Skip to content

Chapter 79

Chapter 79

Nakasa Ba Kasawa Bace Book One Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
Download Book

da ganinsu zasuyi taushi, ji yadda suke shek'i." still bai kulata ba, ganin ta shagala wurin kallonshi, ido ya lumshe yana tuno Zaleeha a ranshi sai yake jin inama itace kusa dashi, a hankali taja numfashi kana tasa hannu bisa fuskarshi ta karkad'a mishi yatsunta, d'ago lumsasshun idanunshi yayi ya d'an kalleta. ganin ta nuna mishi allurane yasashi, rumtse ido kana ya d'an mirgina tare da gyara zaman damtsen hannunshi na dama ya bata damar mishi allurar, a hankali ta zira mishi allurar kana ta fara tura ruwan, ido ya kuma rumtsewa kana yana sunkuyar da yatsun hannunshi har suna bada sautin k'aras-k'aras. a hankali ta kalleshi cikin tausayawa tace. "Sannu." bai nuna mata ya ganeba dan ya lura bata san yana gane mgnar mutaneba in yana ganin bakinsu, maganin ta babballa kana ta mik'a mishi. Hannun dama yasa ya amsa kana ya afasu a baki tare da amsar robar ruwan da ta mik'o mishi, sannan ya had'iyesu, bayan ta gama mishi komaine ta k'ara mishi gudun AC ganin tunda ta mishi allurar yake d'an had'a zufa, gaban gadon ta dawo ta gyara mushi mayafin sannan ta kalleshi tare da cewa. "Zan tafi gida, dare yayi, dan kai gobe da sassafe zan dawo Allah ya baka lfy, da masu kula da kai zasu ku kwana tare." A ranshi yace. "Amin ngd." a zahiri kuma bai kuma kulataba, itako fita tayi, shi kuwa text yayiwa Rahma da Raliyya da Hayatuddeen kana yayi addu'a ya rufe ido dan allurar ta fara sashi gyangyad'i. Rahma kam dama da Adnan zai taho cewa yayi ta koma Side d'in Mamanshi dan yana soron kartayi ta kuka, kuma Alhamdulillahi dake uwar mijintan na sonta suna kuma tausaya mata suna kula da ita shiyasa ta d'an sake bare yanzu da taga text d'in k'anin nata yana ce mata. "Adda, yanzu Ya Adnan yazo, mukasha hira, yace min wai kince sai dai ku taho tare, ni kuwa gani garau na samu sauk'i itama Ummi da Hayatudden zasu dawo, an bar gida ba manya ga Ahmad ma yazo nan, duk sun tare a kaina sai kace basu da aikin yi." murmushi tayi tare da cewa. "Zan zo kam in su Ummi sun dawo, in banzo na gankaba to wa zai zo ya ganka?." murmushi yayi kana yace mata. "Budurwata mana zatazo." dariya tayi cikin samun nitsuwa tace. "Iye to me sunanta surkar tawa." kai ya rausayar tare da cewa. "Sai na dawo zan gaya miki." daga nanne ya rufe wayar tashi. Shiko Dr Adnan tare suka tafi da Dr Aliyu a can ya kwana. Ummi kuwa tunda suka koma ta kasa samun sukuni duk da ta fawwala Allah lamarinta, Amman ta kasa cin abinci, Hayatuddeen kuwa ya d'an sake sabida yadda Ya Rabi'u, da Ya ishaq da Ahmad suka rink'a yi mishi nasiha da bashi k'arfin guiwa da nuna mishi yarda da k'addara. Aunty Mami kuwa tausayin Ummi ya hanata sukuni sabida da ka ganta kasan tana cikin damuwa da fargaba, shiyasa data gama shirin baccinta ta kuma soya mata gwai da biredi kana ta had'a mata tea ta nufi d'akin da suka sauk'i Ummin inda suke sauk'e Mamansu Ishaq in tazo. bisa sallaya ta sameta tana rik'e da carbi, gefenta ta zauna tare da tank'oshe k'afafunta, ganin har yanzu Ummi hawaye take zubdawa cikin sanyi Aunty Mamin tace. "Kiyi hak'uri Ummi ki dena kuka dan Allah kiyi ta mishi Addu'a, insha Allah zai samu lfy." cikin sanyin murya tace, "Mami ya zanyi in banyi kukaba, me zanyi da hawayen nawa, ce minfa sukayi Saifuddeen na bazai sake tsayawa da k'afafunshi ba." cikin tausasawa tace. "A a fa Ummi ana kyautata zaton wata rana zai iya mik'ewa." kai ta jinjina kana tace, "Kayya ba dai boye min sukeyi ba, hakama sukayi min lokacin Nuruddeen da Abbansu." Sai kuma ta share hawayenta cikin tarin damuwa taci gaba da cewa. "Ina rasa nitsuwata da konciyar hankali na in naga Saifuddeen yana cikin wani hali, ina jin tausayinshi a raina ina rasa samun nitsuwata gaba d'aya a kanshi, ina tausayawa Saifuddeen in na tuna lfy lau na haifeshi, sai kuma abubuwa suketa biyu bayan rayuwarshi." cikin tausayawa Aunty Mami tace. "Ummi. Wayene Nuruddeen d'in da Abbansu?." a hankali Ummi ta nisa kana cikin sanyi ta fara bata lbrin asalinsu Saifuddeen dama yadda ya samu larurar rashin ji... Cikin tsananin kuka da tausayawa Aunty Mami tayi saki wani nannauyan ajiyan zuciya. Numfashi ta fudda a hankali sannan ta jingina da gadon tana mai sheshesk'an kuka har saida Ummi ta dawo tana bata hak'uri, cikin rauni ta share hawayenta tare da cewa. "In sha Allah daga yanzu duk sanda nayi salla zansa Saifuddeen cikin addu'o'i na ya bani tausayi tun yana yaro k'arami yayita fuskantar k'alubalen rayuwa." sai ta kuma gyara zamanta tare da cewa. "Dan Allah Ummi na rok'eki ki daina yawan kuka, kiyi ta mishi addu'a in sha Allah Saifuddeen bazai tab'eba." Sassanyan ajiyan zuciya Ummi ta sauk'e tare da cewa. "In sha zan daina yawan kukan zanyi ta mishi addu'a." cikin jin dad'i ta mik'a mata kofin tea d'in, ba musu ta karb'a tare da cewa. "Ngd Allah ya miki al'barka." Amin Amin tace sannan ta mik'e ta fita dan bata wuri. Washe gari kuwa tuni Doctor Aliyu ya harhad'a dukkan bayanan cutar Saifuddeen ya turawa Dr Acash prasat wanda yake aiki a wani babban asibiti dake New Delhi India, Ahmad kuwa E passport d'in Saifuddeen da Hayatuddeen da nashi ya tattara ya nufi Airport tun da sanyin safiya ya fara musu cuku-cukun samun visa, A nan ya samu Adnan ya taho dan tare zasu tafi dole yayi musu jagora a matsayinshi na likita da yaso ace da Dr Aliyu zasuje to shi aiyuka sun mishi yawa, sai da suka gama duk abinda ya dace na zirganiyar samun tafiyar nasu cikin sauri cikin sa'a kuwa suka samu jirgin da zai tashi jibi nan zuwa India direct New Delhi Indira Gandhi Enternational Airport, saida suka gama komai na tafiyar sannan suka baro airport d'in. Ummi kuwa da Ishaq da Saifuddeen Ya Rabi'u ne ya kaisu Asibitin. Suna isa Dr Batulu tayi musu jagora har d'akin da Saifuddeen d'in yake, sosai Ummi taji dad'in samunshi cikin nitsuwa yana rik'e da wayarshi fuskarshi d'auke da murmushi, da sauri ta isa bakin gadon kujerar dake kusa dashi taja ta zauna, ishaq kuwa yana isa bakin gadon ya rik'e k'arfen gadon ya tsaya, Hayatudddeen kuwa gefen shi ya tsaya kusa da Umminsu, da sauri ya ajiye wayarshin tare da juyawa inda suke jin Ummi na shafa kanshi, murmushin ya kumayi tare d'ago hannunshi ya shafa kan Hayatuddeen yayinda Ummi kuwa ke shafa kanshi, sai ya kuma mik'o hannunshi d'aya ya kamo hannun ishaq. Ya Rabi'u ne ya d'anyi murmushi tare da cewa. "Masha Allah. Alhamdulillahi jiki da sauk'i ko?." kai ya jinjina alamum eh. Dr Batulu kuwa sai binsu da idanu takeyi cikin shawar shak'uwar dake tsakaninsu. Cikin kula Ummi tace. "Sannu ko babana ya jikin?." wayarshi ya d'auka da sauri ya rubuta mata. "Alhamdulillahi jiki da sauk'i." cikin jin dad'i duk sukace. "Allah ya k'aro mana sauk'i." Amin Amin ya amsa a saman lab'b'ansa. Dai-dai lokacin kuma su Ahmad da Adnan suka shigo, bayan duk sun gaisa sun tabayi ya mai jikine sannan Ahmad ya

Table of Contents

Chapters

148 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148