Skip to content

Chapter 75

Chapter 75

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
Download Book

meyasa ban aurar dake ba, na barki kinata gallafiri a gari sai kije gidan radio kiyi ta zuba kid'e-kid'e kina waƙe-waƙe kamar zabiya, to na baki shekara guda." cikin jin dad'i Zaleeha ta gyada kai dan ita a ganinta ai bata da matsala shekara guda aka bata so sai takega ai lokacin da tsawo lokacin ya isheta ta nemo inda yake tasan halin da yake ciki ta bashi tukuicin aurenta bisa kareta da yayi ya zame mata Garkuwa ya saida ranshi a kanta, to me take dashi da zata bashi a duniya in banda kanta ta hanyar haure tayi mishi biyayya ta faranta mushi ta haskaka mishi dararen rayuwarsu. Aminu kuwa tsawa ya daka mata tare da cewa. "Baki da bakin amsawa ne sai mgna da kai?." cikin tsoronshi tace. "Na amsa fa Ya Aminu." tsaki ya d'anja kana yace. "Wallahi Allah kenan, kada kiyi kuka da kowa kiyi kuka da kanki in har kika bari akaje matakin da Baba Malam zai miki zabi, kin sani muddin yace eh to eh d'ince har gaban abadan in kuma yace a a to a ance, dana gaba ake gane zurfin ruwa kin daiga Maryam gata a gidane tana kuma da yara har biyu dan haka kada kiyi wasa da damarki ki fito da zabinki in kin tsaida goni dai babu mai miki dole." cikin sanyi tace. "To ngd Ya Aminu." sai ta kuma kalli Mahaifin nasu cikin sanyi da tsantsar biyayya tace. "Ngd Baba Malam Allah ya k'ara girma, ya jik'a magabata." "Amin Amin Allah ya muku al'barka ya tsareku da sharrin shaid'an da fitinar zamani." ya fad'i yana gyara zamanshi, domin yana jin dad'in addu'ar da yaranshi kewa iyayenshi haka yana nuna mishin koda bayan ranshi zasu kasance mishi al'waladul saliha. Ita kuwa Zaleeha sai ta kuma kalli Ya Habu tare da cewa. "Ya Habu ga car Key inka." amsa yayi yana hararanta kana yace. "Ni naso ace wata biyu za'a bata ai." hannu Baban nasu ya d'aga mishi kana yace. "Aminu yi mana addu'a." Addu'a yayi musu kana suka tashi daga taron. ita da Mamanta suka wuce side din Maman, Maryam kuma tabi bayan Mamy, kana Aminu da Ahmad kuwa, suna zaune gaban Baba Malam suna tattauna kan lamarin Zaleehan, ganin mangrib ta gabato yasa sukayi al'wala suka nufi masallacin dake cikin gidan nasu. A falo suka samu d'an wani matashi wanda bazai wuce sa'an Hayatuddeen ba, yana ganin Zaleeha yazo gabanta tare da cewa. "Dan Allah Zaleeha sammin motarki mana." hararanshi tayi tare da cewa, "Lallai kam Zakariyya ni zan baka motata wacce nima ko hawanta banba kai ko key d'intama Ya Ahmad bai banba nima yau da ta Ya Habu naje wurin aiki, yanzune dana dawo ne naga motar a parking lot." harara ya watsa mata cikin tsama irinta sak'o da sak'o yace. "Kada Allah yasa ki bada, kawai dan na tambayeki sai kita min ihu a kai." cikin huce haushinta a kanshi tace. "Ni zaka cewa ina maka ihu a kai ni mahaukaciyace da zan maka ihu." Gwalo ya mata tare da cewa.. "To da banne? Ba gashiba daga mgna kin fara zubda ƙolla." juyawa tayi ta kalli Mamansu data zuba musu ido tana dariya dan yanzu in ta shiga zasu nuna mata itace bare inda sabo kowa yasan Zaleeha da Zakariyya, shida hatta abo kanshi sun medata abokiyar wasansu. ganin Maman tana murmushi yasa tace. "Mama kina jinshi yana cemin mahaukaciya, kuma kina dariya." cikin muryar rashin fara'a tace. "Kunfi kusa." shi kuwa Zakariyya dariya yayi tare da cewa. "Ni barima in koma." zama tayi bisa stull din dake tsakiyar falon kana tace. "Da yafi maka kam, d'an ci rani kawai, gwara ka koma can wurin tsohuwar nan data sakaltaka kuyu fama da wannan tsukekken anguwar taku dake saman dutse." zama yayi kusa da ita tare da cewa. "Tab kaji yarinya nida gidanmu harda cemin d'an cin rani, toma na fasa tafiya." murmushi tayi tare da share hawayenta dake zuba duk sanda ta tunoshi kai ta sunkuyar kana tace, "Rainon kaka kawai". Oho dai na fiki shanawa Baba malam yana ji dani tunda na girma gaban tsohuwarshi bakiji har cewa yake nine zan samu irin tarbiyarshi." cewar Zakariyya, ita kuwa Zaleeha wayarta ta duba tare da cewa. "Rainon sakalci ba, naga hatta abo kanka sakalallune." dariya yayi kana yace. "Oho dai na yarda ni goyon kakane, inje ƙasar da nakeso da ƴar tsohuwata." baki ta tabe kana tace. "Yaro kai ke jiran wani ya biya maka ni in naga dama al'bashi na zai kaini ." murmushi tayi tare da cewa. "Daga baya Keenan." Gefenta ya zauna kana yace. "Yauwa Adda Zaleeha kin tuna wannan abokin nawa Hayatuddeen wanda kwanaki kuka had'u a gidan kaka yaje wurina?." jim ta d'anyi kana tace. "Yes na tunashi wani kekyawan yaro shima sakali irinka." da sauri yace . "Eh shi dai." aje wayarta tayi tare da cewa. "Har yace min shine d'an auta a gidansu shiyasa akeji dashi." Cikin sauri Zakariyya yace. "Yesss kin gane." sai ya kuma yayi kalar tausayi tare da cewa. "Ayyah to shine nakeso inje gidansu. Yayanshi ba lfy, suna Abuja yace ba mmki ma su wuce India, to shine zanje in gaida wata yayarshi Raliyya irinki." cikin sanyi tace. "Ayyah Allah ya bashi lfy, kaje wurin. Ya Ahmad ka amshi Key din." tsalle yayi tare da manna mata kiss a goshinta tare da cewa. "Yesss my lovely Aunty faratu." ajiyan zuciya tai kana tace. "Yayi kyau dan na bakane zaka cemin faratu ko?." bazan sakeba yace yana mai fita, da sauri tabi bayanshi kana tace. "Yauwa Zakariyya ga kud'i in kana dawowa dan Allah ka saya min feesh roll." ba musu ya amshi kudin kana yaje ya amshi key din sannan ya tafi. Ita kuwa saida ta wasa ruwa sannan ta nufi side d'in Mamy inda ta samu Ya Ahmad da Maryam suna cin abinci. Gefen Maryam ta zauna tare da cewa. "Ya tafi ko?." Ahmad ne ya d'an kalleta tare da cewa. "Waye d'in?." jujjuya kai ta d'anyi tare da lek'a hanyar shiga sannan tace. "Wannan masifeffen mijin nata mana. Shi komai in ansa dashi sai ya zak'e ya rink'a rabka over acting." tab'e baki Maryam tayi kana tace. "Kamar a kunnenshi kika fad'i yaseen zan fad'a mishi." ido ta zazzaro tare da cewa. "Dan Allah rufa min asiri, wannan saggamin yanzu zaice zai gwada gwanjinshi a kaina." dariya sukayi sannan daga bisani Ahmad da Maryam sukayi ta bata shawarar kadafa ta bari ta k'ure Baba malam, suna nan sunata hira Zakariyya ya dawo nan akaci gaba da hira tare dashi, sai dai sam Zaleeha bata tare dasu har Ahmad ya fahimci hakan , so sai ya danganta abin da ko mgnar auren da akayi matane, sai daga baya Maryam ta mik'e ta tafi side d'in mamansu nan suka d'an tab'a hira kana, suka fito dan tafiya gidan ganin Ahmad ya fito zai maida Zakariyya gidan kakar tasu da yake shi tun yaye yake hannunta, ganin dare ya d'anyi ne yasa Aminu cewa, Ahmad ya bari zasu biya su sauk'i Zakariyyan. *** Asalin ahlin Zaleeha. Malam Bashir Suleiman Dukku asalin haifeffen garin Dukku ne gaba da baya, Malami ne wanda yakeda cikar haiba da kamala, Su uku ne a wurin iyayensu babban yayansu Malam

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148