kalleshi cikin lunshe ido tace. "Ya jikin ka?." bata tsumayi amsaba dan tasan ba samu zatayi ba shiyasa taci gaba da cewa. "In zo har garinku har gidanku in dubaka da jiki, in dawo Amman ko ka kira kaji mun dawo lfy ko?." a hankali ya zaro harshenshi ya lashi jajayan labbanshi hakan yasa suka ƙara fitar da sheƙi, Lumshe idonshi yayi tare ds longoɓar da kanshi bisa kafaɗarshi tare da narke fuska, haka nan yaji wani guntun murmushi ya suɓuce mishi, ido ta lumshe tare da cewa. "Bakinka yana min kyau, gashin girarka mai kyau, idanunka masu tarin kyau, sajenka yana min kyau sosai Hamma, ina son komai naka surarka, yan uwanka, abokanka ina son duk wani abu naka, bayan Ya Amir kaine mutun na forko da nake bege da so." shiru yayi ya zuba mata idanu, yana karantar lafuzanta, ita kuwa cikin zazzafar soyayyarshi dake sarƙe mata zuciya da ruhi tace. "Ina sonka Hamma Saifuddeen zaka aureni? Kayi haƙuri kunya nakeji bazan iya rubuta makaba, kuma inajin kunyan in gayawa Hayatuddeen, gashi kai kuma baka jina to ta yaya zan shaida maka soyayyata, ina sonka ka zamo mijina uban ƴaƴana, ina addu'ar Allah ya azurtamu da samun yara masu kama da kai." sai kuma ta kalleshi ganin ya tsareta da ido haka nan yake jin kalaman nata har cikin zuciyarsa, to amman wai meyasa ita bata kunyan faɗi mishi wasu abin ne, ita kuwa ganin yayi shiru ya kuma rage girmam idanunshi ne ya sata cewa. "Ka gaji ko? bacci kakeji ko?, naga idonka yayi limshi, bari in kashe wayar sai da safe." Tana kaiwa nan ta katse kiran, shi kuwa Saifudddeen dariya yayi a ranshi yace. "Sokuwa kawai mai tunanin yara wato kina sona, hmmm ke dai faɗi gsky bani kike wani soba, kinada dai abinda kikeso daga gareni." daga nan yayi ta aikinshi. sai kusan ƙarfe ɗaya, ya sauƙo ya shimfid'a sallaya kana yaje yayi al'wala sannan yazo yayi nafilfilinshi sai d'aya da rabi ya konta. Washe gari ranar Jummu'a tun da safe su Zaleeha suka dawo, daga gidan Hajja inna tayi wanka ta wuce Billiri dan hira da nakassusun wancan yankin wanda k'arfe biyar na yammacin ranar jumma'ar ne zata gabatar da shirin, tun randa ta had'u da Saifudden a Jonapwd, bata sake zuwa canba, kuma tunda ta turawa ishaq text ɗin ban haƙuri bai kulataba itama bata sake bin ta kanshi ba, shi kuwa Ishaq shida Saifuddeen bakinsu a had'e a cewarshi ita da kanshi zata nemeshi har mazauninshi... K'arfe uku ta dawo daga billiri kai tsaye gidan radio nasu ta nufa, a nan tayi sallan la'asar, sannan ta zauna jiran lokacinta, tana zaune anan Bilkisu ta shigo ita da Manager d'insu tana ganin Zaleeha ta kwashe da dariyar shak'iyanci cikin ingizarwa tace. "Hajiyar nakasassu ina mutanen naki ne? Koda yake amaryar nakasashen gurgu kurma zance ko." cikin tsananin takaici Zaleeha ta watsa mata harara tare da cewa. "A a uwar nakasashe zakice ba amryar nakasashe ba wlh mai gado bana so ki daina had'ani da wannan musakin." cikin Shek'iyanci bilkisu ta iso gareta tare da cewa. "Sorry baza k'araba, amman mutanen nakine da abin dariya." juyawa tayi ta fita tabi bayan Manager ita kuwa Zaleeha Raveel ta kalla wanda yake mik'o mata sweet amsa tayi tare da cewa. "Ngd." kai ya gyad'a mata tare da cewa. "Kada ki sake aibata nakasassu dan duk wanda bai mutuba ba'a gama mishi halittaba. da kullum haka kike gaya min to meyasa kawai dan nakasasshe yace yana sonki sai ki juye daga Mai kakkyawar alaƙa i zuwa mummunar ɗabi'a, kada ki bari imaninki ya samu rauni." kai ta gyaɗa mishi sannan ta juya ta nufi ɗakin gabatar da shirin nata ganin lokacinta yayi. Mama kuwa da Zahira sosai zugar Ruda yayi tasiri a kwanyarsu da yake dama zuciyar ba inganci. Ƙarfe huɗu dai-dai suka dawo daga doho, suna shiga gidan kai tsaye side d'in Baba malam suka nupa, a parlour suka sameshi shida Ya Ahmad da Ya Habu, sai Mamy dake haɗa musu tea a kofuna. sannu da hanya sukayi musu,

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148