Skip to content

Chapter 66

Chapter 66

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
Download Book

bamu sa'an aiki, kana kasa a ranka nakasa ba kasawa bace, ka jajircewa zuciyarka, kasa a ranka wannan jarrabawace da ubangiji kan iya jarabtan dukkan bawanshi, kaga misali a kaina gani bana iya mik'ewa tsaye kuma rana tsaka larurar ta sameni sakamakon had'arin mota, wanda lokacin ina ganiyar k'uruciya ta, na gama karatu na kenan na fara aiki da mako biyu nayi hatsarin, wanda saida akayi tsawon shekaru biyu ana jinyata kafin na fara tashi zaune da kaina, kumani a lokacinma nakasata ta shafi lafiyata a matsayina na d'a namiji, koda na yarda da k'addara, nasan cewa jarrabawace bayan shekara 8 da faruwar abun lfyar mazan takana ya fara dawowa cikin ikon Allah kafin na cika 10 years da yin had'ari har nayi aure sai da muka shekara 7 da ita kafin Allah ya bamu ciki a lokacin har na cire tsamnani, Allah da ikonshi ciki nada wata 5 ya bare. Nayi matuk'ar shiga damuwa a lokacin ashe abinda bamu saniba, cikin tagwaye ne d'ayan nan bai bareba, bayan wata hud'u aka haifa min d'iya mace, daga kanta kuma Allah bai bamu waniba, to nima kenan da nakasata tafi taka in sha Allah kai muna sa ran zaka samu lfy kuma Alhamdulillahi kaga kai matsalar bata shafi mazantakan kaba. kasa a ranka kana nan da lfyarka." kai ya rausayar tare da lumshe ido kana ya gyad'a kanshi kai alamar. "To, ngd." daga nan suka fara aikinsu ba kama hannun yaro, babu mgna sai nuneneniya, tuk'uru suka duk'ufa kanshi. A can waje kuwa Ummi aje carbin hannunta tayi kana ta jawo wayarta ta fara karatun qura'an tanayi tana nemawa gudan jinin ta lfy a wurin mai rayawa mai kashewa mai badawa mai hanawa, Allahu wahidun k'ahharar. Ya Rabi'u kuwa ya d'auki Aunty Mami sun tafi ya maidata gida, dan tayiwa bak'in nasu abinci, kana shi kuwa ya wuce ma'aikatansu. Ishaq kuwa da Ahmad suna nan zaune suna dakon fitowan doctors dan suji menene matsalar Saifuddeen d'in. Kana Hayatunddeen kuwa ya tafi Airport dan tarbo Dr Adnan. Bayan kamar awa biyu suka fito a jere, Dr Ayman yana turawa weelchair d'in da Dr Aliyu ke zaune, yayinda, Dr Batulu ke biye dasu a baya. Suna fitowa Dr Adnan da suka ise bada jimawa ba, ya mik'e da sauri, ya nufi inda suke hakama Ahmad da Ishaq wanda kunnuwanshi ke mishi jagora duk inda sautin muryarsu da sautin takun Ahmad yake bi, kai baka tab'a cewa makaho bane, domin mutunne mai cikar zarrah da zati kekyawane mai tarin tsabta da yawa sukance suna ɗan kama da Saifuddeen. cikin girmamawa Dr Adnan ya d'an rusuno ya bawa Dr Aliyu hannu tare da cewa. "Barka da hantsi sir." cikin kula da dottaku Dr Aliyu yayi murmushi irin nasu na manyan doctors kana yace. "Barka dai Adnan ashe har ka iso, ya hanya." "Alhamdulillahi ya aiki?." Adnan yace yana bin bayansu shida Ishaq da Ahmad suka shiga tamfatsetsen office d'in Dr Aliyun. Ummi kuwa addu'a tayi kana ta kife wayar bisa cinyarta, ido ta zuwaba Hayatuddeen dake tsaye gaban Dr Batulu yana neman a barshi ya shiga yaga d'an uwan nashi. cikin kula tace. "Kayi hak'uri bayan mun gama aikin bashi taimakon gaggawa an mishi allurar bacci so ana buk'atar ya huta." sai ta kuma matso gaban Ummi da idanunta suka cika da hawaye, ganin tazo gabanta Ummi tace. "Dan Allah Dr ki gaya min halin da yake ciki? koda baya rayene kada ki boye min, tunda abinnnan ya farufa bangashi ba sai dai in haggoshi daga nesa, ke uwace kinsan abinda uwa kanji in makamancin wannan ya faru da d'anta please me ya sameshi?." a hankali Dr Batulu ta zauna gefenta kana ta dafa kafad'arta tare da cewa. "Abinda ma muke zaton zaiyi tsanani sai muka sameshi da sauk'i, Saifuddeen bai mutuba yana raye kuma insha Allah da yamma ni da kaina zan shigar dake inda yake, kafin nan ya farka zaki ganshi ya ganki kuyi mgna dashi, yanzu dai da ku koma gida domin nan akwai masu kula dashi. wadanda Dr Aliyu ya tanatar su zasu mishi komai, sannan batun abinci ma karku damu akwai d'iyar Dr d'in duk abinda za'a bashi damar ci ita zata shirya mishi komai. Yanzu kuje gida da yamma Ku dawo,zaku ganshi kuma Dr Aliyu zai gaya muku duk abinda ke damushi da matakin daya kamata ku dauka dama yadda zaku kula dashi." sosai Ummi ta gamsu da bayananta kana taji sanyi a ranta, haka yasa tace. "To ba matsala ngd matuk'a Dr in sha zanyita addu'a zamu koma biyar na yamma zamu juyo." cikin fara samun nitsuwa Hayatuddeen yace, "Dr zai gane mu ko? numfashi sa ya dai ta ko?." kai ta gyad'a mishi tare da cewa. "Sosai ma har magna fa yanayi mana da body language alamun yana gane duk abinda muke cewa." a tare sukace Alhamdulillahi. sannan Dr Batulu ta bawa Ummi number ta kan in sun dawo da yamma su nemata. Su Abban Farida kuwa, da Dr Adnan da Ishaq bayasu shiga sun so Dr Aliyu yayi musu bayanin matsalar Saifuddeen, so amman sai ya basu hak'uri sabida ya gaji yana buk'atan hutu ya dai ce suje da yamma su dawo dukansu yana son ganinsu dan zai musu cikekken bayanin matsalar Saifuddeen d'in da basu shawara da da gaya musu dabarun kula dashi. dole suka hak'ura kan saida yamman in sun dawo. Kai tsaye gidan Ya Rabi'u suka wuce dan Ishaq ya k'i su Ahmad da Adnan suje su kama hotel. A motar da Ya Rabi'u ya bari a hannun Hayatuddeen suka tafi, amman Ahmad ya karb'i tukin a cewarshi Hayatuddeen d'an koyone bazai yarda ya jasuba, Ummi na gaba kusa da Ahmad kana Ishaq da Adnan da Hauatudeen suna baya a haka suka tafi. Aunty Mami kuwa tuni ta shirya musu abinci tasa an gyara BQ ensu. *A garin Gombawa d'iban fari* Yau tunda sanyin safiya Zaleeha ta shirya domin zata je kaltingo don zantawa da nakasassun wannan yankin. Amman har zuwa ƙarfe taƙwas na safiyar ta gaza yin komai, ji takeyi tamkar tayi ta kurma ihu ta faɗi abinda folisawannan suka haneta faɗi tare dayi mata barazana da ranshi, kukan da takeyi ya sanya ida nunta kumbura sukayi jazir ga wani fitinennen ciwon kai, ya zatayi a duniya ko wacw ƴa in tanada matsala uwarta take fara tinkara ,amman sam Mama itama bayan folisawan tabi. tafin hannunta tasa ta share hawayenta a karo na barkatai, a hankali ta miƙe kana ta zari car key ɗinta, a falo ta samu Mama a hankali ta gaiseda da muryarta dake disashe, cikin haɗe fuska tace. "Wato dai bazaki bar koke-koken nan ba ko, so kike sai an gane wani abu ya faru da ke ko?." Kai ta jinjina cikin sanyi tace. "Mama ai wani abu kam yama faru, sanadi nane fa akayi mishi komai, ban saniba yana raye ko ya mutu wani hali yake? tun randa abin ya faru da dare washegari naje asibitoci sunfi bakwai babushi ba dalilinshi, ni badan raina da sukayi min barazana da shiba, a a shida yake hannunsu nakeji kar su ƙara cutarmin dashi." ta ƙarishe maganar wasu zafafan hawaye na kwaranyo mata, ita kuwa Mama kasake tayi tare da cewa. "eyeh sannu uwarshi harda su wani kada su ƙara cutar

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148