Skip to content

Chapter 116

Chapter 116

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,204 words 0 views Progress saved
Download Book

tab'a yarda yanada matsalar spinal cord injury ba. mik'awa Baffa Ali wayar yayi, tare da maida hawayen tausayin Saifuddeen da suka cika masa idanu, kana a hankali yace. "Shin zai iya aure har ya iya kusantar mace har in Allah ya nufa su samu haihuwa!?." Wani sassanyar ajiyar zuciya Baffa Ali yayi kana ya, musu duk cikekken bayanan da doctors sukayi musu ya k'ara da cewa. "Likitoci sun bamu tabbacin cewa zai iya aure harma da haihuwa, domin nakasarsa bata shafi jijiyoyin mazantakarsa ba. Kuma ko jiya da sukaje suka sameni da batun saida na kuma tambayarshi batun lafiyarshi. Ya bani tabbacin shifa baida matsala ko kad'an." Jin haka yasa Baba malam yin murmushi tare da cewa. "Alhamdulillahi, na bawa Saifuddeen dama yazo ya gabatar da kanshi a wurin Zaleeha, in dai tayi mishi to in sha Allah Zan bashi ita." Wani matsainacin farin cikine ya rufesu baki d'aya, Aminu da Ahmad ma sun aminta da Saifuddeen, domin suma ai basu san k'arshensu ba. Malam Adam ne ya gyara zama tare da cewa. "An bashi dama yazo ya gabatar da kanshi, fatanmu Allah ya dai-dai-ta tsakaninsu." "Amin Amin." Sukace baki d'aya kana, daga nan suka ɗan taɓa hira, daga bisani su Baffa Ali suka mik'e da niyar tafiya, Har bakin gate wurin motocinsu, Baba malam da abokinshi Malam Adam dasu Aminu sukayi musu rakiya. Kai tsaye gidansu Saifuddeen suka nufa, Wanda yake zaune a falon side ɗinshi shida Ahmad da kuma ishaq, hira suke amman gaba ɗaya hankalinshi baya kansu, duk tunaninshi naga su Baffa Ali, tsoro yakeji kar suje ace musu anyi mata miji. Ahmad ne ya kalleshi tare da cewa. "Wai mene sai kayi wani shiru, in ma an bada ita, ai akwai wasu matan." Hararanshi yayi tare da girgiza mishi kai, kana ya mishi alaman "Itace muradin zuciyarshi, kuma abincin ruhinshi." mik'ewa Ahmad yayi cikin yin dariya kana yace. "To nama jiyo muryar Baffa Ali a parlour ku taho muje muji dame suka dawo." Kusan a tare suka fito, yayinda Saifuddeen yaketa musu kallon nazartar fuskokinsu. Murmushi yayi ganin Dirankadi na cewa Ummi. "Alhamdulillahi tafiya tayi kyau, abuma duk namune." wani irin sassanyan ajiyan zuciya Ummi tayi tare da cewa. "Gidan mutunci ne ko?." Da sauri baffa Ali yace. "D'iyar Bashiru nefa d'an abokin babanmu, kin tuna malamin su Saifuddeen na islamiya?." Da sauri Ummi tace. "La Bashir kam ai bazan mantashi ba, lokacin da muke karatu su sunyi sauk'a, kusan sune manyanmu a wurinsu muke biyawa in kawu baya kusa." Cikin dariya malam Ashiru yace. "Ato baki mance mu ba ashe." Kai ta gyad'a cikin jin Kunya dan tuno k'uruciya. Dirankadi ne yace. "To Zaleeha d'iyarshi ce ai?." Ahmad ne yace. "La Zaleehan Malam Bashir ce? D'alibar Saifuddeen lokacin in bashine zai bata haddaba sam bata tab'a iya kawoshi dai-dai." Sai ya kuma juyawa ya kalli Saifuddeen da ya kauda kanshi kamar ba shiba. Baffa Ali ne ya shafa kanshi, tare dayi mishi cikekken bayanin irin tarbar da suka samu, da irin karra masu da akayi, da kuma basu izinin ya fara zuwa zance duk sanda ya shirya. Wani irin tarin farin ciki yakeji a ransa, a fili kuwa sai hannu ya bawa Dirankadi da Malam Ashiru tare da yi musu alamun godiya da jinjina. sosai Ummi ke lura da irin yadda fuskarsa ke cike da farin ciki, Amman kunyarsa ta boye hakan. Sosai sukaji daɗi daga nan Ahmad ya ɗauki su Baffa Ali ya maidasu Dukku, Ishaq kuwa yabi babanshi suka tafi. Bayan duk sun fitane, Saifuddeen ya sarrafa whellchair ɗinshi har zuwa gaban Ummi dake tsaye, yana isa inda take ya ruggumeta cikin farinciki da salama. Murmushi tayi itama tare da tallafo haɓarshi cikin son abinda ɗan nata keso tace. "Allah ya sanya al'khairi a cikin wannan lamarin naka, Allah ya shige maka gaba ya tabbatar maka da ingantaccen farin ciki!!." A saman lips ɗinshi ya amsa da "Amin Amin my Ummi." Sai ya kuma sarrafa whellchair ɗin nashi ya nufi falonsa. Ummi kuwa da sauri ta haura sama, inda Hayatuddeen ya tasa Raliya a gaba ala dole sai ta share mishi d'akinshi. A parlour ta samesu ita tana shara, shi kuwa yanata zuba mata surutu, hannunshi rik'e da pillet d'in kifin margi special yanaci yanata zuba mata zance, kana yana watsar da k'asusuwan a bayan inda ta share. Cikin gajiya tace. "Wlh na gaji Ummi autanki zai samin ciwon baya dana kunne, duk inda na share yana b'atawa kuma ya cikamin kunne da surutu kamar kabari." Baki ya turo gaba tare da cewa. "Ummi wai dan ina bata labarin wata mawaƙiya, Asma'u Ahmad Matawalle ce da take son Hammana kamar ta mutu, ɗazu muka gama waya da ita wai in gaisheki." Cikin mamaki Ummi tace. "Mawaƙiya kuma?." "Eh" Yace yana lumshe ido tare da kurb'ar juice d'in dake hannunshi. Kauda zancen Ummi tayi da cewa. "Su Baffanku sun dawo harma sun koma." Cikin tsalle Hayatuddeen ya diro daga kan firijin da yake zaune tare da wurga kwalin juice d'in yace. "An bawa Hamma na ita ko yaushe ne auren?." Cikin dariya Ummi tace . "Oh ya Allah ka kimtsa min autana ya zama nitsastse kamar Saifuddeen." Jin Raliya na cewa. "Ummi an bashi izini zuwa zancen?." Cikin gyad'a kai tace. "Eh an bashi sosaima suka samu karramawa, d'iyar Malaminshi nefa Malam bashir, wanda kuma yake shirin Hanyar tsira na gidan radion vission FM." Tsalle Hayatuddeen ya kumayi tare da cewa. "Yanzu kuwa zan tafi gidan Adda Rahma inje musha hira." Kafinma su ankara tuni ya fice abinsa. Nan Raliya ta samu daman gyara mishi ɗakin nashi. Ummi kuwa falonta ta dawo ta zauna taci gaba da karatun da takeyi. Shi kuwa Saifuddeen dake zaune akan lumtsuma -lumtsuman sofan dake falonshi, gyara zamansa yeyi. Wayarshi ne a hannunshi da alamu hira yakeyi da ishaq. "Kai yaro kaji dai ko mun samu karɓuwa. Yanzu yaushe zamuje ne dan gabatar da kanmu?." Cikin tsokana Ishaq yace. "Sai next week ko?." Da sauri ya rubuta mishi. "Kayi hauka ne, ai zuciyata zata narke kafin nan." Dariya sosai Ishaq yayi kana yace. "To yaushe zamuje?." Cikin gyara zamanshi yace. "Anjima da yamma zamuje, kafin nan Ahmad ya dawo." Dariya Ishaq ya kumayi kana yace. "A a sarkin sauri, gsky ka bari sai gobe da yamma. Dan yau zata gabatar da program ɗinta na mushaƙata." Badan ya soba sai don dole haka ya haƙura. 6:00 pm. Zaleeha ce ke cikin ɗakin watsa shirye-shiryen su. Zamanta ta gyara bisa kujerar da take kai, tare da ɗan rage sautin waƙar da tasa, kana cikin irin muryarsu na ma'aikatan gidajen radio tace. "Assalamu alaikum, al'ummar jihar gombe da kewaye, barkanmu da war haka sannunmu da sake saduwa cikin shirin Mushaƙata, tare dani Zaleeha Bashir Sulaiman Dukku." Sai kuma ta ɗan dakata tare da ƙara sautin waƙar nan ta. Nura M Inuwa mai taken. "Kaso a soka yafi ƙawance cika taso a soka kanaso." sai kuma ta ɗan range sautin tana mai bin waƙar, yadda ake iyajin muryarta dana mawaƙan na tafiya atare. Raveel dake ɗakin kula da shirin dake fita, dariya yayi domin yasan dashi da manager akeyi. Ita kuwa Zaleeha tuni shauƙin sonshi ya rufeta, saboda zafafan waƙoƙin so da take sakawa. Cikin shauƙi ta katse wata waƙan Nura M Inuwa

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148