Skip to content

Chapter 119

Chapter 119

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

mugun kallo ta watsawa Mamy tare da cewa. "Mugun furuci? Akwai wani mugun furucine daya wuce abinda kuka haɗa baki kuna cewa, dan tsabar son k..". Shiru tayi da bakinta sabida yadda taga Baba malam na watsa mata kallon ki shiga hankalinki kana ya nuna mata ƙofar fita. Kamar kububuwa haka ta fice cikin zafin zuciya da takaici, tana isa parlour'nta ta rinƙa kai mari ta kai gwarzo cikin tarin takaici tace. "Shike nan ga irin ta nan, ni dama sam-sam ban taɓa yin farin ciki da wannan aiki na Zaleeha ba, ta ƙare lokutanta cikin waɗannan kurame da makafi da guragu, abinda nike tsoron shike bina, in banda tsinennen gurgu mai shegen tsaurin ido inashi ina ɗiyata da ƴaƴan ministers ma basu isheta kalloba, wayyo Allah ni Halima Allah ka dubeni da idon rahama wannan kurma kuma gurgu ya Allah tsole idonsa ya zama makaho inga ta inda zai sake kallarmin ƴa bare yace yana sonta." zama tayi bisa sofa cikin zafin zuciya da tarin masifa, sai ta kuma miƙewa tamkar an tsikareta, cikin ɗaga sauti tace. "Ina ai wlh muddin ina raye bazata taɓa saɓuwaba, ɗiyata ta zama matar gurgu kurma nakasasshe. lallai shima Ahmad, wato ɗan ubanci zai nunawa Zaleeha dan ya gadi munafurcin uwarshi, a rinƙa musu kallon salihai kuma mugaye ne." haka dai tayi ta safa da marwa tana surfa bala'i. A parlour kuwa tana fita sukaci gaba da abinda ya damesu, inda Ahmad ya matso mahaifin nashi yana karantar dashi. A can BQ kuwa suna shiga Zaleeha tayi mamakin ganin Ishaq so sai ta saki ranta a zatonta kawai ziyara ya kawo mata ba wanda Baba malam yace zai zo ɗin bane. Cikin ɗan sakin fuska tace. "Malam Ishaq kaine yau a gidanmu kai lale marhaba." cikin jin daɗin yanayin muryarta yace. "Yauwa ƙanwata yau kam dai gani na kawo miki ziyara." "Ai kuwa ka kyauta naji daɗi sannunku da zuwa." ta ƙarisa maganan tana mai kallon Ahmad. "Yauwa Amaryarmu." Ahmad ya faɗa cikin sakin fuska, da sauri ta ɗan waro idanunta wanda kuma sai lokacin ta kalli Saifuddeen dake gefen Ahmad, kamar abin tsafi idanunsu suka sarƙafe cikin na juna. wani irin azabebben faɗuwa taji gabanta yayi, wanda a take ta janye idanunta dan sam bata iya juran kallon cikin ƙwayan idanun wanna ɗan ruwan injita da faɗi. Wani dogon tsaki taja tare da cilla mishi wani zazzafan harara, kana ta janye idanunta da sauri. wanda ganin haka yasa fara'ar Ahmad daƙushewa. Rashida ce ta kalli Ahmad cikin kamala tace. "Ina wuni." jiki a sanyaye yace. "Lafiya lau ya gida." "Alhamdulillahi" Bilkisu tace dashi, ita kuwa Zaleeha juyawa tayi ta fuskanci Ishaq rai a ɗan ɓace tace. "Ya Ishaq ya mutane na?." gyara zamanshi yayi tare da shafa cinyoyinshi irin yadda al'adar makafi take yace. "Duk suna lfy sunce in gaidaki." Cikin ɗan sakin fuska ta kuma cewa. "Ina ko amsawa." sai kuma ta ɗan daure ta ɗan kalli Ahmad a fizge tare da cewa. "Ina wuni." A gajarce yace. "Lafiya!." Juyawa sukayi kan Bilkeesu jin tana cewa. "To waye ne angon namu a cikinku?." Dan so take taje taci gaba da kallonta. Ahmad ne ya kalleta cikin cikar haiba ya nuna Saifuddeen da yake hukunta Zaleeha da ƙwayar idanunshi kana yace. "Gashi nan wannan shine angon naku mai jiran gado in Allah ya yarda." Kusan a tare su duka uku suka zuba mishi ido. ita Zaleeha wani irin mutuwar zaune furucin Ahmad ya jaza mata, hatta bakinta data buɗe dan cewa hahhhh Allah bai bata iko da damar rufeshi ba. Bilkeesu da Rashida kuwa wani irin kallo sukewa Saifuddeen tare da cewa. "Masha Allah. Kai angon nan da amaryarnan sune sirrin kyau." sai kuma Rashida ta kalleshi cikin mutuntaka taka tace. "Ina wuni ango mai jiran gado." shiru bai amsaba sai ta kuma yin murmushi tare da cewa. "Rowar murya ne angon zai mana?." Ahmad ne ya d'an tab'ashi wanda sai yanzu suka lura cewa kan whellchair yake zaune. kusan a tare suka kalleshi suka kalli Zaleeha sai kuma suka kalli juna cikin tarin mmki. Bilkeesu ce tayi ƙarfin halin cewa. "Ina wuni angon Zaleeha." Kai ya jinjina mata alamar lfy, tare da yi mata mgna cikin body language. "Ya kuke." tofa abin ya fara zarta zatonsu cikin son gano gaskiyar abin Bilkeesu tace. "Wai meyasa baya Magana ne? Kodai zuwanmu tarene ya ɓata mishi rai?." Ishaq ne ya ɗanyi Murmushi tare da cewa. "No, ai kurmane bayaji kuma baya Magana." Ya ƙarishe maganar cikin rashin damuwa dan shi a wurinshi sam nakasa ba kasawa bace. Da ƙarfi suka haɗa baki wurin cewa. "Toh kurma kuma gurgu a kan whelchair!." sai kuma Bilkeesu ta tuntsure da wata iriyar dariya mai cike da jin daɗi kana ta bugi ƙafar Zaleeha tare da cewa. "To Hajiar babu nakasashe sai rago. Lallai yau shirinki ya miki rana kin samo zankaɗeɗen saurayi kurma kuma gurgu." ina ita ma Rashida tuni dariyarta da take dannewa ya subce mata. Ahmad kuwa wani irin haɗe fuska yayi tamkar zaiyi ruwan jini. Ishaq kuwa cikin kaushin murya yace. "Ke Zaleeha waɗan nan ƙawayen naki wasu irin muta nene da basu san daraja da ƙimar ɗan adam ba? me a jikinmu da zasuyi ta mana dariya." cikin dariya Bilkisu tace. "Kai tafi daga nan makahon banza makahon wofi. In banda iskanci ina wannan gurgun ina zankaɗeɗiyar baby kamar Zaleeha." Cikin zafin rai da tsawa Ishaq yace. "Ke Zaleeha ki dakatar da wannan mahaukaciyar ƙawar taki da wanna hauk..". Shiru yayi ba tare daya ƙarasa zancen nasa ba jin wani irin kuka mai cin rai da Zaleeha ta saki da ɗan ƙarfi cikin ɗaga murya tace. "Ya isa! Ya isa!! Ya isa!!! Haka malam Ishaq ka farka daga wanna wawan baccin da kakeyi har ya kaika dayin mummunan mafarki. Ƙawata ba mahaukaciya bace, sai dai ko wannan dutsen da ka zo dashi shine mahaukaci." Cikin tsananin fushi Ahmad ya yunƙura, sai ya kuma koma ya zauna jin wani irin zazzafan riƙo da Saifuddeen ya yi mishi wanda ya zubawa su Zaleeha da ƙawayenta ido yana gane duk abinda suke faɗin. Cikin zafin rai Ahmad yace. "Waye kike cewa dutsen?." A zafafe ta kalleshi tace. "Shi wannan halittan ruwan da kuka zomin dashi. Me marabarshi da dutse, kurma kuma gurgu, kalleshi kamar al'jani dan kyau. Ginennen taɓo kawai." Sai ta kuma juyo ta kalli ishaq cikin kuka ta haɗe hannayenta duka biyu wuri ɗaya alamun neman al'farma tamkar yana ganinta tace. "Dan Allah Malam Ishaq kada ka sake min wanna haukan, kadai san ina ganin ƙimarka da darajar ka, so please bana sonshi na tsaneshi!." Sai kuma ta juyo ta kalli Saifuddeen tare da cewa. "Wallahi kurwata kurr ko kaine sarkin mayu to ni nan Zaleeha nafi ƙarfinka, nan gani nan bari, ƙwalelen kare da hantar kura, mcheeww banza kawai!! " Hannu tasa ta jawo hannayensu Bilkisu daketa dariyar ƙeta tayi, fuuuuu suka fice daga cikin falon... Ina Ahmad fa bazai iya magana ba, dan tsananin ɓacin rai da jin tsanar Zaleeha a ranshi. Miƙewa yayi a fusace ya koma bayan Saifuddeen tare da tura whelchair ɗin cikin ƙunan rai yacewa ishaq. "Mu tafi ishaq." shima ishaq rai a ɓace ya miƙe yabi bayansu. Mota suka shiga, kana Ahmad ya figi motar ya

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148