Chapter 146
Chapter 146
ta dinga sake zafafan waƙoƙi na soyayya masu taɓa zuciya, wani waƙan idan tasaka har ƙwalla ne ke bin ƙuncinta, domin sosai suke ratsa mata zuciya. kai ta jinjina tare dacewa. "Ganin lokaci na hararanmu a gurguje ga zazzafan sak'o na masoyo, wanda shine na kusa da k'arshe. sai kuma ta saki wak'ar K'anina Hamisu Breaker tare da k'ara volume. A hankali Wak'ar ke tashi. Tun forkona duniya an dasa so bisa zuciyar mutun biyu. kuma har abadan bazai yankeba dan yanada armashi. sai ta kuma d'an rage volume d'in tare da d'aga muryarta tana bin wakar yadda sautin ke fitowa tare cikin rauni take bin baitukan. "Soyyyy ruwan zuma inji wasu, wasuko sukace ruwan gubane." haka tai tabin wak'ar har k'arshe kana tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa. "Ganin lokacin da aka d'ibar mana ya k'are ga wak'armu ta k'arshe." wak'ar isa ayagi. Duk masoyi zai jure karan tsan." sai kuma ta d'an k'ara sautin muryarta tare da bin mawak'in inda yake cewa. "Zaya jure kai kawo ko ina, zai nufin masoyinsa da hassada. Ba'ason fushi sai dai dangana." sai kuma ta dai-daita muryarta da mawak'in suka had'a baki wurin cewa. "Yin fushi a so tono fittina, wanda ya fara so baishiga yak'i na kanganba." sai kuma tayi maza ta katse wak'ar dan sai taji kamar Saifuddeen take bawa k'arfin guiwa, tana ƙare shirin nata ta fito. Balkeesu ce ta karɓa don itace zata gudanar da labaran duniya, bayan tagama gabatar da labaranne ta gyara zama, cikin isgilanci tace. "Kanun Labaran duniya da ɗumi ɗuminsu.mun samu wani labarin mai cike da al'ajabi daga wata majiyarmu mai taken Babu nakasasshe sai rago, cewa soyayya ta ɓarke tsakanin masu lafiya da kuma nakasassu, inda shahararriyar matashiyar budurwa maiji da kyau, ilimi, wayewa, haɗi da aji tayi gamdakatar da wani nakasashshen kurma, kana gurgu, inda yazo ya bayyana mata soyayyarsa hartakai ga suna ƙoƙarin yin aure, mudai fatan mu anan shine Allah yaƙara danƙon ƙauna da soyayya, domin ai Nasaka ba kasawa bace, kuma babu nakasasshe sai kasasshe!." taƙare maganar tana me ƙoƙarin gimtse dariyarta. Zaleeha dake zaune aɗakin watsa shirye shirye tanajin abun da Balkeesun ta faɗa, taji ranta yayi wani irin ƙuna, take ɓacin rai ya cika mata zuciya, sam bata tsammaci haka daga Balkeesu ba abinda taketa boye shine take son sanarwa duniya. Jakarta ta ɗauka tare da miƙewa tsaye batajin zata iya jure zama awajen aikin, saboda haka tafiyarta gida shine kawai zaifi. Tana fitowa, tayi kiciɓus da Balkeesu, tare da wani Hamza wanda yake shima abokin aikinsu ne, Hamza irin mutanen nanne masu gulman tsiya da kuma shishshigi, gason shiga abun dabai shafesa ba, shiyasa ma sam basa shiri da Zaleeha. Yana ganin Zaleehan yasaki dariya tare da dubanta da kyau, cikin son ƙarin jin gulma don wanda Balkeesu ta gulmata masa bai ishesa ba yace. "Zalees fashion amaryar nakasasu, anguji masu lafiya an ƙare a nakasassu." Cak ta tsaya da tafiyan da takeyi tare da juyowa ta watsa masa wata uwar harara, bata da lokacin tanka masa hakan yasa ta juya taci gaba da tafiyarta. Dariya suka ci gaba dayi shida Balkeesu, ita kuwa ko sake waiwayosu batayi ba. Kaitsaye wajen motarta ta nufa, tana shiga ta murza wa motar key tare da cillata kan titi, kanta ne ke mata ciwo sosai, gaba ɗaya damuwa ya cika zuciyarta, har wani ɗaci takeji aranta. Baba malam ne zaune a falonshi bayan tafiyan iyayen Abdussalam wai sun kawo sadakinsu wa Zaleeha kuma wai masu kawo kayan aurenma suna kan hanya, Malam Adam ne ke tausarsa da cewa. "Malam Bashir ka kwantar da hankalinka domin al'amarin yaran yanzu sai du'a'i." cikin tsananin b'acin rai da tarin bak'in ciki murya a hargitee Baba Malam yace. "Me Zaleeha take son maidani da zatayi ta turomin manyan mutane masu daraja a kanta ita d'aya, da kaifa muka amshi sadakin Saifuddeen a hannun mutane masu kima da daraja, sannan yanzu ta kuma turo min wasu, biyu za'a rabata ne? ga uwarta ita ma sai tayar min da hankali takeyi." cikin tausasawa Malam Adam yace. "Kada ka damu tunda su iyayen Abdussalam mun basu hak'uri mun kuma ce musu kada su bari a kawo kayan lefensu ai inaga sun fahimcemu." kai ya jujjuya tare da cewa. "Banga alamun hakaba a fuskokinsu, bakaji cewa suke ai dai da fari nine na bawa d'ansu damar zuwa zance wurinta, kanaji har cewa sukeyi wai in dai daure inyi dottaku kaji fa abinda Zaleeha ta jaza min zubewar mutunci da kima da dottaku a idanun mutane." "Ba komai in sha Allah, bari inje gida anjima zan dawo inyi mgna da ita Zaleeha ka kwantar da hankalinka." Da haka Malam Adam ya sallami Baba Malam ya tafi ya barshi cikin tarin bak'in cikin abinda Zaleeha da Mama keyi mishi... Ita kuwa Zaleeha kaitsaye ta fara zuwa Makay ice cream and chocolate ta saya, daganan ta ɗauki hanyar komawa gida. Tun daga shawo kwananta ta hango wata ƙatuwar mota tirela fake aƙofar gidansu sai ya Habu dake kusa da masu motar alamun suna mgna dashi kamar dai umarni yake basu kan su dena fidda kayan bisa dukkan alamu jagoranci ko kwatancen wani wuri yake musu inda zasu kai kayan. Abakin tangamemen gate ɗin gidannasu tayi parking, buɗe murfin motar nata tayi ta fito nan tashiga bin kayayyakin furnitures ɗin da ake shigarwa cikin gidannasu da kallo, mamakine bayyane akan fuskarta haka ta wuce zuwa cikin gidan. Kai tsaye ɓangaren Mamy ta nufa, nan ta iske su Zahira da Ziyada zaune gefensu kuwa Mamyne hannunta riƙe da littafin hisnul muslim. Wurga jakanta tayi kan kujera cikin gajiya ta dubi Mamy ashagwaɓe tace. "Barka da gida Mamy." Dubanta Mamy tayi tare da cewa. "Yauwa Zaleeha ya aikin." "Alhamdulillah". tafaɗa tana me ƙoƙarin buɗe ledar ice cream ɗinta, zaro roban ice cream ɗin tayi tare da buɗewa, harta sanya ɗan ƙaramin cokali cikin ice cream ɗin sai kuma ta ɗago kanta duban Mamy tayi cikin son ƙarin bayani tace. "Mamy naga anata shigo da kayan furnitures gidannan, Baba ne zai sanja kayan part ɗinsa ko?" ta k'arishe maganar tare da cika bakinta da daddad'an sassanyan ice cream d'in Kafun Mamy tayi magana tuni Zahira tayi carab ta cabke maganan inda tace. "Kayan furnitures ɗinki ne na aure wanda Ya Ahmad yayi miki order daga Dubai shine suka iso." Tuni ta ƙware da ice cream ɗin dake cikin bakinta, wani irin tari me ƙarfi ne ya sarƙafemata wuya da numfashi, take idanunta sukayi jajur, tari take sosai, har saida su Mamy suka tsorata, Ziyada ne tatafi kitchine da gudu inda ta dawo hannunta ɗauke da bootle water, Mamy ne ta karɓi ruwan tare da ɓalle murfin goran ta kai bakin Zaleehan, sosai tasha ruwan, saida taji ta rin nata ya tsaya sannan ta kawar da goran daga bakinta, zamowa ƙasa tayi daga kan kujeran tare da fashewa da wani irin kuka, kuka take sosai kamar wacce aka faɗawa ranan mutuwarta, Mamy da su Zahira baki kawai suka sake suna kallonta. Cikin kuka ta mirgino tare da kama ƙafafun Mamy, cikin matsanancin kuka tace. "Mamy dan Allah Kifaɗawa Baba Malam cewa banason wannan auren, wallahi na tsaneshi, matuƙar aka aura mini shi kashe kaina zanyi, wallahi dana aureshi na gwammace mutuwata!" Ajiyar zuciya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148