Skip to content

Chapter 98

Chapter 98

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

ta nitsu kana ya jawota suka zauna kan kujera, tafin hannunshi yasa yana share mata hawaye tare da cewa. "Am so sorry my happiness kiyi shiru ba abinda zai sameta sai al'khairi ki daina kuka, zan mata duk abinda kike so kinji ko Ummu Ayman?." Kanta ta gyad'a mishi alamun gamsuwa, duk da haka bai bartaba har saida ya sama mata cikekkiyar nitsuwa. Ita kuwa Zaleeha tuni wani baccin kuka ya kwasheta. Shi kuwa Raveel koda yaje office ya kasa samun sukuni. Sai sak'onnin ban hak'uri yaketa tura mata. Abuja Amina ce ke zaune bisa sallayarta, yayinda ta bud'e hannayenta sama Cikin sanyin lafazi take cewa. "Ya haiyu ya k'aiyum ya ubangijin sammai da k'asai ya rabbil izzati kaine mai rayawa mai kashewa ya Allah ka raya min wannan bawa naka Saifuddeen. Ya Allah ka bashi lfy, Allah ka jib'anci lamuranshi ka sanya salama da farin ciki a rayuwarshi ya Allah ka cika mishi dukkan buk'atunshi na al'khairi." A hankali ta shafa addu'ar tare da zamewa ta kwanta a nan bisa sallayar, tare da jawo wayarta hotonshi dake bisa fuskar wayarta ta zubawa ido. murmushin da yake a hoton sai takega kamar ita yakeyiwa. Indian Mumbai A guje nurses da Doctors suka shigo d'akinda Saifuddeen ke ciki sabida ihu da kururuwan da Hayatuddeen keyi. Ihu yakeyi yana tsalle tamkar yaro kana yana yarfa hannu yana cewa. "Wayyo Allah na yau farin ciki zai kasheni, Wayyo ni Hayatuddeen waye zai tayani farin ciki, Wayyo Ummi na yau ga Hamma Saifuddeen d'ina a zaune da k'ugunshi, ya tashi ya zauna da kanshi ba tare da taimakon kowaba. Wayyo Adda Rahma Raihana, Raliya d'an uwanmu ya fara zama da kanshi. Ya Adnan ya Ahmad Bappa Ali ina kuke?." sai kuma yayi kan Hamman nashi wanda tuni likitoci sun zagayeshi, yayinda suma duk fuskokinsu ke cike da farin ciki. Wani Irin sassanyan rugguma yayiwa Saifuddeen sai kuma ya fashe da wani irin kuka wanda daga kaji kasan daga cikin zuciyarshi kukan ke fitowa. Ganin haka yasa Saifuddeen ruggumeshi da kyau tare da d'an bubbuga bayanshi kana ya d'agoshi ya share mishi hawayenshi tare da mishi alamun. Shin irin godiyar daya dace yayi Allah kenan?. gane hakan ya sashi yin sujhadar shukur da sauri, wanda kafin ya d'ago daga sujjadar tuni an tura gadon da Saifuddeen ke kai an shiga dashi wani d'aki na musamman. Ummi kuwa duk abinda Hayatuddeen keyi da fad'i tanaji, Lokaci d'aya hawayen farin ciki ya rufeta, cikin tsananin happy ta sanarwa Raliyya abinda taji, ruggume juna sukayi dan tsananin farin ciki, daga nan Raliya ta fita a guje side d'insu ta nufa, tana shiga ta samu ya Ahmad d'in baya parlour da gudu ta kutsa kai bedroom nanma baya ciki. Jin motsin ruwane yasa tayi saurin bud'e k'ofar bathroom d'in, hangoshi tayi k'asan shower yana tsaye ba komai a jikinshi, cikin wani irin tsalle ta fad'a jikinshi dan ta mance cewa wai gudunshi tayi. Da sauri ya ruggumota ganin yadda taketa tsalle kawai sai yaga ta fara mammanna mishi kiss tako ina najikinshi. Sam ta kasa cewa komai ganin haka sai ya fara zame mata kayan jikinta, bata bi ta kanshi ba bare ta hanashi sai ma k'ara mak'aleshi tayi cikin fizgo mgna tace. "Al'bishirinka Ya Ahmad." cilla rigarta gefe yayi tare da had'e jikinsu wuri d'aya kana yace. "Goro fari k'al." kiss ta manna mishi a goshi sannan tace. "Jikin Hamma Saifuddeen da sauk'i ya shida kanshi ya tashi zaune ba taimakon kowa." Wata iriyar amintacciyar rugguma Ahmad yayi mata tare da giggicewa gaba d'aya ya abka mata, bata da zabi dole ta karb'eshi a yadda ya zo mata, mgna d'aya sukayi ta maimaitawa juna, "Hamma Saifuddeen ya fara workewa yana zama da kanshi." shi kuma sai yace. "Alhamdulillahi ya Allah mun gode maka ka nuna mana ranar da zai kuna tsayuwa da sawunshi." A haka dai sukayi ta kabta nanayensu. Ummi kuwa wayarta ta d'auka ta gaya dukkan 'yan uwa da abokan arziki. Adda Rahma kam kawai sai taje gaban surkarta tana kuka tana sanar da ita, cikin kula tace. "A a Rahma to ai wannan abin farin cikine bana kukaba Allah zamu godewa." A gefen Raihana ma haka abin yake, dan ita cewa ma tayi dole Saminu ya kawota gida gombe. Su Salisu, Mudassir, Warisu, da Bappa Ali kuwa duk Ahmad ya sanar dasu. Ummi da kanta ta kira Ishaq ta sanar mishi. Kai wannan rana wannan safiya tazowa da masoyan Saifuddeen da daddad'an labari da sanyin safiya. Kafin zuwa shabiyu duk makota da 'yan uwa anata zuwa yiwa Ummi barka. Bappa Alima yazo da Aunty Nina da Goggo Dada maman Ahmad, Shi kuwa Hayatuddeen sanin bazasu barshi ya shiga bane ya sashi komawa ya d'auki wayarshi, aifa kusan a Jere a jere kiran abokan Hamma Saifuddeen da k'annenshi ke shigowa wayarshi, Haka ya zauna yana musu cikekken bayani yadda komai ya faru, sai ya k'ara da ce musu yanzu an shiga dashi wani d'akin. Haka dai yayi ta zaman jira, Abu wasa-wasa har azahar ba'a fito da Saifuddeen ba, Ganin haka ya kira Dr Aliyu ya sanar mishi abibda ke faruwa, sun gama mgna da Dr Aliyu kenan sai ga Dr Acash prasat ya shigo inda yake cikin tsananin jin dad'i ya ruggume Hayatuddeen kana ya jawoshi suka zauna cikin kula yace. "Hayatuddeen jinya tayi kyau komai yana tafiya yadda mukeso Alhamdulillahi yanzu alamomin samun sauk'i sunata k'ara baiya a wurin d'an uwanka, tun d'azu muna tare a kanshi duk wani bincikenmu yana bamu tabbacin kaso saba'in cikin kaso d'ari na cutar ya worke a koda yaushe Saifuddeen zai iya tashi tsaye da sawunshi. Yanzu kuma Alhamdulillahi zai iya tashi zaune daga konce, kuma zai iya juyawa hagu da damanshi. Sannan zai iya durk'usawa kan guiwowinshi, kai nan gaba kad'an ma zai iya sunkuyawa, shine zatonmu a binciken da muketa gudanarwa a kanshi. So yanzu ka kwanrar da hankalin ka koma masauk'inka dan sai gobe zaka kuma ganinshi." Cikin gamsuwa da jin dad'i Hayatuddeen ya gyad'a mishi kai tare da cewa. "Thanks Doctor." sai ya mik'e cikin jin dadi har zai fita sai Dr Acash ya jawo hannunshi gaban wani window ya kaishi tare da cewa ya lek'a. Hammanshi ya hango cikin wata na'ura mai girma dan k'afafunshi kadaine a woje sai kanshi kad'an. Cikin bashi k'arfin guiwa Dr Acash yace, "Wannan shine taimako na k'arshe da akeyi masu irin larurarsa, Yanzu sai in an fiddashi sai bayan, wata shida za'a sake sashi, so nanda one month za'a sallameku, in zaku iya duk bayan 6 months sai yazo a dubashi, a k'ara canza mishi drugs d'inshi. So ka kontarwa iyayenku hankalin kada wani yace zai zo." Tofa wannan abu shine Noor ala noor haske kan haske, sosai bayanin ya kontarwa Hayatuddeen hankalin. Shiyasa cikin k'arfin guiwa ya koma masauk'inshi. A ranar dai kam wannan family sunyi matuk'ar shiga farin ciki. Musammam Ummi da Hayatuddeen ya mata bayanin likita, kawai sai takeji kamar bata da wani sauran damuwa a duniya. Hakama Dr Adnan da yaji bayani a bakin Dr Malik Khan sosai ya samu konciyar hankalin. Ahmad kuwa a ranar ya nemo ma'aikata sukazo suka gyara side d'in Hayatuddeen dan Ummi tace anan Saifuddeen zai zauna, So an fasa duk wani wuri mai d'an tutu ko steps

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148