Skip to content

Chapter 129

Chapter 129

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

ya nufi wurin mai gadin, hannu ya bashi suka gaisa sannan yace mishi ya shiga cikin gida yace bak'in sun iso. Cikin mutuntawa mai gadin yace to tare da juyawa ya shiga cikin gidan. Jim kaɗan ya fito yace. Ance su isa. Nan duk matan suka shiga su kuma mazan duk suka zauna cikin motocin. Suna shiga cikin gidan Maryam tayi musu jagora har babban parlour Mama duk da bata nan dole a bata matsayinta na uwa. Bayan sun zazzauna, an gaisa cikin mutun taka, an kawo musu drinks da snacks, sun ɗan taɓa abin sha. Hajia Rabi ce ta gyara zama tare da cewa. "Raliya je kice Imran Suleiman da Hayatudeen su shigo da kayan." A hankali ta mik'e tare da cewa. "To." A tare suka shigo duk suna riƙe da akwatuna harda ma'aikatan gidan, haka suka dinga shigowa da haɗaɗɗun akwatunan cikin falon, saida suka ƙare sannan suka juya suka fiti suna haki, dan sosai akwatunan suke da nauyi kasancewar kowanne ashaƙe yake da kaya. Aunty Kubra ce ta kalli Raliya dake riƙe da ɗan Maryam tana mishi wasa, tace. "Ke ƙanwar ango ai bakici ta zama tashi ki nuna musu kayan." murmushi tayi tare da cewa. "To Aunty Kubra amman dai a tayani." Murmushi sukayi baki ɗaya ganin yadda taketa kiciniyar bubbude akwatunan, tare da cewa. "Wannan turamene a ciki wannan laces, wannan shadda wanna boyel." sai kuma ta fara jawo na ƙananun kaya dana kayan shafa wanda ta buɗe akwatuna biyu wanda suke cike maƙil da ababen shafawa na kwalliyar jiki irin na mata. Da sauri Mommy matar Malam Adam tace. "Masha Allah. Gsky ki huta kawai, wannan ai yafi ƙarfinki muma masu gani har mun gaji, wani abun ai bazai ganuba, sai dai muce Allah ya sanya al'khairi yasa al'barka a ciki." Aunty Lubna kuwa kai kawai take jinjinawa domin idonta ya raina fata, nakasasshen da ake zatawa riƙe ƙoƙon bara da bin kwararo lungu da saƙo yana allazi wahidin, shine da wannan kayan lefe wanda ita dai a iya ganinta lefen Zahra buhari ne kawai ta taɓa gani wanda zatace yafi wannan, a dai gani da idonta. Goggo Maryama kuwa tausayi suka bata ganin irin ruwan dukiya da suka binne a kan yarinyar da ta sani tabbas uwarta bazata barta ta zauna a gidan Saifuddeen ba. Mamy ma tabbas tausayinsu taji ganin yadda sukayi ɓarin naira. Maryam kuwa sai addu'a takeyi a ranta tana cewa. "Ya Allah ka rufa mana asiri, ka hana mahaifinmu jin kunya da tozarta, ya Allah ka tausasa mana zuciyar wannan baiwar taka Zaleeha kasa tayiwa mahaifinmu biyayya ta zauna lfy da mijinta da yan uwanshi." sosai Maryam ke jin tsoron abinda zai zubarwa mahaifinsu darajarsa da mutuncinsa. Adda Rahamace ta ɗanyi dariya kana ta jawo ɗan kit ɗin da saraƙuna suke ciki, ta buɗe babban gwal ɗin da Saifuddeen ya saya a India ta zaro ta miƙawa Mommy dake kusa da ita cikin sanyi tace. "To ga wannan ko za'a adanashi da ban, duk da cewa sauran ma gwala gwalaine amma shi tsadansa dabanne." sosai Mommy ta girgiza da girma da darajan gwal ɗin, mai surki da ruwan farin zinari. amsa tayi tare da miƙawa Mamy, mamakinsu ya ƙaru ne lokacin da Aunty Kubra ta miƙawa Aunty Lubna car key ɗin kia d'innan tare da cewa. "Ga wannan Key d'in motar amaryarmun ce, motar tana nan waje. zuwa yanzu fa Mamy abin ya fara zarta zatonta cikin dattaku da nitsuwarta da iliminta tace. "Anya kuwa, gsky Malam zaiyi faɗa in muka karɓi abubuwan nan, ko lefen ma in ya gani zaiyi faɗa." Da sauri Goggo Dada da Aunty Kubra sukace. "Dan Allah da manzonsa kar muyi haka daku, Saifuddeen bazaiji daɗiba tunda shi ya gani zai iya yiwa matarsa komai, kuma abinda nanda wani ɗan lokaci ta zama matarsa." Murmushi Aunty Lubna tayi tare da cewa. "Kuma shi za'ayiwa kolliyar ba." Ta ƙarishe mgnar tana kallon Aunty Kubra wacce bazata wuce sa'arta ba. da sauri Aunty Kubra tace. "Ato kunga ai kanshi yayiwa tanadi, mutun da matarsa." Goggo Maryama ne tace. "To mu dai tunda kunce dan Allah da manzonsa to zamu amshi kayan, saura mgna kuma tana wurin Yaya Malam." Hajia Rabi ce tace. "Shima anjima da dare za'a kawo sadaki fatanmu Allah yasa, a saka bikin nanda mako ɗaya." Amin Amin sukace baki ɗaya. Maryam ce tace. "ai kam naga alaman Saifuddeen ya zaƙu yana son matarsa nan kusa tunda gashi harda kayan rufi kuka kawo." Cikin sakin fuska Adda Rahma tace. "Sosai makuwa ,ai shi ko yau ya sameta yana so." Daga nan suka ɗan taɓa hira sannan suma miƙe tare da cewa. "To mu zamu tafi sai kuma in munzo ɗaukan amaryarmu." Da sauri Mommy ta kalli Maryam da Lubna ta musu alamun su ɗauko food flasks ɗin dake cike da ababen mƙulashe. Ganin sunata cika musu kulolin a gabansu yasa, Goggo Dada cewa. "wannan abu yayi yawa ku barshi." da Saudi Goggo Maryama tace. "A a ai yaba kyauta tukuici, ku barmu muma muyi iya iyawarmu." Hajia Rabi ce ta kalli Mommy matar Malam Adam dake miƙa mata damin kuɗin tukuicinsu rafa guda shida yan dubu daddaya. A hankali tace. "Hajia wannan kuɗin kuma na menene duka?." Cikin salon girma ba batun ƙaramta Mommy tace. "Yaba kyauta tukuici, ba ku muka bawa ba yaran da suka shigo da kayan muka bawa." Akan dole su,suka karɓa, nan Aunty Lubna taƙira biyu daga cikin masu aikin gidan Baba Malam ɗin suka shiga jidan food flask ɗin suna kaiwa cikin motocin da su Adda Rahama suka zo dashi. Har bakin gate suka rakosu baki d'ayan su, aka rabu cikin mutunci da jin dadi. Bayan sun koma cikin gida ne, Aunty Lubna ta kalli Maryam tare da cewa. "Ke zo muga kayannan da kyau,". Dariya Maryam tayi kana ta matso ta fara bubbud'e akwatunan, Mommy, Mamy, goggo Dada kuwa suma zama sukayi suna kallon kayan d'aya bayan d'aya. yayinda tuni Aunty Lubna keta viewing tana d'aukan komai a zazzafar wayarta. Sune basu gama ba har aka kira sallan magrib, dole suka hak'ura suka k'arisa kallon a gaggauce kana suka rufe komai, suka shirgeshi a cikin d'akin Mama, kana duk sukayi al'wala dan gabatar da salla. Bayan sunyi sallah harda na isha, sukaci abinci, sukaci gaba da hira, dan Maryam jira take mijinta ne zaizo ya d'auketa hakama Mommy Malam Adam ne zaizo ya d'auketa, Goggo Maryama kuwa Ya Ahmad ne zai maidata gida. Baba Malam kuwa, tunda yamma yake gidan Malam Adam, dan amaryarshi bata zoba. Ya Ahmad kuwa da Ya Aminu tunda safe suka tafi dukku kai ziyara dan Ya Ahmad ya kusa komawa Abuja. Saida akayi sallan magriba suka dawo, Kai tsaye parlour'n Baba Malam suka nufa, nan Maryam ta kawo musu abinci, bayan sun gama cine sukayi al'wala suka nufi masallaci a nan suka samu Baba malam da Malam Adam. Koda aka idar da salla tare suka shigo cikin gida. Suna shiga bada dad'ewa ba, Dirankadi da Bappa Ali da Malam Ashiru suka iso harabar gidan. Dirankadi ne ya kira Baba malam ya shaida masa isowarsu, jin haka ya kalli Ahmad tare da cewa. "Ahmad tashi kaje ka shigo da iyayen Saifuddeen." Cikin tsananin girmamawa da sanin darajar mahaifa Ahmad yace. "To." sannan ya miƙe

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148