Skip to content

Chapter 13

Chapter 13

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

kolban man shanun da suke sawa in sunyi d'umame, bud'ewa tayi tare da tsiyaya mishi kana ta mik'e ta koma kitchen robar dakekken yajin borkono ta d'auko sannan ta dawo barbad'a mishi tayi, sannan ta d'auki kofi ta nufi d'akinshi ruwa ta d'ebo mishi a wannan randar tashi, sannan ta kawo mishi tare da cewa. "Kaci kafin ku tafi." kai ya gyad'a mata kana ya kalli Umminshi dake shirya Hayatuddeen yanata zumbura baki, murmushi yayi tare da jawo hannun Hayatuddeen yana mishi tambaya irin tasu ta kurame ya tambayeshi me ya sashi fushin. Bakin ya kuma turawa kana ya rab'a jikin Saifyddeen d'in tare da cewa. "Hamma Saif ba Adda Rahma bace tayi d'umame kua tasan ni bana cin d'umame hakama Faruq da Adda Raliyya." murmushi yayi kana ya jawoshi ya ajiyeshi gefenshi, a hankali yasa cokalin da Rahma ta mik'i mishi ya gutsuri gayan kana ya dandalo miyar da taketa k'amshin man shanu, bakin Hayatuddeen ya kai, tura baki yayi tare kwabe fuska kana yace. "Na k'os. " bai k'arisa mgnar tashiba yayi shiru, jin ya sa mishi loman a bakinshi, lumshe ido yayi tare da fara sarrafa abincin, saida ya had'iye kana ya bud'e idanunshi tare da cewa. "Dad'i wlh miyar tayi dad'i Faruq zo kaci." Ummi kam da Raihana dake shirya Faruq tuni dariya sukeyi, shima Saifuddeen dariya yakeyi har saida dimples nashi suka lotse sosai kana fararen hak'oranshi suka baiyana manyan idanunshi ya lumshe tare daci gaba da basu abincin a baki, aifa sukaci sukayi nak, sannan suka tafi makaranta, ita kuwa Raihana da sauri ta fita tace. "Adda Rahma ki samishi wani abincin su Faruq sun cinye wannan, harda santinsu." dariya sukayi kana Rahma ta samishi wani yana cikin cine Salisu ya shigo nan sukaci tare kafin suka fita suka tafi. Yauma kamar kullum Saifuddeen wuni yayi yana yawo da bulayi a kasuwa, sai da magrib tayi ya fito, kana yayi salla kafin Salisu yazo ya d'aukeshi yau ma fura da nono yasha da zasu tafi. Haka dai Saifuddeen yayi ta fama yawo da wahala a cikin kasuwar Gombe har tsawon kwana bakwai, to a ranan ne kuma Salisu ya basu balance ensu kamar yadda sukayi duk sati zaike basu dubu biyar. Koda ya karbi kud'in Bappa Ali ya kaiwa su, shi kuwa Bappa Ali k'in amsarsu yayi yace ya kaiwa Ummi kud'in zasu samu abinda zasuke sarrafa cefenen abincin. da yake har yanzu sunada sauran abincin da baban Arabi ya kawo musu. Shi kuwa Saifuddeen sai ya zare dubu biyu ya bawa bappan nashi, amman sam yak'i karb'a acewarsa ai da yanada hali shine ya kamata ya basu, to dai ganin Saifuddeen ya b'ata rai ya sashi amsar 1k yasanya al'barka. Shiko yaje ya bawa Ummi dubu uku sannan ya d'auki dubu d'aya. Ummi kam sai sanya mishi al'barka takeyi. Washe gari kamar kullum suka shirya suka tafi cikin. Gombe a inda ya saba sauk'eshi yau ma nan ya sauk'eshin, bayan Salisun ya tafi shi kuma Saifuddeen sai ya d'anyi tattaki zuwa bakin mashigar kasuwar, addu'a yayi kamar kullum kana ya shiga da k'afar dama, yauma bakin shagunan yayi tabi har kusa k'arfe shad'aya lokacin rana ta tsala zafi ya fara, sai ya nufi layin masu robobi, yana zuwa shagon wani bayerbe sai ya tsaya, bokatin kand'e tsirara ya saya wanda wasu ke cemai ganta sarai, bayan sun gama ciniki cikin mgnar kurame ya bashi dubu d'ayannan, kana bayerben ya bashi canjinshi, daga nan ya nufi wani layin tafiya kad'an yayi sai gashi a wani babban shago da yake cike da d'ima-d'ima firiji masu tsawo da masu fad'i. Yana zuwa d'aya daga cikin yaran shagon yace mishi. "Kana son ruwane?." da sauri ya gyad'a mishi alamar eh. shi kuwa yaro bud'e wani k'aton firiji yayi kana ya juyo ya kalleshi, sannan yace. "Leda nawa kake so?." hannunshi ya d'ago kana ya had'a yatsunshi biyu yayi mishi alama da leda biyu yakeso. cikin mmki yaro ya kalleshi kana ya kawo mishi leda biyun sannan yace mushi. "Kai kurmane?." murmushi Saifuddeen yayi kana ya gyad'a mishi kai tare da mik'a mishi d'ari biyun, amsa yayi tare da bashi canjinshi kana yace. "Kuma naga kamar kana gane abinda nake fad'i ko?." still kai ya gyad'a tare dasa lododin ruwan cikin bokatin daya saya d'in, a take botikin yayi sanyi sabida ruwan yanada tsananin sanyi wasu har sun fara yin k'ank'ara, shi kuwa yaron shagon ashirin ya kuma zarowa a al'jihunshi kana ya mik'a mishi tare da cewa. "Gashi nayi maka ragin naira 10 cikin ko wanne leda akan yadda muke sararwa Allah ya baka sa'a inka k'arema kazo zan ajiye maka mai sanyi." cikin murmushi Saifuddeen ya jujjuya mishi kai alamun baya son ragin, kana ya juya ya nuna mishi sauran yaran ya mishi alamun da sai dai in suma duk za'ayi musu ragin, cikin sauk'e numfashi yaro yace. "To sadaka na baka." fuska ya had'e kana ya tsuguna gefe tare da rubuta mishi. "Bara nazo makane da zakace sadaka ka bani? in sadaka kakeson badawa kaje gidan marayu da gajiyayyu, ni karka kashe min zuciya, ka dai ajemin mai sanyi in wannan ya k'are zan kuma zuwa." hannu yaron ya bashi sukayi musabaha lokacin daya karanta rubutun kana yace. "To kayi hak'uri abokina sai ka dawo d'in." kai ya jinjina kana ya juya hannunshi rik'e da botikin. ya fara bin layi-layi yana yawo, amman babu wanda yace mishi kawo, har ruwan ya fara rage sanyi. cikin gajiya ya dawo bakin shagon masu kayan kitchen inda ya huta jiyan nan, inda ya zauna jiyan yauma nan ya zauna ya tasa batikin a gabanshi. yaron jiyan ne ya kula dashi cikin fara'a yace. "Balarabe yauma ka zone?." cikin gajiya ya lumshe mishi idanu alamar eh, shi kuwa yaron shagon cikin karantar yanayinshi yace. "To yau ma hutawa kazo yine ko zaka sayi abune?." da ido ya nuna mishi botikin pure water enshin, cikin sauri ya zaro ido tare da cewa. "Wai kai dama tallan ruwa kakeyi ne?". Kai ya gyad'a mishi tare gyara zamanshi, cikin sanyi yace. "To wai kai kurmane naga jiyama har ka tafi body language kakeyi min." still sai ya d'aga mishi gira duka biyu alamun eh shi kurmane. da sauri yaron ya kalli alajin shagon cikin tausayawa yace. "Abba kalli wai wannan Balaraben kurmane kuma wai ruwa yake saidawa." sai ya kuma kalli Saifuddeen tare da yin rau-rau kamar idanunshi zasu zubda hawaye, ganin haka da sauri Saifuddeen ya jujjuya mishi kai sannan yasa hannunshi bisa idanunshi alamun kar yayi kuka. still shima wanda ya kira da Abba sai ya zuba musu ido tare da cewa. "To Hisham kafi ubangijin daya halicceshi a haka sonshi ne? kada kayi kuka kasa mishi rauni, ai ita Nakasa ba kasawa bace, bare wannan mai nagartane Kaga dai jiya kun dad'e tare amman duk bamu gane kurma bane kuma kaga yana gane duk abinda muke cewa. So shi bai sa nakasar jikinsa ta zamar mishi na zuciya ba." Jin haka sai Hisham ya sharshe hawayenshi kana yayi murmushi tare da bawa Saifuddeen hannu yace. "Daga yau kai aboki nane." shima Saifuddeen murmushi yayi, shi kuwa Alhaji Ibrahim al'barka ya samusu. Sai ya kuma kalli costumers insu da suke cike da shagon inda d'aya daga cikinsu ta kalli botikin

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148