Chapter 92
Chapter 92
imani cewa Amina batasan da cewa Hammanshi na fahimtar maganar mutunba idan yana kallon bakin me maganar ba, tabbas da batayi wannan katoɓarar ba. Shikuwa Saifuddeen idanunsa ya mayar ya rufe yana mejin yanda heart ɗinsa ke beating, sam yarasa ma tunanin me zaiyi hakan yasa yanemi ƙaƙalowa kansa bacci. *** A nan Nigeria kuwa Zaliha jiki asaluɓe haka kuma zuciyarta ɗauke da mamakin ganin Abdussalam da iyayensa acikin gidansu ta tura hancin motar tata cikin gidan. Tana gama dai-dai-ta parking ta ɗauki ƴar jakanta me kyau tare da buɗe murfin motar ta fito. Kaitsaye ɓangaren Mamy Hajiyar Ya Ahmad ta nufa, da sallama ɗauke abakinta ta kutsa kanta cikin falon, Mamy dake zaune akan kujera ta amsa mata sallaman nata fuska ɗauke da murmushi. "Mamy sannu da gida". tafaɗa tana me nufar inda makeken fridge ɗin dake cikin falon yake. "Yauwa Zaliha ya wajen aikin naku?". cewar Mamy data maida hankalinta ga tv. "Alhamdulillah". tabawa Mamy amsa tana me ƙoƙarin kafa bakinta ajikin goran ruwan data ɗauka acikin fridge, dawowa cikin falon tayi tare da kwantawa akan kujera kana ta lumshe gajiyayyun idanunta wandanda suke cike da zallar zazzafar soyayyan Saifuddeen, wanda kullum take k'ara narkar da zuciyarta. Zahira ce tashigo cikin falon daɗan sauri, ganin Zaliha kwance yasanya taɗan tsaya tare da cewa "Laaa Adda Zalee dama kina nan?". Harara Zaliha ta wurga mata tare dacewa. "Da bananan ai bazaki ganni ba!". dariya Zahira tayi tare da cewa. "Dama kina da baƙo a BQ yanajiran dawowarki". Idanu Zaliha ta ɗan zaro cike da mamaki tace. "Baƙo kuma wajena yazo?". Mamy dake jinsu ne tayi murmushi tare da cewa "Bak'ofa akace miki ba dodoba, kike wani zaro ido Abdussalam ne yazo". Jitayi gabanta ya faɗi don sai yanzune ma tatuno ganin da tayi musu shida iyayensa a lokacin da zata shigo cikin gidan, fuska ta kwaɓe tare da langwaɓar da kanta gefe, murya asanyaye tace. "Ayya Mamy mekuma yazoyi?". "Me kuwa zaizo yi idan ba abun da bakyaso ba, kullum muna miki faɗa akan kifitar da tsayayye guda ɗaya amma kinƙi, to dai Abdussalam kam yagaji da wainasa da kikeyi yaturo iyayensa sun nema masa izinin zuwa zance awajen mahaifinki, ko tantama banayi kuma nasan ya amince musu!" Wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tsaya amaƙoshin Zaliha, take haushin Abdussalam ya cika ranta, meyasa zaiyi mata haka batare da ya tsaya yaji ta bakinta ba? ɗan ƙaramin bakinta ta turo gaba tare da komawa ta kwanta. "Tashi kije ko bakiji Zahira tace nemanki akeyi ba, Kije ki sameshi ku fuskanci juna, inafa gaya miki Zaleeha kada ki bari ki k'ure Malam kinfa sanshi kaifi d'aya ne zafa kiyi kuka a sanda babu mai lallashinki". Mamy tafaɗa cike da kulawa, cikin turo baki gaba Zaliha ta-tashi daga kwancen da take tare da ɗaukan hand bag ɗinta tafice, sashinsu ta nufa fuskarnan tata babu fara'a ko kaɗan, harta kusa kaiwa ɗakinta taji muryar mahaifiyarta inda take cewa. "Da kika dawo tun ɗazu kika tsaya shashancinki bakisan cewa kina da baƙo bane?". bakinta taƙara turowa gaba tare da cewa. "Ni agajiye nake yaje sai wani lokaci kawai". kallon bata da hankali Mahaifiyarta ta tayi mata tare da cewa "Zaki shirya kije ki samesa ne ko ko sai na ɓata miki rai yaro yazo yana son ganinki kice yaje sai wata rana shi bawan gidanku ne, ko kin mance shi d'an wanene?". ganin yanda mahaifiyarta ta ta haɗe fuska ne yasanya ta buɗe ɗakinta ta shige tana me guna-guni acikin ranta, kayan jikinta ta rage tare da faɗawa bathroom, haka tayi wanka ranta duk acushe, koda ta fito sama sama ta shafa lotion ajikinta, riga da sket na wani purpule ɗin material tasanya, sosai kayan suka amshi jikinta sukayi ɗas. kallon kanta tayi amadubi, tabbas ita kanta tasan cewa kyawunta ya zarce misali, sannan tanada diri irin wanda ke ɗaukan hankalin maza, yanda takeji aranta yasanya bata jin zama ta iyayin kwalliya akan fuskarta, saidai kuma abun da batasani ba shine ko babu kwalliya akan fuskarta tauraron kyawunta haskawa yake, farfumed ta fesa ajikinta me daɗin ƙamshi kana ta ɗauki wani purpule ɗin mayafi tayafa ajikinta, normal flat shoe ta zura aƙafanta kana ta murɗa handle ɗin ƙofar tafice, BQ ta nufa inda tuni tasake sanja yanayin fuskarta. Sallama tayi can aƙasan maƙoshinta haka ta tura kofar katafaren falon tashiga. duk da cewa sautin sallaman nata baifito sosai ba amma yaji sautin acikin kunnuwansa, lumshe idanunsa yayi sakamakon wani daddaɗan ƙamshi daya kawowa hancinsa ziyara, ahankali ya amsa mata da "Wa'alaikissalam!" Cikin takunta me ɗauke da nutsuwa taƙaraso cikin falon tare da zama akan wata kujera dake nesa da wanda yake kai. Murmushi Abdussalam yayi tare da cewa "Barka da dawowa gimbiyar mata, kiyi haƙuri kindawo kuma na hanaki hutawa". ɗan satan kallon inda yake tayi tare da ɗauke kanta gefe, sanin cewa ba lallai tayi magana ba yasanyashi cigaba da cewa "Kiyi hakuri nima zazzafar soyayyarki ce take hanani hutawa, ita ke ingizani wurin kafa naci. Haƙiƙa yau ina cikin farinciki kasancewar nasamu izinin zuwa wajenki daga wajen Malam. Ina sonki Zaliha ina miki so me tsanani, tabbas kina da wata irin baiwa ta musamman wanda duk wani ɗa namiji idan yaganki dole zaiji wani abu dangane dake, burina bazai wuce naga na sameki amatsayin mata ta ba, dan Allah Zaliha ki amincemin ki duba girman soyayyar danake miki!". yaƙare maganar cikin yanayi na kwantar da murya. wani murmushi Zaliha tayi wanda ya sake bayyana asalin kyawunta, bakomai yasata murmushin ba kuwa face jin ta tsuniyar da Abdussalam keyi mata akan wai yana fatan tazamowarta mata agaresa, lumshe kyawawan idanunta wanda ke masifar jan hankalin maza tayi tare da jingina bayanta da jikin kujera, hoton kyakkyawar fuskarsa ne ke yawo acikin idanunta koda yaushe, wani irin azababben so da shauƙin ganinsa ne suka dirar mata alokaci guda, take yanayinta ya sauya wani irin sanyi taji na shiga jikinta, ƙwaƙwalwarta ne ta tuna no mata lokacin data kalli cikin idanunsa, tsikar jikinta ne taji yatashi yayinda taji zuciyarta na bugawa da sauri-sauri ji take kamar tayi ta shelanta duniya tana sonshi tana kuma nemanshi da buƙatar ganinshi. Abdussalam kuwa ganin tayi shiru kamar ma bata cikin hayyacinta yasanyashi ƙiran sunanta murya asanyaye yace. "Zaliha!". Ƙiran sunanta dayayi shiyayi sanadiyar dawowarta cikin sense ɗinta, ahankali ta buɗe idanunta da suke cike da shauƙin ganinsa, sam bataso Abdussalam ya katse mata tunaninta ba, kasancewar ayanzu tunaninsa shiya zame mata abincin ruhinta, miƙewa tsaye tayi tare da duban Abdussalam daya ƙafeta da ido. "Zanshiga gida!". ta faɗa ataƙaice. Murmushi yayi tare da cewa. "Idan muna tare banaso kiyi nesa dani". Bakinta taɗan taɓe tare da cewa. "Saida safe". Bata tsaya jin wani abu daga bakinsa ba tasakai tafice daga cikin falon, shiru Abdussalam yayi tare da bin bayanta da ido, jin soyayyarta yake tana ratsa ko ina na jikinsa, jiki asanyaye haka ya ɗauki makullin motarsa shima ya fice daga cikin falon. Itakuwa Zaliha tana kaiwa part ɗinsu kai tsaye ɗakinta ta wuce, kwanciya tayi luf akan gado tare da hugging pillow, idan da ace za a fasa zuciyarta to tabbas za'atarar da tarin begensa acikinta, wani irin abu takeji dangane dashi na musamman, sake rungume pillow'n tayi tare da sakin wata sassanyar ajiyar zuciya,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148