Skip to content

Chapter 133

Chapter 133

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,204 words 0 views Progress saved
Download Book

fuskarnan kamar zatayi ruwan jini Mama ta amsa musu kana ta gaida Baba malam, sannan Ahmad da Habu suka gaidata, Zahira kuma duk ta gaidasu sannan ta wuce cikin gidan tayi shashin maman. Ita kuwa Mama a hankali ta mik'e ta fita ganin duk basubi ta kantaba, to wazai kulata yadda taketa harare-harare, tana fita ta nufi Side d'inta da yake tsab Maryam da Aunty Lubna sun gyarashi jiya da dare. A parlour ta zauna, dai-dai lokacin kuma Zahira ta fito daga bedroom d'in Maman a guje, ganin Maman a parlour yasata tsayuwa cikin rawan jiki da halin fitina tace. "Mama zo zo zo kiga wani abu a bedroom naki." tsaki ta d'an ja tare da cewa. "Menene kike wani zaro idanu haka?." hannun uwar ta kamo tare da cewa. "Mama zo ki gani mana an cika miki d'aki da akwatuna dasu buhunan gishiri dasu goro." ido ta zaro gaba d'aya tare da cewa. "Akwa tuna kuma to na meye." cikin hatsabibanci tace. "To waya sani ko lefen Anty Zaleeha aka kawo." ai kafin ta rufe bakima Mama ta kutsa kai cikin bedroom ɗin. wani irin wawan birki taja tare da cewa. "To wanna kuma daga ina, to ko Abdussalam ne da tace mishi a turo komanshi Zaleeha ta yarda dashi, tuni ya turo ɗin, sai kuma ta girgiza kai ina sam ba shi bane ai in shine zai gaya mata, shida kuma ɗazu suka gama mgna, cikin tafasan bala'i tace to waye. Sai kuma ta dawo parlour da sauri cikin karad'i da kware murya baki d'aya ta fara rabkawa Habu kira. "Habu! Habu!! Habu!!! Habuuuu!." da sauri ya iso cikin parlourn a tsorace yace. "Na'am Mama ganifa nazo." A hatsale tace. "To dan ubanka meyasa bazaka amsa da kyau ba." cikin had'e fuska yace, "Na'am." cikin yamutsa fuska tace. "Wancan kayan fa na meye ne." Kai tsaye yace. "Lefen Zaleeha aka kawo jiya." cikin ɗaga sauti tace waye kawo lefen?." A dake yace. "Wasu mata ne." zaburowa tayi kanshi tare da cewa. "Dan ubanka ba wanda suka kawo nake tambaya ba wanda aka kawowa nake nufi." cikin kauda kai yace. "Zaleeha aka kawowa." wani dogon tsaki taja tare da jawo hannunshi tace. "Kai mahaukacin inane wanne saurayin ne ya aiko lefen." Cikin dakiya da rashin tsoro yace. "Saifuddeen." wani irin zabura tayi tare da buga tsalle tace. "Inji uban waye ya basu damar kawo banzayen lefen wanna musakin d'an nasu?." Yana fita yace. "Inji Baba Malam mana Baban Zaleeha shine ya basu dama." wani irin kware murya tayi tare da yin sauri ta nufi parlour Baba malam tana shiga parlour tare da masifa murya a hargitse tace. "Lallai yau za'a sabunta yaƙin duniya....! *Dan Allah da manzonsa ku dena fitarmin da littafi,* By *GARKUWAR FULANI* 8/ *NAKASA BA KASAWA BACE* *PAGE 30* NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 "Lallai yau za'a sabunta yaƙin duniya na biyu". Fuska ta ƙara haɗewa tamkar wacce akayiwa bushara da mummunan al'kaba'in rayuwar duniya. Ido suka zuba mata baki ɗayansu, tare da maida hankalinsu gareta. Cikin takaici da tashin hankali tace. "Meyasa! Meyasa haka ne malam? Ina dalilin kullum sai an sani baƙin ciki kan aurar da ƴaƴana?." Kauda kanshi yayi daga kallon mummunar fuskarta tare da maida dubanshi ga al'ƙiblah, a hankali yaci gaba da tasbihi da yakeyi. "Subahallahi, walhamdulillahi, wa la'ilahalillahu, wallahu akhbar." haka yaketa mai-maitawa tare da motsa yatsun hannunshi na dama, kana yana ɗan karkaɗa ƙafafunshi dake miƙe bisa table ɗin dake gabanshi a hankali a hankali. idonshi ya rumtse da ƙarfi jin Mama na cewa. "Wallahi-Wallahi bazan taɓa yarda a zalumunci Zaleeha irin yadda aka zalumci Maryam ba, akan wani dalili zai sa baza'a sakarmin rayuwar yarana ba, suma su auri wanda sukeso sai ayi ta musu cushe da auren dole ina dalili? to Wallahi muddin ina raye, Wallahi bazan taɓa lamunta Zaleeha ta zauna da wannan banzan nakasasshen kurma kuma gurgun, da kuka yayibo zaku liƙa mata ku kashe mata rayuwa ba, haka kawai dan an iya min kisan mummuƙe, shine za'a nunamin wariyar launin fata, a nuna min ni bare ce to Wallahi ban amince ba!." Cikin gajiya da ihu da hayagagar da take musu Ya Ahmad ya ɗan tanƙwashe sawunshi tare da cewa. "Mama ai Zaleeha ita ta kawo shi, zaɓinta ne ita ta amince dashi babu wanda ya mata dole, itace ta amince tasa ya turo iyayenshi." Cikin tsawa tace. "Rufe min baki, kaima ae munafuki ne, ban nemi jin ta bakinka ba, da ubanka nake magana, karka wani karkace kace zaka meda laifin kan Zaleeha, munafurcin banza kawai." Rumtse idanu Ya Ahmad yayi, cikin takaicin abinda Mama'n kewa mahaifin nashi yace. "Allah ya huci zuciyarki." A hasale tace. "Wannan karon dai zuciyar tawa ba zata huce ba, Wallahi bazan taɓa lamunta da batun ƴata ta auri musakiba, dan rainin hankalin yarinya da kyawunta da ƙimarta tanada masoya gabas da yamma kudu da arewa amman a rasa wanda za'a zaɓa mata sai nakasasshe, wulaƙantacce wanda ko magana bayaji!." Tafaɗa ranta amatuƙar ɓace domin sosai zuciyarta ke tafasa. Duk ihu da hargowan da takeyi Baba Malam bai sake ɗaga ido ya kalleta ba, sai ma tasbihi da yakeyi ga mahaliccinsa da ya jarabceshi da auran wanna mata mai munanan al'adu. Mamy kuwa wayarta ta jawo kana ta fara karanta Dua Azkar. Ganin haka shima Ahmad sai yasa hannu ya ɗauki ɗan madai-daicin Qur'Ani'n dake gefenshi ya buɗe ya fara karatu ahankali cikin suratul. Kahf kasan cewar yammacin Jummu'a ne. Habu ne ya shigo parlour'n a hankali ya nufi gefen mahaifin nasu ya zauna kusa da ɗan uwan shi Ahmad, ido ya rumtse da ƙarfi yana mai jin takaicin hali irin na mahaifiyar tashi, cikin sanyin sauti yace. "Ya salam! Dan Allah Mama kiyi haƙuri ki bar yin ihun nan, kowa yanayin abinda zai samar mishi lada ke kuma kinzo kina tarawa kanki zunubi kina ɗaga harshenki sama dana mijink..." Da sauri ya haɗiye rogowar maganar tashi, sakamakon jin Maman ta kai mishi wani uban bugu kan bakinshi. "Habu kayi asara Wallahi, kai dai ka banunka da baka da kishin mahaifiyarka!." Takuma faɗa a hasale. Baba Malam ne ya miƙe tsaye, tare da kallon yaran nashi cikin kamala da cikar haiba yace. "Kuyi al'awala mu tafi masalaci lokacin sallah ya gabato." Da sauri suka mimmiƙe tare da cewa. "To." Haka duk sukaje suka sabunta al'wala kana suka tafi zuwa masallaci. Mamy ma tuni tayi side ɗinta, inda ta samu Aunty Lubna a parlour tana sawa ƴarta hijabi alamun zatayi salla ne. "Barka da shigowa Mamy." cikin nitsuwa da mutuntaka Mamy tace. "Barka dai Lubna ya gajiyar kitchen? na tafi na barki ke ɗaya da aiki niƙi niƙi ko." Kai ta rausayar tare da cewa. "Tun ɗazu na gama ai Mamy aikin ba yawa." "Masha Allah! Allah Ya saka da al'khairi, ya baki surkai masu miki fiye da abinda kike min." "Amin Amin" Aunty Lubna ta amsa cikin jin daɗi, kana tayi side ɗin da nanne masauƙinsu duk lokacin da sukazo Gombe dan ita da Mamy tamkar uwa da ƴarta haka suke. Ita kuwa Mama ta cika tayi tam sai ihu da haushi takeyi ita kaɗai kamar karya. "Watoma mahaukaciya suka medani? sun watse sun barni wato inyi ta haushi ni ɗaya ko, tam zanyi maganinku, Wallahi gaba ɗaya

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148