Skip to content

Chapter 18

Chapter 18

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,204 words 0 views Progress saved
Download Book

bakin igiyar daga jikin kuros d'in, dan ta gama gugar nashi har ta goge uniforms d'insu Hayatuddeen da Faruq na boko da islamiya. gyara zamanta tayi suna fuskantar juna, a hankali ya bud'e bakinshi kana ya had'a lips enshi da alamu furta. "Sannu Addana ngd." lumshe ido tayi tare da cewa. "Godiya kuma a kan me?." zuba musu ido Ummi tayi tana jin so da k'aunar yaran nata da tausayinsu na ratsa mata zuciya musamman Saifuddeen, hannu ta d'aura bisa kan Saifuddeen d'in, shafawa takeyi a hankali tare kallon yadda ya manna kanshi bisa cinyarta murya a tausashe tace. "Babana kayi shiru kamar ranka baiso mu amshi kayan bako?." jujjuya mata kai yayi kana suka juyo suka kalli Rahma data shafa k'afarshi tare da jan 'yan yatsunsi biyu kana tace. "Kada ranka ya b'aci muma bisa dole muka amsa bawan Allah nan har durk'usa mana yayi yana kuka yana bamu hak'uri, k'in amsar kayan zaisa yayi ta zaton ko bamu yafe mishi bane." murmushi yayi tare da lumshe ido cikin kurma-kurma dayin body language ya had'a hannunshi duka biyu ya karkad'a kana ya shafa gemunshi tare da nuna musu kunnenshi alamun yace. "Ba komifa na fahimta, ai Bappa Ali yamin bayani." sai ya kuma kalli Ummi kana ya gyara zama sannan yayi mata bayanin canjin kasuwancin da zaiyi, haka nan Ummi ta tsinci kanta cikin farin ciki dan wannanma wata alamace dake nuna Saifuddeen inta yana tare da mutanen kirki nagari kuma wannan ya nuna mata kasuwa tasan da Saif d'inta. "Alhamdulillahi Babana Allah ya sanya al'khairi yasa ka fara harkar a sa'a rabbi yasa ka shiga da k'afar dama." Amin Amin suka amsa shida Rahma, kana ya mata bayanin fasa asusunshi nanma tace. "Hakan yayi yadda bappankun yace haka zakayi, ka bari tukun kaga yadda kasuwar ledan take." kai ya gyad'a mata kana sukaci gaba da hirarsu har zuwa 11:36 pm sannan sukayi saida safe, Rahma ta tafi d'akinsu ita dasu Raihana Ummi kuwa ita da Autanta da Faruq, shiko Saifuddeen d'akinshi ya tafi, koda yaje buta ya d'auka al'wala yayi sannan yazo yayi nafilfili daga bisani ya fara karatun Qur'an yayi kusan awa biyu sannan yayi addu'o'in da neman sa'a da nasara a kasuwancinsa ya rok'i Allah ya tsareshi da cin amana sannan daga bisani ya mik'e ya kashe wutan d'akin kana ya matso da fankanshi kusa da gadon tare da k'ara gudun fanka, gefen katifar ya zauna tare da yin addu'o'in bacci qulhuwa 3 falaqi 3 nasi 3 sannan ayatul kursi'u 1 ya shafa sannan ya konta da hannun dama, a hankali ya gyara konciyarshi tare da yin mik'a ido ya lumshe yana mai mamakin Al'amarin halittarshi a ranshi yake cewa. "Anya kuwa ni lafiyeyye ne." sai ya muka juya rigingine ya kuma yi mik'a still ba sauyi ajiyan zuciya yaja tare da barin abin a ranshi kana ya fara tasbihi dan ya samu bacci ya saceshi cikin k'ank'anin lokaci kuwa yayi bacci abunshi. Washe gari kuwa kamar kullum da sassafe suka tafi gombe shida Salisu nan suka wuni kasuwancinsu, bayan sallan isha suka koma Dukku. washe gari wanda ana gobe za'a d'au Azumi sabida ana zaton ganin wata yau, wanda ranar ne kuma Baba bello zai sallami kasuwa sai kuma bayan salla. Ranar sammako sukayi sosai shida Salisunshi k'arfe bakwai dai-dai na safe suka isa birnin bubayero, bayan Salisu ya sauk'eshi sai ya tsallaka bakin tashar gombe line, ya fara d'aukan irin masu kai aike tasha da sanyin safiyan nan. Shi kuwa Saifuddeen yazo dai-dai mashigar kenan yaga Jabeer ma, da sauri Jabeer ya iso gabanshi tare da bashi hannu cikin fara'a yace. "Tab Lallai wannan balaraben dukkun da himma kake wato in junin wani sammako kai a tafe ka kwanako?." hannu yasa ya d'an bugi k'eyar Jabeer irin ya cika surutu nan. shi kuwa Jabeer kama hannunshi yayi suka nufi cikin kasuwar da yanzu ake shirin bud'eta sai ya kuma kalli Saifuddeen tare da d'aga mishi gira kana yace. "Ko dai kudin aure kake nema ne wannan iya sammako haka har ka rigamu mu yan cikin gari, nima dana fito yanzu yaseen Ya Adamu ne ya matsa wai inzo in kimtsa shagon yau zuwa jibi kayanmu zasu iso zamu fara baza hajar cinikin salla ne." murmushi ya d'anyi kana ya jinjina mishi hannu alamun mgninka ai. suna isa shagon Jabeer ya bud'e sannan ya fara kikimtsa wurin, yayinda Saifuddeen ke taiyashi, tuni suka kimtsa shagon suka gyara komai yayi ras, kafin su gama tuni kasuwa ta fara cika duk masu shaguna sun firfito da kayayya kinsu cikin yin mik'a alamun gajiya. Jabeer ya kalleshi tare da cewa. "Yauwa Balarabe jirani bari inzo." kai ya gyad'a mishi kana ya konta bisa tattausan sallayan daya shimfid'a cikin shagon ga iskan fanka na kad'ashi ido ya lumshe tare da gyara kinciyarshi. Shi kuwa Jabeer yana fita bakin tashar ya nufa inda wasu masu saida abinci suke, soyayyan dankali da kwai, sai gasashiyar kaza ya sai musu kana ya shiga shagon gefen wurin ya saya musu Faro k'ananun roba guda biyu, sai molt, kana ya juya rik'e da ledojin ya nufi cikin kasuwar. Bayan ya isa ya tsallaka wani dandamali da akayi wanda yake shamaki tsakanin masu shago da masu sayan kaya, kusa da Saifuddeen d'in ya zauna bubbud'e musu takardun abincin yayi kana ya kalli Saifuddeen dake konce yanata tab'e baki cikin tsuke fuska yace. "Ka tashi muyi breakfast." fuskar ya kuma ya mutsawa tare da jujjuya mishi alamun bazai ciba ya koshi, ido Jabeer ya tsura mishi domin tabbas yasan wannan d'abi'ace ta fulani yin fulaku wa kowama. shi kuma Saifuddeen tashi zaune yayi ganin kamar ran Jabeer ya sosu sai ya d'auki ruwa kana ya b'alle marfin sannan ya d'an sha ruwan har kusan rabin robar, a hankali yayi gyatsa kana ya ajiye goran ruwan sannan ya d'auki na molt, ya fara k'ok'arin mik'ewa da sauri Jabeer ya rik'o hannunshi kana yace. "Meyasa ne kake min haka shin baka d'aukeni aboki bako bare in kai matsayin amini." kai ya jujjuya mishi kana ya zaro bironshi tare da ballan takarda ya rubuta mishi. "Am so sorry my friend, wlh a k'oshe nake Ummi ta cika min ciki da d'umame yau da kanta taimin dan Adda Rahma taje gidan Goggo Dada can ta kwana, kana ni bana cin kaza, shiyasa, sannan dankalin kuma ba irin suyan da nake so bane akayi shiyasa bazanci ba, ai dani da kai yanzu mun zarta abokai mun zamma aminai, ka fahimceni." yana karantawa yace. "To gaya min me Kakeso in sayo maka?." amsar takardar ya kumayi ya juya bayanta kana ya rubuta mishi. "Am sorry Jabeer ba wai nak'i ci bane haka nan badan wani abu ba because inada wani banzai kyakk'yani wanda ni kaina yana damuna ba ko ina nake iya cin abinciba. Kaga zansha molt baka tab'a lura daniba haka nake wuni bani cin komai wani lokacin sai dai in had'a molt da pic milk sai insha." tabbas Jabeer yasan hakane so duk da haka baiji dad'in rashin cin nashiba, amman dole ya hak'ura dan Saifuddeen da wuya yaci, shi kuwa Saifuddeen tsallaka madandalin yayi kana ya nufi shagonsu Hisham wanda yau cikansa ya zarta na kullum, bayan sun gaisane yaje ya amshi botikinshi sabida lokacin wasu nata karya kumallonsu

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148