Chapter 62
Chapter 62
yayi tare da cewa. "ai ba idone gani ba, ku masu idone kuke d'auka da ido kawai ake gani, mu kunnuwanmu ma tamkar idone kana da zuciyarmu da k'ok'wolwarmu, yayinda kuramenmu kuma idanunsu ne kunnuwansu, ba gashi yanzu koda bana ganinka nasan kana zubda hawaye daga sautin muryarka." cikin sanyi Hayatuddeen yace. "Ku kwantar hankalinku, ku dakata dan Allah kuyi hakuri yanzu bazaku sami ganin saba dan yasamu yin bacci saidai zuwa anjima." cikin gamsuwa sukace. "To yajikin nasa?." saida ya maida hawayensa dake kukarin zubo masa dagudun kada hankulansu yatashi,danyasan cewa basu kadai ahalinsa kebukatar Hamma Saifuddeen ba, hardasu wadanna nakasassun,dama wasunsu baki d'aya,. "Da sauki". yace dasu atakaice, dakyar shugabannin nasu suka samu suka lallab'asu sukatafi,sanna shikuma Hayatuddeen yayiwa su ishaq d'in iso zuwa ciki inda su Ummi suke. Suna shiga Dr Adnan nafitowa, kana Dr Arabi nabiye dashi su Ummi naganinsu sukamike tsaye suka k'araso inda suke,Ummi kallonsu take fuska kunshe da tanbayoyi Dr Arabi yakalli Dr Adnan wanda keta noke-noke yayi masa alama da ido, jiki asanyaye Dr Adnan ya mik'awa Ummi wata doguwa takarda fara yace. "Ummi wanna takardar ta transfer ce zuwa Abuja, naturaku asibitin kimiya dake birnin tarayya Abuja National hospital Abuja ,idan kun isa saikiba su wanna takardar da sauri Ummi tace. "Abuja! Kuma?." kai ya gyad'a mata alamar eh, a hankali tace. "Lallai ciwon Saifuddeen babbane tunda har katuramu Abuja." Kai Adnan ya girgiza dasauri,dan bazai iya fad'a mata akwai masala ba, yafiso sai sunje can d'in asanar musu. tana karbar takardar yayi saurin juyawa dasauri dan gudun kada Ummi takuma jefo masa wat tanbayar, yanafita yayi duk wani cuku-cukun dayadace natafiyarsu ba tareda bata lokaciba yakammala komai bank'arensu. Ishaq kuwa takardar ya amsa kana suka juya tare da Raihana, kai tsaye Federal low cos suka nufa, E passport d'in Ummi da Saifuddeen dana Hayatuddden yasa Raihana ta kawo mishi, daga nan direban k'ungiyar tasu yaja suka wuce Airport, nan ya gama musu dukkan shirin tafiya hardashi d'in suka kuma yi sa'a akwai jirgin da zai tashi zuwa Abuja k'arfe biyun rana zai tashi. 1:53 pm duk sun gama shirin komai, takofar baya Dr Adnan yashiga yaturo gadon yafita takofar bayan, Dr Arabi natsaye ajikin motar da zai kaisu airport da taimakon sa suka tura gadon cikin motar suka dai-dai zaman gadon sosai acikin motar, Kana Dr Adnan yakoma indasu Ummi suke yace. "To Ummi an gama shirya komai shirya komai ku akejira yanzu, sanna kuma tafiyar zai kasance dole damutun biyune sanna kuma... da sauri Raihana tace. "Ummi ku kutafi keda Hayatuddeen, mu zamu koma gida nida Raliya fatanmu samun saukin Hamma Saifuddeen zan kira Abban Farida yayi k'ok'arin dawowa,." cikin gamsuwa Ummi tace. "to". "kuyi maza kutafi nima zuwa gobe da yamma zan shigo Abujan." Dr Adnan ya fad'i tare da juyawa yayi gaba, da sauri suka bishi abaya. koda suka'isa jikin motar, Ummi da Hayatuddeen suka shiga,driver yatada motar Raliya da Raihana nad'aga musu hannu dayimusu fatan samun nasara,yiyinda dukansu suke ta sharar kwalla,driver yaja sukabar harabar asibitin, "Sukadau hanyar Airport, in da tuni ishaq na can su kawai yake jira. suna isa bada jimawa ba jirginsu ya tashi. 3:00pm yamusu a cikin birnin taraiya Abuja direct National hospital suka nufa. Kasancewar duk abinda yadace Dr Adnan yarigada ya'aiwatar dashi ta online , so ansan da zuwansu,basusha wani wahalaba,suna isa nurses suka taho jikin motar data d'aukosu daga airport nan suka fito dashi. Kana Ummi tamikawa d'aya dagacin nurse d'in takardar da Dr Adnan yabata,sanna suka turoshi sukashiga cikin asibitin, direct Emergence room aka shige dashi. Nan Doctors suka dukufa akanshi basu yi wata-wata ba suka fara bincike akan laluransa kamar yanda yazo musu arubuce, cikin k'ank'anin lokaci S.....! By *GARKUWAR MARUBUTA* 8/18/20, 7:52 PM - Ummi Tandama: [3/30, 10:50 AM] 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *NAKASA BA KASAWA BACE* *PAGE 15* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ~Free page~ Suka gano matsalar shi, kana suka dugufa kanshi dan samo numfashin sa ya dai-dai ta, domin babu wani aiki da zasuyi mishi har sai ya dawo haiyacinshi. Hakan yasa suka meda hankali ganin komai ya dai-dai ta, cikin ikon Allah a daren ranar ya farfad'o yana kuma cikin haiyacin sa, kasan cewar dare yayi nisa, yasa aka bar batun dubashi zuwa safiya. Bappa Ali da Warisu da Mudassir kuwa tunda Hayatuddeen ya sanar musu gaba d'aya hankalin su ya tashi sai dai sun meda hankali wurin yi mishi addu'ar samun lfy a cikin ka'aba. Ishaq kuwa, tunda aka shaida musu bazasu dubash yau ba sai gobei, sai ya kira babban yayanshi dake nan Abuja da iyalanshi ya shaida mishi, ba jimawa kuwa Ya Rabi'u yazo tare da direbanshi, domin dukkan sashin zuriya biyun sun san abotar Ishaq da Saifeddeen domin abotace tun na yarinta, hakan yasa har iyaye su suke mutunci da zumunci mai k'arfi. Kasan cewar babban doctor uban gidane ga Dr Adnan hakan yasa tun kafin suzo an shirya komai, hatta da masu kula dashi, ya tanadar cikin ma aikatan nasu, ya kuwa kontarwa Ummi hankali ta tare da bata k'arfin guiwa. Haka yasa Ya Rabi'u ya tafi da su gidanshi, cikin sa'a ma kuwa asibitin ba tazara sosai da diganshi. Ummi kuwa da Hayatuddeen dugufa sukayi da Addu'a jigon nasu. Deren ranar sam basu rumtsaba, shima Ishaqa bayi bacciba. A can gida Gombe kuwa, bayan su Raihana sun koma gida, kai tsaye falon Ummi suka wuce, cikin sanyin jiki Raihana ta zauna bisa kujera, idonta ta rumtse da k'arfi, a jere wasu zafafan hawaye suka zubo mata, ita kuwa Raliya wayarta ta d'auka, ta fara 'yan dube-dube bayan yan wasu dak'ik'u ta kara wayar a kunne, a hankali ta bud'e labbanta tare da cewa. "Wa'alaikassalam, Abban Farida, yaushe zaka dawo?." a can d'aya sashin Abban Farida yace. "Lafiya dai ko?." murya a sanyaya tace. "Alhamdulillahi ala kulli halin." jin haka yasan to tabbas akwai matsala sai dai iya sarrafa harshe na matar kwarai wacce tasan yadda zata isar da sak'o wa mijinta ba tare data firgitashi ba, cikin dakiya yace. "Meke faruwa?." tallabe hab'arta tayi tare da cewa. "Abban Farida ka dawo gobe, please inda hali in zaka samu jirgin yau dan Allah ka taho gida." cikin kad'uwa yace. "Raliya meke faruwa ki gaya min mana, zuciyata ta cika da zulumi." "Hamma Saufudddeeen! Saifuddeeen!! Saifuddeen..!!!." tai ta maimaita mishi murya na rawa. mik'ewa yayi tsaye cikin fargaba yace. "Innalillahi wa Inna'illaihi rajiun. Meya sameshi? ina Hayatuddeen? Ina Ummi?." Cikin kuka tace. "Suna Abuja an tafi dashi asibiti." daga nan ta sanar dashi dukkan abinda yake faruwa, ta k'ara da cewa. "Ya Adnan ya turasu Abuja. Abban Farida ka dawo wlh Hamma Saifuddeen ko motsi baya yi sanda suka tafi dashi." ta karishe maganar tana zubda hawaye. Shi kuwa Abban Farida datse kiran yayi kana ya fara harhad'a yan abin buk'atunshi, kai tsaye Airport ya nufa cikin sa'a ya samu jirgin Abuja, dama shi bai niyar zuwa Gombe ba. Kafin su isa abuja dare ya d'an fara nisa kuma yayi ta kiran number Hayatuddeen da Ummi duk basu d'agawa, haka yasa ya nemi masauk'i inda ya kwana da nufin da safe zai nemesu. Dr Adnan kuwa, saida yaga tashin su Ummi sai da ya koma asibitin kafin ya koma gida. Shiru parlour nasu ba kowa haka yasa ya zauna bisa 1
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148