Skip to content

Chapter 6

Chapter 6

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

mutanen dake zageye da Nuruddeen suke fad'i, yayinda wasu suka ma kasa mgna sai d'aura hannu sukayi a kai, kana wasu sai jujjuya kai sukeyi. mai mota kuwa da ker ya samu ya fara sarrafa motar har ya samu ta tsaya, yana fitowa da gudu ya nufi inda dandazon mutanen suke, kutsawa yayi tayi tsakiyar mutanen har ya samu ya isa, ido ya rumtse da k'arfi cikin tsananin fargaba ya sunkuyo kan Nuruddeen da yake konce lib bisa titi, ida nunshi a rufe kirib sai numfashin shi dake korar juna, da sauri ya tallaboshi tare dagowa ya kalli mutanen cikin tashin hankali yace. "Ku taimaka min mana in d'agashi in sashi a mota." wani k'ak'k'arfan matashi ne, yayi maza ya sunkuyo ya ciccibi Nuruddeen kana cikin, d'aga murya yace. "Biyoni." yana fad'in haka ya juya ya tsallaka titin zuwa d'aya hannun kana ya nufi cikin asibitin MUSABA dake fuskantar tashan Dukkun, cikin rawan jiki mutumin ya mik'e kana yabi bayanshi. suna shiga Reception suka nufa, ganin sun shigo hajaram majaram yasa Nurse's yin kansu da tambayar meke faruwa, cikin kad'uwa mutumin nan yace, "Accident ne ku taimaka doctor ya dubashi." juyawa sukayi suka kalli juna, kana d'aya daga cikinsu tace. "Ko an gayawa doctor bazai dubashi ba sai an nemo police." jin haka yasa mutumin nan juyawa da sauri ya fita, gudu-gudu sauri-sauri ya tsallaka titin kana ya nufi wurin motar tashi, yana shiga ya nufi Gombe division yana zuwa ya musu bayanin abinda ke faruwa, ba b'ata lokaci suka had'ashi da police d'aya, kana suka tafi tare, suna zuwa Doctor in ya amsheshi bisa sa hannun hukuma kana fara bashi taimakon gaggawa, sannan daga bisani ya ce su tafi Medical Center. Ba b'ata lokaci suka amshi shawararshi suka tafi can, suna zuwa aka amsheshi. shi kuwa police yasa d'aya police d'in yaje ya d'auki machine d'n nashi ya kaishi officensu. kana sun samu wayarshi y'ar Nokia dake jikinshi tanan aka kira Bappa Ali aka sanar mishi meke faruwa. Lokacin da aka gayawa Bappa Ali yana cikin garin kurugu da yake ranar larabace, to yaje cin kasuwa, ana gaya mishi bawan Allah ya bar duk abinda yakeyi ya nufi cikin Gombe kai tsaye Medical Center din ya nufa, inda yana zuwa fargabarshi ta k'aru domin tunda Nuruddeen ya fad'i bai sake bud'e idanunshi ba kuma uwa uba yana konce tamkar gawa komai sai an mishi ga roba a hanci da baki da k'asanshi wannan abu yayi matuk'ar firgitashi, duk da k'arfin zuciya irin na bappa Ali sai da yayi ta kuka, mutumin daya bugi Nuruddeeen ma sai kukan yake sabida kukan da Bappa Ali keyi ya matuk'ar karya mishi zuciya sai hak'uri yake bashi da neman yafiyarsu. Cikin raunin murya yake cewa. "Ku gafar ceni tsautsayine, nayi iya k'ok'arina inga na tsare motata bataje ta bugeshi ba amman ina Allah ya k'addara faruwar hatsarin bani da tsumi ko wayo bare k'arfin hanawa." sai ya kuma sharte hawayenshi kana yaci gaba da cewa. "Tunda nake ban tab'a shiga cikin tashan Dukku ba, sai yau, ashe ashe ban saniba masifa ke kirana." shi kuwa Bappa Ali ya gaza cewa komai domin da ganin mutumin ya girmeshi kuma bisa dukkan alamu mutum ne mai daraja da ka ganshi kasan mai kamalane, shi kuwa mutum shirun Bappa Ali sai ya sa mishi rauni yana ganin shike nan ya cucesu, yana bashi hak'uri yana tuno dalilin zuwanshi tashan, dan matarshi da ta kasance yar Ngalda to kullum shi ke kaita to yau kuma har ya shirya zai kaita sai kuma motocin kayanshi suka iso, so shiyasa yace bari ya kaita tasha ta shiga motar kasuwa, to shinefa ya kaita kenan yana fitowa wannan hatsarin ya auku. Bappa Ali kuwa ganin yanata bashi hak'uri ya sashi yin k'arfin halin cewa. "Ba komai Allah ya bashi lfy, ai shi tsautsayi ba ta inda baya wakana." sosai mutumin ya d'anji sanyi kana yace. "Wacce uguwa kuke ne?." cikin sanyi Bappa Ali yace. "Har Dukku muke." da sauri yace. "Ina mamanshi?." kai ya jinjina kana yace. "Mamanshi da babanshi duk basu saniba, suna Dukku ni kuma dama ina Kurugu to da aka kirani sai na taho nand'in. Yanzu in ba matsala in akwai masu kula dashi zan wuce Dukku inje in sanar musu." cikin kad'uwa yace. "To kai waye d'inshi ne?." "Ni bappanshi ne k'anin mahaifinshi kuma mahaifin nashima baida lfy." kai ya jinjina kana ya zaro kud'i a aljihunshi sannan ya mik'a mishi tare da cewa. "Ba matsala zan kula da komai kayi maza kaje ka sanar musu." k'in amsar kud'in yayi, shi kuwa mutumin ya sashi karb'a a dole. Haka dai ya amshi kudin badon ya soba ya tafi, shi kuwa mutumin shida kanshi ya zauna wurin kana ya bada duk abinda ya dace na jinyar Nuruddeen. Shi kuwa bappa Ali daya koma Dukku jiki a mace yayiwa Ummi bayani sai dai ya boye mata hak'ik'anin halin da Seyojinta ke ciki, yace mata da sauk'i sosai baiji ciwoba an dai mishi allurar bacci ne dan ya huta. To shiyasa hankalin ta bai tashi sosaiba, Saifuddeen kuma tun lokacin da Yayan nashi ya tafi sai yaja hannun Hayatuddeen suka tafi gidan Goggo Dada, to shiyasa bappa Ali bai tarar dashi a gidaba, kuma gidan Goggo Dada nada d'an nisa don ita a Shabewa take. Abba kuwa baida lfy ba damar yaje, haka yasa Bappa Ali ya juya shida Adnan babban abokin Nuruddeen d'in, kana sai Rahma. Koda sukaje gaba d'aya hankalinsu ya tashi ganin yadda Nuruddeen ke kwance tamkar gawa Rahma tayi ta kuka tamkar ranta zai fita, Adnan yanata rarrashinta, Bappa Ali kuwa mutumin ne keta rarrashinsa. Ganin dare ya fara nisa yasa Bappa Ali cewa Rahma ta koma dan har takwas na dare yayi, jin haka yasa mutumin nan k'iran d'anshi mai suna Arabi yazo. Kana yace ya maidata Dukku da motar da yazo, ba musu ya d'auki Rahma ya maidata Dukku, yana ajeta ya juyo Gombe. Ita kuwa Rahma jiki a mace ta shiga gida, Ummi dasu Saifuddeen da Abba dasu Raihana suka tasats a gaba da tambayar ya jikin nashi. sanin in ta gaya musu gskyar halin da yake ciki ba mmki jikin Abba ya tashi, Ummi ta k'ara shiga damuwa dan haka sai tai ta ce musu jikifa da sauk'i, koda Ummi ta bata abinci sam ta kasa ci, sai hawaye da take zubdawa time to time, kana tana sa hannu tana goge hawayen dan kar Ummi ko Saifuddeen su gani dan sam ta lura hankalin su a tashe yake. haka dai sukayi ta jimantawa juna kana sukayi shirin bacci da nufin gari na wayewa Ummi da Saifuddeen zasu shirya suje. Rahma kuwa har ta konta Ummi ta kuma biyota d'akinsu tana k'ara tambayar yanayin jikin nashi nanma dai boye mata gskyar tayi. a haka dai suka kwana da fargaba. A can Gombe kuwa k'arfe d'aya dai-dai na dere Nuruddeen yace ga garinku, Allah sarki rai bak'on duniya, bayan likitan ya sanar musu ya cika, Bappa Ali kam sai ya rasa inda zaisa ranshi kawai sai ya shiga d'akin da gawar yake yayi ta zagaya gadon yana wani irin azabebben kuka maicin zuciya da tada hankalin mai sauraro, Adnan kuwa kanshi ya kife gefen kan Nuruddeen yana wani irin sassayan kuka mai zazzafan

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148